← Book details Kwai cikin Kaya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 50 OF 75

Sashe 50

Kwai cikin Kaya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Bayan Jay ya koma Office ne Gimba ya je ya kai masa abinda Dr Tayyeb ya kawo.
Jawaad ya amsa yana buɗe ledar da aka zubo su a ciki, ɗaya bayan ɗaya ya fiddosu ya duba, yay guntun murmishi saboda kowanne da alamar da Dr Tayyeb yayma kwalin yanda za'a gane na kowa, maidasu yay duka a ledan ya sake miƙama gimba.
“Ka kaima Aliyu su, yanzu nake buƙatar results ɗinsu”.
“Okey boss” gimba ya faɗa cikin girmamawa yana amsar ledar..

Ba a wani ɗauki lokaci mai tsawo ba Aliyu ya shigo Office ɗin, lokacin Jawaad na tare da Rose suna magana akan wani aiki daya sakata.
Zama Aliyu yayi a kujerar dake kallon ta Rose ɗin ya miƙama Jay takardu na results ɗin, ya kuma ajiye kwalaben dake a ledar.
“Boss Result biyu fa yayi kama da na farko, dan a jikin syringe ɗin jiya yatsun hannun mutum biyu muka samu, amma ɗaya yafi fitane da ƙyau, duk da dai haka mun samu yanda mukeso. Ka duba da Result ɗin jiya da waɗannan na saman na mutane biyune dake jikin syringe ɗin kamar yanda na faɗa maka tun farko”.
Kai Jay ya shiga jinjinawa yana ɗan lila kansa a kujera, tuni idanunsa sun canja launi sai wani munafukin murmushi dake shimfiɗe bisa fuskarsa wanda Aliyu da Rose duk suka kasa fahimta.
Cikin sauke numfashi ya ajiye takardun yana maida kallonsa ga Aliyu.
“Aliyu kiramin Jabeer”.
“Okey Boss” Aliyu ya amsa yana ƙoƙarin kiran Jabeer a waya, koda Jabeer ya ɗaga daga can sai Aliyu ya sanar masa saƙon Jawaad.
Babu jimawa kam saiga Jabeer ɗin.
Jawaad dake rubutu a takarda ya ɗago ido ya kalli Jabeer, kafin ya miƙa masa takardar daya gama rubutun.
“Jabeer wannan Number ɗin nakeson nasan daga shekaran jiya zuwa yau da mutum nawa akai waya, sannan mutane nawa suka kira layin?”.
Amsa Jabeer yayi yana kaɗa kai, ya nufi wasu Computers guda uku dake can gefe a cikin Office ɗin Jawaad.
Hakan ne ya saka Aliyu miƙewa yabi Jabeer dan ya taimaka masa.
Rose ma mikewar tai ta koma wajen su Jabeer ɗin, shiko Jawaad ya cigaba da aikin da yake a Computer gabansa zuciyarsa na masa wani zogi da ƙuna, domin kuwa result ɗin sayin hannun Jack da Shahudah aka samu a jikin syringe ɗin, na Jack shine ya danne na Shahudah alamar shine ƙarshen riƙe sirinjin.
Kusan mintuna goma sha biyar Jabeer ya juyo yana kallon Jawaad daya maida hankalinsa ga aikinsa tamkar babu abinda ke damunsa.
“Boss ga waɗanda sukai kiran da waɗanda aka kira, sai text messages guda uku da akayi, kuma duk a jiyane kamar ma kai akaimawa”.
Miƙewa Jawaad yay zuwa inda su Jabeer suke, Aliyu yay saurin tashi ya bashi kujerar da yake zauna, jawota baya kaɗan Jay yay ya zauna, da kansa duk yabi ya duba, tabbas saƙo biyu shi Shahudah ta turomawa, sai dai babuma wanda ya duba a ciki dukda yaga shigowarsu tun ɗazun da safe, komawa yay duba Numbers uku da Shahudah ta kira randa abun ya faru, ya ƙurama Number ƙarshe ido yana nazarinta.
