Sashe 72
Kwai cikin Kaya Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read
Ni dai har muka bar wajen ban sake yarda na kallesa ba, hasalima gaba ɗaya na kasa samun sukuni, na sauke ajiyar zuciya ina dafe kaina, tare da fatan ALLAH ya kawo mani sauƙi akan wannan *Sabon al'amari* dana tsinci kaina a ciki.
Mun isa wani ɓoyayyen wajen sirri na hukumar mai ban tsoro, dan kuwa yau naga abinda a films kawai nake gani, wato manya-manyan makamai masu ban tashin hankali, yanzu dama a ƙasarmu akwai irin waɗannan manyan mahaukatan makaman irin haka?
Gaba ɗaya ganinsu ya saka karsashina guduwa, sai binsu muke da kallo tamkar wasu sokaye, mun daɗe munaji a labari babu jami'an da suka kai hukumar DSS mahaukatan bindigu. ban taɓa gasgata hakanba sai yau da idanuna suka ganemin zahiri......
Jin takun mutum a bayana ya sakani saurin juyawa, nai saurin matsawa gefe ƙirjina yana bugawar da bai taɓa yiba, dan sam bansan sanda ya shigo wajenba balle isowarsa kusa dani irin haka.
Baiko nuna yasan dani ba a wajen ya zuge glass ɗin da nake dab, hakan ya sakani yin gaba da sauri.
Jawaad dake hidimarsa cikin halin ko in kula ya ciro wata ƙaramar bindiga mai ƙyau ruwan Silver, sannan ya taka zuwa kujerar dake tare da tebir ya zauna yana ɗora bindigar da harsasai kusan guda takwas.
Jabeer da suke tare ya ɗauki bindigar da Jay ya ajiye ya ɗura harsasan robar dake tare da bindigar a cikinta suna magana da Jay wadda sam su bily basajinsu.
Bayan Jabeer ya kammala ya nufi su Bily dake tsaye suna jiransu.
Umarni ya bamu akan mutum ɗaya yazo, dama dukanmu mu bakwaine, na rasa yanda zanyi na iya samun cikakkiyar nutsuwa a wajennan, nikam a raina nama fara zargin wannan mutumin ko yanada aljanin da baya sonane shiyyasa yake kiɗimani? Kokuma shine aljanin kansa?.
Ta yaya dukkan mutane ina mu'amula dasu hankalina kwance, sai shine a duk lokacin da muka samu kusanci gabana zai keta faɗuwa? Wannan lamarin da mamaki wlhy...........
Ƙarar harbin da ɗaya a cikinmu tai bisa allon gwajine ya maidoni a hayyacina babu shiri, danma harsashin robane, amma a hakan ba ƙaramar firgita nayi ba.
Kallon da sukemin ya sakani yin murmushin yaƙe, shima na saci kallonsa, sai na tsinci idonsa a kaina, amma saiya janye kamar ba haka bane, ya maida ga allon da wancan yay harbin.
Sai kuma mukaga ya taso zuwa garemu, hakan ya sakani sake aro nutsuwa na azama kaina, ya karɓi bindigar hannun Oga Jabeer ɗin, a wani salon kai tsaye ya harba harsashin saɓanin mu da sai ka tsaya wajen nutsuwar ina zaka harba.
A tsakkiyar inda ake buƙata harsashin ya shiga anan kuwa ya shige jikin allon, ya juyo yana fuskantarmu sosai,
“Wannan shine wajen da nake buƙatar kaɗai harsashi ya shiga”.
Iya abinda yace kenan ya wurgama Oga Jabeer bindigar shiko ya caɓe.
Na ƙagara yabar wajen, amma sai naga yama gyara tsaiwarsa alamun babu inda zaije.
Ɗaya bayan ɗaya muke zuwa kowa yana gwada ƙwazonsa, amma ni na kasa tafiya, dan ji nake tamkar bazan iya komaiba a gabansa.
Wanda daga shi sai ni dana rage ta ƙarshe yayi shima, hakan na nufin dai duk wayon amarya sai ansha manta, dan ta laɓe-laɓe ta ƙare kuma.
Haka na taka nima na amsa, sai dai hannuna rawa yakeyi, gashi duk sun wani zubamin idanu.
