Sashe 49
Kwai cikin Kaya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*_____________________________________*
*_BOOK ONE_*
_Shafi na ashirin da shida_
*_____________________________________*
*_Yauma babu editing🤫⛹♀😣_*
............Shahudah taɗan samu sauƙi, sai dai fargabar Jawaad ta hanata sukuni sam, gashi a yau ko ƙeyarsa basu ganiba a gidan, tanason kiransa a waya tanajin tsoro.
Kusan ƙarfe uku na rana sai ga Doctor Tayyeb yazo gidan, lokacin duk suna falo, Qaseem ne kawai babu a gidan dan yana Office wajen aiki.
Shahudah na kwance ne a kujera doguwa kanta a kan cinyar Mummy, karenta na kwance daga ƙasa kusa da ita, sai Aamilah da Jack da Salma waɗanda shigowarsu gidan kenan.
Sai da Dr Tayyeb ya bama su Salman hannu suka gaisa sannan ya zauna yana gaida Mummy idonsa akan Shahudah da keta ɓata rai, dan tasan allura yazo yay mata ita kuma batason ta.
“My patient yaya jiki?” ‘Ya faɗa yana mata murmushin yaƙe’.
“Fine” kawai tace masa ta ɗauke kanta.
Bai damu ba yace, “Alhmdllh, yanzu dai babu ciwon marar ko?”.
Kanta kawai ta ɗaga masa.
Shima bai sake cewa komaiba ya shiga haɗa allurar da zai mata, ƙasan zuciyarsa yana tunanin ta yanda zai ɓilloma aikin Jawaad.
Da ƙyar Shahudah ta tsaya akai mata wannan allura, saboda tsabar taɓara harda kukanta.
Sai da ta koma dai-dai ne ya gyara zama yana mata bayanin yanda zata kula da kanta, ya fiddo wasu ƴan kwalaben magani, ɗaya ya miƙama Salman dake kusa dashi yana faɗin, “Salman ko kasan wannan maganin?”.
Karɓa Salman yayi yana dubawa, Dr Tayyeb ya sake ɗibar biyu ya mikama Aamilah da Jack suma, “Kuma ku duba kuga ko kun sanshi”.
Suma basu musaba suka amsa, itama Mummy da Shahudah duk ya miƙa musu, da farko dai Shahudah kam taƙi amsa, a cewarta karya isheta.
Mi kuma ta tuna oho mata, sai ta miƙo hannu ta amsa.
Salman da Aamilah suka fara maido masa da kwalaben suna faɗin sudai bama su gane kan maganinba, kwalayen kwalaben ya miƙa musu duk suka saka da kansu sannan ya amsa ya maida ajikka.
Jack ya kalli Dr Tayyeb cikin nuna shiɗin ƙwararrene yace, “Wannan ai maganin hana ɗaukar cikine, macen da bata haihuwama akan bata ta gwada shi kamar na wasu wattani kafin ta dakata”.
Murmushi Dr Tayyeb yayi yana jin jina kai alamar gamsuwa da bayanin jack, ya miƙa masa kwalin shima ya saka yana faɗin, “A lallai kasan magani kam sosai”.
Jack yaji daɗin yabon da ake masa ya miƙama Doctor bayan ya saka a kwalin yana sake bajewa a kujera, suma su Shahudah duk basu yay suka saka ita da Mummy ya amshe abunsa ya maida duka a jaka, ba tare daya yi musu wani ƙarin bayani ba yay musu sallama ya tafi.
Kaf ɗinsu babu wanda ya kawo wani abu a ransa game da maganin da Doctor Tayyeb ya nuna musu, garama Mummy taji haushinsa sosai, dan ita gani take kawai Doctor ɗin nasu yayi hakanne danya nunama Shahudah hanyar ɗaukar mataki a gaba, itako yanda suka tsara yanzu nanda kwanaki kaɗan Shahudah zata koma ɗakinta ko ALLAH zaisa a dace wani cikin ya shiga.
Dan jiya dai ta daure taje gida tama Mama Atika da ƴan uwanta bayani akan matsalar Shahudah ɗin.
Dukansu sun nuna rashin jin daɗinsu da tausayin Shahudah, sai dai kuma hankalinsu ya tashi, dan a ganinsu inhar Shahudah nada wannan matsalar to kenan yaushene ciki zai fara zaman da zasu sami cikar burinsu?.