Kallon Rose dake tsaye yay yay mata nuni data ɗakko masa wayarsa dake tebir ba tare da yay magana ba.
Cikin hanzari taje ta ɗakko ta kawo masa.
Number Aamilah da tunda yake bai taɓa kiraba sai dai ita ta kirashi ya lalubo.
Akan laɓɓansa ya furata, “Aamilah” a hankali, Murmushi ya saki yana cizar leɓensa na ƙasa, “Jabeer bincikamin itama wannan Number ” yay maganar yana nuna masa Number Aamilah.
itama duƙufa Jabeer yay a kanta, ana cikin hakane Hafiz ya shigo hannunsa ɗauke da takardu, ganin sun haɗa kai waje guda ya nufisu yana faɗin, “Wane shagalin ake anan kuma?”.
Duk kallonsa sukayi, banda Jawaad da Jabeer da hankulansu ke bisa Computer ɗin.
Jabeer yace, “Wannan sune ta kira a jiya, waɗan nan suka kirata, ga kuma na yau”.
Shiru Jawaad yay yana kallon Numbers ɗin, ya sauke numfashi yana girgiza kai, “Ina na shekaran jiya?”.
“Gasu nan” cewar Jabeer yanama Jawaad nuni dasu bayan ya kuma zooming ɗinsu yanda Jay zai gani sosai.
Ahankali ya ringa nazarinsu ɗaya bayan ɗaya, “Jabeer inason nasan kowacce number daga ina akai kira da ita, wanda ta kura kuma a ina yake”.
“Amma zamu ɗauki lokaci Boss, magriba kuma ta gabato........”
Kafin Jawaad yay magana Rose tace, “Bara muyi tanan kawai zaifi mana sauri”.
Duk juyawa sukai suna kallonta har Jay ɗin da yake lafe jikin kujera yana shafa ƙasumbar data ɗan taru mai a fuska kaɗan.
Sun santa mayyace itama a irin waɗannan binciken, shiyyasa suke son zamanta a tafiyarsu sosai.
Tana danne-danne tana kai kawo, hakan yasa suketa binta da kallo, shima Jabeer bai fasaba dubawar yake daga ɓangarensa.
Cikin min tunan da basu gaza biyarba, Rose tace, “Number mai ƙarshe 3434 mai ita tana a anguwar Sunusi Abdullahi stress, layi na biyu gida mai lamab 107, an kiratane da ƙarfe 10:34am, zamu iya kiran kamfanin layin idan kana bukatar jin abinda aka tattauna akanta Boss”.
Cikin kafeta da idanu yace, “Kin tabbatar?”.
“Yes Sir, gashima ka duba da kanka” tai maganar tana miƙa masa.
Amsa yay shima yana dubawa, duk abinda ta faɗa dai-dai ya gansa, wani luuuu yay da idanunsa yana busar da huci mai azabar zafi. Kafin ya samu cewa wani abu Jabeer ya katseshi da faɗin,
“Boss ita kuma wannan daga Asibitin *NASARARMU* yanzu haka ma mai Number yana cikin asibitin, sannan Number da Rose take magana itama ta kirashi mintuna biyar kafin ita wannan ta kirasan, shima kuma ya kira waccan ɗin bayan awa ɗaya da kiran wannan.
Da ƙarfi Jawaad ya bugi tebirɗin da Computers ɗin suke kai, sai faman fidda numfashi yake da sauri-sauri.
Cikin kakkausar murya yace, “Muna idar da salla ku tababbar likitannan ya gurfanu a gabana, sannan mai wannan number itama kuje har gidan ku kamomin ita!!!”.
Ya ƙare maganar a matuƙar tsawace.
Su duka a tsorace syke kallonsa, gashi dama basu san komai game da aikinba, amma sun kula ya ɗaukesa da zafi tun jiya.
A cikin girmamawa duk suka amsa masa.
Uffan bai sake faɗaba, sai da ya ɗauki rigar suit ɗinsa yana nufar ƙofa yace, “Duk ku kaimin su Zangina road ina jiranku a can”.
Bai jira amsarsuba yay ficewarsa...............🤫✍🏻