Cikin karanto addu'a na fara dake raina da maida hankali akan abinda ke gabana.
Amma sai babu zato naji ƙamshin mayen turarensa mai daɗin shaƙa ya sake kusantoni..............✍🏻
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*😭🙏🏻https://youtu.be/T8bCANmJA5E
*_MANHA HAUSA NOVELS_*
https://youtu.be/xUINNiDdeH0
*_AL-ƘALAMI TV_*
*_Facebook_* _Bilyn Abdull_ 😉
https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=102039014953186&id=100054412625125
*_Typing📲_*
*_🧺ƘWAI_* _cikin_ *_ƘAYA!!🧺_*
*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*
*_Wattpad:-_* _BilynAbdull😉_
*__________________________________*
*_BOOK ONE_*
_Shafi na talatin da tara_
*__________________________________*
.............“Ki maida hankali akan abinda kikeyi”.
Muryarsa mai tarin nutsuwa da amo ta daki dodon kunnena, yayinda zuciyata tai wata irin bugawa tamkar zata faɗo ƙasa, idanuna suka cika da ƙwalla.
Ruɗanin dana shiga na babu zato babu tsammani ya sakani danna kunamar bindigar ba tare dana saniba.....
Ji nai kawai sautin tafi na tashi, nai azamar kallonsu kafin na maida ga allon harbin, sai naga na harba ainahin inda ake buƙata.
Bansan murmushi ya suɓuceminba, na saci kallonsa sai naga wayam yabar wajen ma gaba ɗaya, yana daga can gaban kantar da aka zagaye ɗakin da ita aka kuma rufeta da glasess baki ɗaya, wasu bindigu yake zubama harsasai tamkarma baisan mi akeba.....
Maganar oga Jabeer ta sakani maida kallona garesa, yace, “Lallai kin cancanci a kiraki gwanar harbi”.
Murmushi nayi da faɗin, “Nagode sir”.
Dai-dai Jawaad ya dawo wajen kalamar godiya da Bilkisu kema Jabeer ta shiga kunnensa, yay musu kallo ɗaya yana ɗauke ido da ƙara tamke fuska ya miƙama Jabeer bindugun hannunsa.
Amsa Jabeer yayi ya miƙama kowannenmu a hannunsa, sannan ya nuna mana inda kowa zai harba ba tare da ya mana bayanin dalilin hakanba.
Duk jeruwa mukai, kowanne ya zam cikin shiri kafin Oga Jabeer ɗin ya irga uku sannan ya bamu umarni.
Koda muka harba nidai idanuna na lumshe dan nasan dai bai zama lallai na zam cikin masu nasara tamkar ɗazunba,
“Inhar zakuyi harbi ku rufe idanunku da tunanin rashin nasara to lallai wataran a filin daga wani zai fasa kayinku da nasa harsashin”.
Maganarsa ta shiga kunnuwan kowannenmu babu zato, saurin buɗe idanuna nayi da mamakin jin furucinsa, musamman ma da naga ba'a kusa dani yakeba, hasalima ya nufi ƙofar fitane zai fice daga wajen.
Dukanmu da kallo muka bisa harya fice. kafin sauran ƴan uwana su shiga ma juna kallon-kallo, kowa nason fahimtar wanene ya rufe idon a cikinmu?, sai dai babu wanda ya samu amsarsa.
Jabeer yay murmusa yana girgiza kansa kawai, da maida kallonsa gasu Bilkisu.
Shima sallamarmu yayi, dan haka duk muka fito kowa yana ƴar maganarsa da wanda halinsa ya saɓa, mu biyune mata a ciki kawai, ita kuma tunma a wajen training bama shiga sabgar juna da ita.
Koda muka fito sai na shiga neman Ummie, na iske su basu fitoba, komawa nai bakin aiki, sai dai duk yanda naso ture abinda ya faru a raina yaƙi turuwa, sai kai kawo yakemin a zuciya da ƙwaƙwalwa.
A wannan yanayin Ummie tazo ta sameni, tun tana kallona harta kasa jurewa ta jehomin tambaya,
“Madam wai yaya dai?”.
Kallonta nai da mamaki,
Nace, “Kamarya?”.
Dariya ta ƙyalƙyale da ita tana girgiza kanta, “Kinga bar zaromin idanu tambaya kawai nayi”.