Uncle Uwaisu daya kasa haƙuri sai cewa yay, “Anya kuwa kuna ganin bazamu ɗauki matakiba? Indai hakanefa zaman Shahudah da Jawaad bazai mana wani amfaniba kenan? Ko dai mu sake dubawa cikin yaran nan saimu aura masa wata?”.
Tsitt falon yayi kowa ya kasa magana, sai dai fuskar Mummy ta nuna alamun ɓacin rai.
Mama Atika ce ta katse shirun nasu dayin gyaran murya, cikin muryarta ta tsufa tace, “Maganar Uwaisu nakan hanya, hakama shawararsa mai ƙyau ce, sai dai akwai ruɗani a cikin hakan musamman akan ku kanku da zumincin ku”.
“Gaskiyane maganarki mama, gashi kuma bamu da damar sako wani cikin ƴan uwanmu, duk da na daɗe daji a raina kowa nada nasa burin wlhy, suna ɓoyewane kawai dan ace sunason yaron sosai, musamman ma Yaya Nasiru da kuke ganinsa nan ko? Humm”.
Nanma duk shiru suka sake yi, sai Mummy ce a hasale tace, “Amma gaskiya idan akai haka ba aima Shahudah adalciba, ai kamata yay mu nema magani ko mafitar da cikin zaike zama ɗin bawai muyi tunanin mata kishiya ba, sannan ku kunama zaton shi yaron kansa zai yarda da wannan kwamacalar? Shahudah ma da yake so da yaya muka ƙulla auren nasu balle kuma yanzu? Mudai sake tunani amma ba wannan ba”.
Kowa ya gamsu da bayaninta, duk da dai ta nuna akwai nuna taya kishin ɗiyarta a ciki.
daga ƙarshe dai sun yanke shawarar nemawa Shahudah magani, sannan su maidota ɗakinta da wuri ko ALLAH zaisa a dace ciki ya shiga da wuri🤫🥴.
★★★★★
Dr Tayyeb da ya samu abinda yazo nema yana fita ya sauke ajiyar zuciya, mota ya shiga bai zauna wasaba ya koma Office ɗin Jawaad.
Lokacin Jay yana tare da su Jabeer akan tsara aikinsu da zasu dasama ɗanba.
Bayan saƙon zuwan Dr Tayyeb yazo masa ta hanyar Gimba, bai fitoba, sai gimban ya bama damar amsar saƙon a wajen Doctor.
Gimba na tsaye Dr Tayyeb na bashi kwalayen kwalaben da duk yasamo fingers print ɗinsu Shahudah sai ga Qaseem ya fito daga Office, da alama ma dai ya tashi aiki, aiko sai idonsa karaf akan su Gimba.
Ɗunbin mamaki ne ya kamashi ganin Family Doctor ɗinsu anan, yay saurin ciro wayarsa daga aljihu ya ɗauki Dr Tayyeb da Gimba hoto.
_____________________
Lokacin da Qaseem ya shigo gidan duk su Shahudah sun tashi, Aamilah ce kawai a falon itama tana cin abincine a dani.
Yanda Qaseem ɗin ya shigone ya saka Aamilah kallonsa ita da Amina dake gyaran falon.
Cikin tsawa-tsawa yace ma Amina, “K tattaro min kowa na gidannan”.
Da “To” Amina ta amsa cikin girmamawa.
Tasowa Aamilah tai daga falon tana tambayarsa ko lafiya?.
Bai bata amsaba sai ƙokarin danna wayarsa yake domin son nemo hoton su Dr Tayyeb daya ɗauka.
A haka duk suka fito suka samesu har Shahudah dake fama da kanta.
Kowa yazo sai ya masa tambayar lafiya?.
Ganin duk sun hallara ya bisu da kallo yana faɗin, “Jawaad yazo gidannan yau?”.
A tare suka girgiza masa kai, kowanne da mamakin tambayar akan fuskarsa.
Qaseem ya kuma cewa, “Doctor Tayyeb fa?”.
Salman yace, “Yazo har yayma Shahudah allura”.
Dariya sosai Qaseem ya sanya yana tafa hannaye, wadda tasakasu duk zuba masa idanu, Mummy ta katsesa, “Qaseem lafiyarka kuwa? Minene abin dariya to anan?”.