Naji dukkan ƙorafinku akan son posting kullum, sai dai nace kuyi haƙuri kam, dan lokacine banda shi isashe, buks biyu nakeyi a lokaci guda, bazai yuwu kullum nace zan fidda pages biyu ba, na farko typing yana lashe lokutane, ga hidimar gida, sannan idanuna, ko bakwaso na tsufa da idanune😂?, sai kuma ita kanta ƙwalwa ai tana buƙatar hutu, ta hakanne za'a samu rubuta abu mai amfani da nutsuwa, sannu-sannu bata hana zuwa, da zaran mun kammala ZAFAFA komai zai dai-daita da izinin UBANGIJI, ngd da Comments ɗinku dan suna sani nishaɗi matuƙa, hakama addu'oinku ga mahaifina sukan ƙaramin jin kaimin muku typing koban niyyaba😭🙏🏻, I luv u wujiga-wujiga my kankanati fans😻😻🤫😂.

*_ZAFAFA SABON KAFCE SUN DAWO GAREKU_*

_KADA KU MANTA MARUBUTAN DAI SUNE WANDA SU KA RUBUTO MUKU ZAFAFAN LITTATTAFAN NA BAYA, A YANZU MA SUN SAKE YUNKUROWA DA WASU SABBIN MASU SABON SALO_

_*KAUNARMU:* 💋❤️NA MAMUH GEE_

_*DAURIN GORO:* 💋❤️NA HAFSAT RANO_

_*ALKAWARIN ALLAH::* 💋❤️SAFIYYA HUGUMA_

_*GUDU DA WAIWAYE:* 💋❤️NA BILLYN ABDUL_

_*IGIYAR ZATO:* ❤️💋NA MISS XOXO_

_CANCADI DOMIN DUKKANIN LITTAFAN NAN ZAKA/KI IYA MALLAKAR SU A NAIRA DARI BIYAR_

_GUDA DAYA DARI BIYU_

_GUDA BIYU DARI UKU_

_GUDA UKU DARI HUDU_

_GUDA HUDU DARI HUDU DA HAMSIN_

_DOMIN MALLAKAR SU SAI A TUNTUBE MU TA HANYAR_

*_ZAKU BIYA KUDI TA BANKI TA WANNAN ACCOUNT DIN👇👇_*

2260792279
_MARYAM SANI_
_ZENITHBANK_

saiku tura shaidar biyanku ta maana screenshot ta wannan layin👇👇
*07067124863*

*_GA MASU TURA KATIN MTN SAISU TURA KATINSU ZUWA GA WANNAN NUMBER TAREDA TURA MATA SHAIDA_*👇👇

*09032345899*

_Sayen nagari, maida kuɗi gida masoyan asali😉😻🥰🥰😍😍😘😘👌🏻💃🏻💃🏻_

Mucigaba da shakatawa da wannan dan yanzune aka fara kafta WASAN😁👉🏻📻

_Sannan akwai tashoshinmu na Youtobe da zasu fara kawo muku daɗaɗan labarai bisa tsaftataccen karatu, kuyu azamar garzayawa tashar *ALƘALAMI TV & MANHA HAUSA NOVELS* domin samun wannan gara ɓasa, a danna mana subscribing domin nuna ƙauna ta musamman masoyan gaskiya.😃🥰🥰💃🏻👌🏻_.

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*😭🙏🏻https://youtu.be/Zyl7_eSgXuo

Please and Please amana subscribing domin nuna ƙauna🤩🤝🏻

*_Typing📲_*

*_🧺ƘWAI_* _cikin_ *_ƘAYA!!🧺_*

*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

*_Wattpad:-_* _BilynAbdull😉_

*_____________________________________*
*_BOOK ONE_*
_Shafi na ashirin da bakwai_
*_____________________________________*

............Koda motar Jawaad da ta Security's nashi suka iso ƙofar gidan nasu Shahudah basu shigaba, cayay suyi fakin a ƙofar gida.
Zamansa yay a mota bai fitaba, hakan yasa securitys nashi fitowa su zagaye motar da yake a ciki.
Yanata danne-dannensa a waya kai kace bashi bane ya fito Office ɗazun a fusace, sai dai shi yanajin zafinne a cikin zuciyarsa, yayinda fuskarsa ta shanye komai tamkar babu komai.
Har aka kira sallar isha'i suna wajen, da kansa ya buɗe ya fito daga motar dan son gabatar da salla.
Masallacin anguwar dake jikin gidan maƙwaftan su Shahudah suka shiga, tare dasu akai jam'i, suka bar waɗanda basayi a wajen.

Bayan fitowarsu daga salla ne sai ga su Hafiz sun iso tare da Zaitun da Dr Jeo, sake shiga mamaki Zaitun tayi ganin ɗan uwanta Jawaad da take mutuwar ƙauna.
Shiko kallo ɗaya yay musu ya ɗauke kansa tamkar bai santaba ma.
Shi da rose da Hafiz, kawai suka shiga gidan, aka bar Aliyu da Jabeer a waje tare da securitys da su Zaitun da aka zubo a mota.

Amina data fito tana shirin wucewa gida tai azamar matsawa ta basu hanya jikinta na rawa, ko kallonta basu yiba kuwa, sai knocking ƙofar falon da Rose ta shigayi.
Amina da ta samu waje ta laƙe inda zata kalli komai, tace, “Ai dama tunda naji dambarwar da akeyi ɗazun a gidan nasan yau akwai kura”, dan haka tai azamar komawa ta ƙofar kicin ta baya, dan tayi alƙawarin sai taga komai kodan ta bama Bilkisu labari idan ta dawo.
Chapter 50 · 0% Book details