Ƙwafa nai mata ina ɗauke idanuna daga kanta da faɗin, “Gulmammiya”.
★★★★★
Mun isa wani ɓoyayyen wajen sirri na hukumar mai ban tsoro, dan kuwa yau naga abinda a films kawai nake gani, wato manya-manyan makamai masu ban tashin hankali, yanzu dama a ƙasarmu akwai irin waɗannan manyan mahaukatan makaman irin haka?
Gaba ɗaya ganinsu ya saka karsashina guduwa, sai binsu muke da kallo tamkar wasu sokaye, mun daɗe munaji a labari babu jami'an da suka kai hukumar DSS mahaukatan bindigu. ban taɓa gasgata hakanba sai yau da idanuna suka ganemin zahiri......
Jin takun mutum a bayana ya sakani saurin juyawa, nai saurin matsawa gefe ƙirjina yana bugawar da bai taɓa yiba, dan sam bansan sanda ya shigo wajenba balle isowarsa kusa dani irin haka.
Baiko nuna yasan dani ba a wajen ya zuge glass ɗin da nake dab, hakan ya sakani yin gaba da sauri.
Jawaad dake hidimarsa cikin halin ko in kula ya ciro wata ƙaramar bindiga mai ƙyau ruwan Silver, sannan ya taka zuwa kujerar dake tare da tebir ya zauna yana ɗora bindigar da harsasai kusan guda takwas.
Jabeer da suke tare ya ɗauki bindigar da Jay ya ajiye ya ɗura harsasan robar dake tare da bindigar a cikinta suna magana da Jay wadda sam su bily basajinsu.
Bayan Jabeer ya kammala ya nufi su Bily dake tsaye suna jiransu.
Umarni ya bamu akan mutum ɗaya yazo, dama dukanmu mu bakwaine, na rasa yanda zanyi na iya samun cikakkiyar nutsuwa a wajennan, nikam a raina nama fara zargin wannan mutumin ko yanada aljanin da baya sonane shiyyasa yake kiɗimani? Kokuma shine aljanin kansa?.
Ta yaya dukkan mutane ina mu'amula dasu hankalina kwance, sai shine a duk lokacin da muka samu kusanci gabana zai keta faɗuwa? Wannan lamarin da mamaki wlhy...........
Ƙarar harbin da ɗaya a cikinmu tai bisa allon gwajine ya maidoni a hayyacina babu shiri, danma harsashin robane, amma a hakan ba ƙaramar firgita nayi ba.
Kallon da sukemin ya sakani yin murmushin yaƙe, shima na saci kallonsa, sai na tsinci idonsa a kaina, amma saiya janye kamar ba haka bane, ya maida ga allon da wancan yay harbin.
Sai kuma mukaga ya taso zuwa garemu, hakan ya sakani sake aro nutsuwa na azama kaina, ya karɓi bindigar hannun Oga Jabeer ɗin, a wani salon kai tsaye ya harba harsashin saɓanin mu da sai ka tsaya wajen nutsuwar ina zaka harba.
A tsakkiyar inda ake buƙata harsashin ya shiga anan kuwa ya shige jikin allon, ya juyo yana fuskantarmu sosai,
“Wannan shine wajen da nake buƙatar kaɗai harsashi ya shiga”.
Iya abinda yace kenan ya wurgama Oga Jabeer bindigar shiko ya caɓe.
Na ƙagara yabar wajen, amma sai naga yama gyara tsaiwarsa alamun babu inda zaije.
Ɗaya bayan ɗaya muke zuwa kowa yana gwada ƙwazonsa, amma ni na kasa tafiya, dan ji nake tamkar bazan iya komaiba a gabansa.
Wanda daga shi sai ni dana rage ta ƙarshe yayi shima, hakan na nufin dai duk wayon amarya sai ansha manta, dan ta laɓe-laɓe ta ƙare kuma.
Haka na taka nima na amsa, sai dai hannuna rawa yakeyi, gashi duk sun wani zubamin idanu.
Cikin karanto addu'a na fara dake raina da maida hankali akan abinda ke gabana.