“Mummy bazaki ganeba, ni dama nasan Jawaad bazai taɓa bariba, da Tayyeb yazo gidannan bayan allura mi yayi?”.
Aamilah taja gajeran tsaki, “Iya allurar yayi mana, sai wani shirmensa na nuna mana wai ko maganin hana ɗaukar ciki, ni jakinma harya wuce ban fahimci manufarsa ba....”
Saurin katse Qaseem yayi, “K shashasha, aiku ya maida jakkan, to lallai akwai manufa, dan inada tabbacin aiki Jawaad ya sakashi, dan naga Dr Tayyeb a Office ɗinmu yanzunan yana bama gimba drivern Jawaad wasu kwalaye”.
Dukansu idanu suka zaro waje har Jack, dan da turanci duk suke magana saboda Jack ɗin ya fahimta.
Mummy tace, “Ni ban ganeba, kai mika fahimta to?”.
Cikin taɓe baki da ɗage kafaɗu Qaseem yace, “Cikinsa yake bin ba'asi mana, ki binciki ƴarki Mummy dan akwai abinda take ɓoye miki, kuma duk wanda yasan da hannunsa a ciki wlhy ya kuka da kansa dan Jawaad ya fiku iya birkicewa, aikin banza kawai kun jama mutane asara, ku duba nan ku gani” ya ƙare maganar yana mika musu wayarsa a hasale.
Dukansu jikinsu tsuma yake, musamman Aamilah da jack da Shahudah, ita kanta Mummy zuface ke karyo mata a kowacce ƙofar gashin jikinta, tsabar ɗumi da ƙwalwar kanta ta ɗauka tama rasa abin faɗa.
Dukansu babu wanda baiga abinda Tayyeb ke mikama Gimba ba, kwalaben daya basune fa.
Mummy da jikinta ke mazari ta juya tana kallon Shahudah dake a birkice, kasa ce mata komai tayi.
Ba Mummy da Shahudah ba kowama a birkicen yake, hatta da Salman da baisan komaiba yay wuƙi-wuƙi da idanu.
Daga nan kowa kai kawo ya shigayi a falon.
Shahudah, Aamilah, Jack, kowa yana tunanine akan a ina matsalar take?.
Yaya akai Dr Tayyeb ya je ga Jawaad? Aamilah da tasan yanda sukai da Dr Tayyeb zuciyarta sai tsitstsinkewa take, zargi biyune a ranta, kodai Doctor ya samu Jawaad da gaskiyar batu, kokuma Zaitun ce ta faɗama Jawaad, to amma ai Zaitun batasan wanene zai amfani da allurarba, ita kawai sun nema sanin likitane ta hanyarta, tayaya zata samu Jay da maganar abinda bata sani ba.
“Kenan a ina matsalar ta fito?”.
Aamilah ta faɗa a fili ba tare da ta sani ba.
Duk kallonta sukayi kuwa, Mummy tace, “Aamilah mi kike faɗane?”.
Cikin in ina Aamilah tace, “M... Mummy bance komaiba”.
Qaseem yace, “Humm yarinya zaki magantu ne, ni dama tun randa abun nan ya faru wlhy na fahimci baki da gaskiya”.
Tsaki Aamilah ta ja mai mugun ƙarfi tana harar Qaseem, tace, “To masheranci, ni kaɗai duk faɗin gidannan ka sakama idanu?, sokake ka ƙalamin sheri? Ai bani cikin ke a jikinaba balle kace....”
A harziƙe Qaseem yay kan Aamilah, ta zuba da gudu ta shige ɗaki ta kulle kanta.
Cikin matuƙar fushi Qaseem yace, “Mummy kina gani ko? Ni wannan ƴar iskar yarinyar take faɗama duk abinda yazo bakinta? Ƙanwata ta huɗu?”.
Cikin damuwa Mummy tace, “Qaseem dan ALLAH ku barni naji da abinda ya dameni, Shahudah inhar zubar da cikin nan kikai wlhy kin cutar damu kuwa”.
Sake ɓaci ran Qaseem yayi ganin Mummy ta nuna halin ko in kula da abinda Aamilah tai masa, Shahudah kam bata iya bama Mummy amsaba saboda jirin dake ɗibarta, ganinta kawai sukai zube a ƙasa wanwars.
______★______★_______★______
*_BOOK ONE_*
_Shafi na ashirin da shida_
*_____________________________________*
*_Yauma babu editing🤫⛹♀😣_*
............Shahudah taɗan samu sauƙi, sai dai fargabar Jawaad ta hanata sukuni sam, gashi a yau ko ƙeyarsa basu ganiba a gidan, tanason kiransa a waya tanajin tsoro.
Kusan ƙarfe uku na rana sai ga Doctor Tayyeb yazo gidan, lokacin duk suna falo, Qaseem ne kawai babu a gidan dan yana Office wajen aiki.
Shahudah na kwance ne a kujera doguwa kanta a kan cinyar Mummy, karenta na kwance daga ƙasa kusa da ita, sai Aamilah da Jack da Salma waɗanda shigowarsu gidan kenan.
Sai da Dr Tayyeb ya bama su Salman hannu suka gaisa sannan ya zauna yana gaida Mummy idonsa akan Shahudah da keta ɓata rai, dan tasan allura yazo yay mata ita kuma batason ta.
“My patient yaya jiki?” ‘Ya faɗa yana mata murmushin yaƙe’.
“Fine” kawai tace masa ta ɗauke kanta.
Bai damu ba yace, “Alhmdllh, yanzu dai babu ciwon marar ko?”.
Kanta kawai ta ɗaga masa.
Shima bai sake cewa komaiba ya shiga haɗa allurar da zai mata, ƙasan zuciyarsa yana tunanin ta yanda zai ɓilloma aikin Jawaad.
Da ƙyar Shahudah ta tsaya akai mata wannan allura, saboda tsabar taɓara harda kukanta.
Sai da ta koma dai-dai ne ya gyara zama yana mata bayanin yanda zata kula da kanta, ya fiddo wasu ƴan kwalaben magani, ɗaya ya miƙama Salman dake kusa dashi yana faɗin, “Salman ko kasan wannan maganin?”.
Karɓa Salman yayi yana dubawa, Dr Tayyeb ya sake ɗibar biyu ya mikama Aamilah da Jack suma, “Kuma ku duba kuga ko kun sanshi”.
Suma basu musaba suka amsa, itama Mummy da Shahudah duk ya miƙa musu, da farko dai Shahudah kam taƙi amsa, a cewarta karya isheta.
Mi kuma ta tuna oho mata, sai ta miƙo hannu ta amsa.
Salman da Aamilah suka fara maido masa da kwalaben suna faɗin sudai bama su gane kan maganinba, kwalayen kwalaben ya miƙa musu duk suka saka da kansu sannan ya amsa ya maida ajikka.
Jack ya kalli Dr Tayyeb cikin nuna shiɗin ƙwararrene yace, “Wannan ai maganin hana ɗaukar cikine, macen da bata haihuwama akan bata ta gwada shi kamar na wasu wattani kafin ta dakata”.
Murmushi Dr Tayyeb yayi yana jin jina kai alamar gamsuwa da bayanin jack, ya miƙa masa kwalin shima ya saka yana faɗin, “A lallai kasan magani kam sosai”.
Jack yaji daɗin yabon da ake masa ya miƙama Doctor bayan ya saka a kwalin yana sake bajewa a kujera, suma su Shahudah duk basu yay suka saka ita da Mummy ya amshe abunsa ya maida duka a jaka, ba tare daya yi musu wani ƙarin bayani ba yay musu sallama ya tafi.
Kaf ɗinsu babu wanda ya kawo wani abu a ransa game da maganin da Doctor Tayyeb ya nuna musu, garama Mummy taji haushinsa sosai, dan ita gani take kawai Doctor ɗin nasu yayi hakanne danya nunama Shahudah hanyar ɗaukar mataki a gaba, itako yanda suka tsara yanzu nanda kwanaki kaɗan Shahudah zata koma ɗakinta ko ALLAH zaisa a dace wani cikin ya shiga.
Dan jiya dai ta daure taje gida tama Mama Atika da ƴan uwanta bayani akan matsalar Shahudah ɗin.
Dukansu sun nuna rashin jin daɗinsu da tausayin Shahudah, sai dai kuma hankalinsu ya tashi, dan a ganinsu inhar Shahudah nada wannan matsalar to kenan yaushene ciki zai fara zaman da zasu sami cikar burinsu?.