Amma sai babu zato naji ƙamshin mayen turarensa mai daɗin shaƙa ya sake kusantoni..............✍🏻
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*😭🙏🏻https://youtu.be/T8bCANmJA5E
*_MANHA HAUSA NOVELS_*
https://youtu.be/xUINNiDdeH0
*_AL-ƘALAMI TV_*
*_Facebook_* _Bilyn Abdull_ 😉
https://m.facebook.com/story.php?story_fbid=102039014953186&id=100054412625125
*_Typing📲_*
*_🧺ƘWAI_* _cikin_ *_ƘAYA!!🧺_*
*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*
*_Wattpad:-_* _BilynAbdull😉_
*__________________________________*
*_BOOK ONE_*
_Shafi na talatin da tara_
*__________________________________*
.............“Ki maida hankali akan abinda kikeyi”.
Muryarsa mai tarin nutsuwa da amo ta daki dodon kunnena, yayinda zuciyata tai wata irin bugawa tamkar zata faɗo ƙasa, idanuna suka cika da ƙwalla.
Ruɗanin dana shiga na babu zato babu tsammani ya sakani danna kunamar bindigar ba tare dana saniba.....
Ji nai kawai sautin tafi na tashi, nai azamar kallonsu kafin na maida ga allon harbin, sai naga na harba ainahin inda ake buƙata.
Bansan murmushi ya suɓuceminba, na saci kallonsa sai naga wayam yabar wajen ma gaba ɗaya, yana daga can gaban kantar da aka zagaye ɗakin da ita aka kuma rufeta da glasess baki ɗaya, wasu bindigu yake zubama harsasai tamkarma baisan mi akeba.....
Maganar oga Jabeer ta sakani maida kallona garesa, yace, “Lallai kin cancanci a kiraki gwanar harbi”.
Murmushi nayi da faɗin, “Nagode sir”.
Dai-dai Jawaad ya dawo wajen kalamar godiya da Bilkisu kema Jabeer ta shiga kunnensa, yay musu kallo ɗaya yana ɗauke ido da ƙara tamke fuska ya miƙama Jabeer bindugun hannunsa.
Amsa Jabeer yayi ya miƙama kowannenmu a hannunsa, sannan ya nuna mana inda kowa zai harba ba tare da ya mana bayanin dalilin hakanba.
Duk jeruwa mukai, kowanne ya zam cikin shiri kafin Oga Jabeer ɗin ya irga uku sannan ya bamu umarni.
Koda muka harba nidai idanuna na lumshe dan nasan dai bai zama lallai na zam cikin masu nasara tamkar ɗazunba,
“Inhar zakuyi harbi ku rufe idanunku da tunanin rashin nasara to lallai wataran a filin daga wani zai fasa kayinku da nasa harsashin”.
Maganarsa ta shiga kunnuwan kowannenmu babu zato, saurin buɗe idanuna nayi da mamakin jin furucinsa, musamman ma da naga ba'a kusa dani yakeba, hasalima ya nufi ƙofar fitane zai fice daga wajen.
Dukanmu da kallo muka bisa harya fice. kafin sauran ƴan uwana su shiga ma juna kallon-kallo, kowa nason fahimtar wanene ya rufe idon a cikinmu?, sai dai babu wanda ya samu amsarsa.
Jabeer yay murmusa yana girgiza kansa kawai, da maida kallonsa gasu Bilkisu.
Shima sallamarmu yayi, dan haka duk muka fito kowa yana ƴar maganarsa da wanda halinsa ya saɓa, mu biyune mata a ciki kawai, ita kuma tunma a wajen training bama shiga sabgar juna da ita.
Koda muka fito sai na shiga neman Ummie, na iske su basu fitoba, komawa nai bakin aiki, sai dai duk yanda naso ture abinda ya faru a raina yaƙi turuwa, sai kai kawo yakemin a zuciya da ƙwaƙwalwa.
A wannan yanayin Ummie tazo ta sameni, tun tana kallona harta kasa jurewa ta jehomin tambaya,
“Madam wai yaya dai?”.
Kallonta nai da mamaki,
Nace, “Kamarya?”.
Dariya ta ƙyalƙyale da ita tana girgiza kanta, “Kinga bar zaromin idanu tambaya kawai nayi”.
Ƙwafa nai mata ina ɗauke idanuna daga kanta da faɗin, “Gulmammiya”.
★★★★★