Uncle Uwaisu daya kasa haƙuri sai cewa yay, “Anya kuwa kuna ganin bazamu ɗauki matakiba? Indai hakanefa zaman Shahudah da Jawaad bazai mana wani amfaniba kenan? Ko dai mu sake dubawa cikin yaran nan saimu aura masa wata?”.
Tsitt falon yayi kowa ya kasa magana, sai dai fuskar Mummy ta nuna alamun ɓacin rai.
Mama Atika ce ta katse shirun nasu dayin gyaran murya, cikin muryarta ta tsufa tace, “Maganar Uwaisu nakan hanya, hakama shawararsa mai ƙyau ce, sai dai akwai ruɗani a cikin hakan musamman akan ku kanku da zumincin ku”.
“Gaskiyane maganarki mama, gashi kuma bamu da damar sako wani cikin ƴan uwanmu, duk da na daɗe daji a raina kowa nada nasa burin wlhy, suna ɓoyewane kawai dan ace sunason yaron sosai, musamman ma Yaya Nasiru da kuke ganinsa nan ko? Humm”.
Nanma duk shiru suka sake yi, sai Mummy ce a hasale tace, “Amma gaskiya idan akai haka ba aima Shahudah adalciba, ai kamata yay mu nema magani ko mafitar da cikin zaike zama ɗin bawai muyi tunanin mata kishiya ba, sannan ku kunama zaton shi yaron kansa zai yarda da wannan kwamacalar? Shahudah ma da yake so da yaya muka ƙulla auren nasu balle kuma yanzu? Mudai sake tunani amma ba wannan ba”.
Kowa ya gamsu da bayaninta, duk da dai ta nuna akwai nuna taya kishin ɗiyarta a ciki.
daga ƙarshe dai sun yanke shawarar nemawa Shahudah magani, sannan su maidota ɗakinta da wuri ko ALLAH zaisa a dace ciki ya shiga da wuri🤫🥴.
★★★★★
Dr Tayyeb da ya samu abinda yazo nema yana fita ya sauke ajiyar zuciya, mota ya shiga bai zauna wasaba ya koma Office ɗin Jawaad.
Lokacin Jay yana tare da su Jabeer akan tsara aikinsu da zasu dasama ɗanba.
Bayan saƙon zuwan Dr Tayyeb yazo masa ta hanyar Gimba, bai fitoba, sai gimban ya bama damar amsar saƙon a wajen Doctor.
Gimba na tsaye Dr Tayyeb na bashi kwalayen kwalaben da duk yasamo fingers print ɗinsu Shahudah sai ga Qaseem ya fito daga Office, da alama ma dai ya tashi aiki, aiko sai idonsa karaf akan su Gimba.
Ɗunbin mamaki ne ya kamashi ganin Family Doctor ɗinsu anan, yay saurin ciro wayarsa daga aljihu ya ɗauki Dr Tayyeb da Gimba hoto.
_____________________
Lokacin da Qaseem ya shigo gidan duk su Shahudah sun tashi, Aamilah ce kawai a falon itama tana cin abincine a dani.
Yanda Qaseem ɗin ya shigone ya saka Aamilah kallonsa ita da Amina dake gyaran falon.
Cikin tsawa-tsawa yace ma Amina, “K tattaro min kowa na gidannan”.
Da “To” Amina ta amsa cikin girmamawa.
Tasowa Aamilah tai daga falon tana tambayarsa ko lafiya?.
Bai bata amsaba sai ƙokarin danna wayarsa yake domin son nemo hoton su Dr Tayyeb daya ɗauka.
A haka duk suka fito suka samesu har Shahudah dake fama da kanta.
Kowa yazo sai ya masa tambayar lafiya?.
Ganin duk sun hallara ya bisu da kallo yana faɗin, “Jawaad yazo gidannan yau?”.
A tare suka girgiza masa kai, kowanne da mamakin tambayar akan fuskarsa.
Qaseem ya kuma cewa, “Doctor Tayyeb fa?”.
Salman yace, “Yazo har yayma Shahudah allura”.
Dariya sosai Qaseem ya sanya yana tafa hannaye, wadda tasakasu duk zuba masa idanu, Mummy ta katsesa, “Qaseem lafiyarka kuwa? Minene abin dariya to anan?”.
“Mummy bazaki ganeba, ni dama nasan Jawaad bazai taɓa bariba, da Tayyeb yazo gidannan bayan allura mi yayi?”.
Aamilah taja gajeran tsaki, “Iya allurar yayi mana, sai wani shirmensa na nuna mana wai ko maganin hana ɗaukar ciki, ni jakinma harya wuce ban fahimci manufarsa ba....”
Saurin katse Qaseem yayi, “K shashasha, aiku ya maida jakkan, to lallai akwai manufa, dan inada tabbacin aiki Jawaad ya sakashi, dan naga Dr Tayyeb a Office ɗinmu yanzunan yana bama gimba drivern Jawaad wasu kwalaye”.
Dukansu idanu suka zaro waje har Jack, dan da turanci duk suke magana saboda Jack ɗin ya fahimta.
Mummy tace, “Ni ban ganeba, kai mika fahimta to?”.
Cikin taɓe baki da ɗage kafaɗu Qaseem yace, “Cikinsa yake bin ba'asi mana, ki binciki ƴarki Mummy dan akwai abinda take ɓoye miki, kuma duk wanda yasan da hannunsa a ciki wlhy ya kuka da kansa dan Jawaad ya fiku iya birkicewa, aikin banza kawai kun jama mutane asara, ku duba nan ku gani” ya ƙare maganar yana mika musu wayarsa a hasale.
Dukansu jikinsu tsuma yake, musamman Aamilah da jack da Shahudah, ita kanta Mummy zuface ke karyo mata a kowacce ƙofar gashin jikinta, tsabar ɗumi da ƙwalwar kanta ta ɗauka tama rasa abin faɗa.
Dukansu babu wanda baiga abinda Tayyeb ke mikama Gimba ba, kwalaben daya basune fa.
Mummy da jikinta ke mazari ta juya tana kallon Shahudah dake a birkice, kasa ce mata komai tayi.
Ba Mummy da Shahudah ba kowama a birkicen yake, hatta da Salman da baisan komaiba yay wuƙi-wuƙi da idanu.
Daga nan kowa kai kawo ya shigayi a falon.
Shahudah, Aamilah, Jack, kowa yana tunanine akan a ina matsalar take?.
Yaya akai Dr Tayyeb ya je ga Jawaad? Aamilah da tasan yanda sukai da Dr Tayyeb zuciyarta sai tsitstsinkewa take, zargi biyune a ranta, kodai Doctor ya samu Jawaad da gaskiyar batu, kokuma Zaitun ce ta faɗama Jawaad, to amma ai Zaitun batasan wanene zai amfani da allurarba, ita kawai sun nema sanin likitane ta hanyarta, tayaya zata samu Jay da maganar abinda bata sani ba.
“Kenan a ina matsalar ta fito?”.
Aamilah ta faɗa a fili ba tare da ta sani ba.
Duk kallonta sukayi kuwa, Mummy tace, “Aamilah mi kike faɗane?”.
Cikin in ina Aamilah tace, “M... Mummy bance komaiba”.
Qaseem yace, “Humm yarinya zaki magantu ne, ni dama tun randa abun nan ya faru wlhy na fahimci baki da gaskiya”.
Tsaki Aamilah ta ja mai mugun ƙarfi tana harar Qaseem, tace, “To masheranci, ni kaɗai duk faɗin gidannan ka sakama idanu?, sokake ka ƙalamin sheri? Ai bani cikin ke a jikinaba balle kace....”
A harziƙe Qaseem yay kan Aamilah, ta zuba da gudu ta shige ɗaki ta kulle kanta.
Cikin matuƙar fushi Qaseem yace, “Mummy kina gani ko? Ni wannan ƴar iskar yarinyar take faɗama duk abinda yazo bakinta? Ƙanwata ta huɗu?”.
Cikin damuwa Mummy tace, “Qaseem dan ALLAH ku barni naji da abinda ya dameni, Shahudah inhar zubar da cikin nan kikai wlhy kin cutar damu kuwa”.
Sake ɓaci ran Qaseem yayi ganin Mummy ta nuna halin ko in kula da abinda Aamilah tai masa, Shahudah kam bata iya bama Mummy amsaba saboda jirin dake ɗibarta, ganinta kawai sukai zube a ƙasa wanwars.
______★______★_______★______