← Book details Kwai cikin Kaya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 10 OF 75

Sashe 10

Kwai cikin Kaya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

..........A kullum duniya canjama bawa ajin karatu take, yau ɗinkace kawai zata tabbatar maka da hakan, musamman idan kaga ta banbanta da ƙaddarar jiyanka. Rayuwa mataki biyu ce, kowacce ka zaɓama kanka zaka isa zuwa makomarta, saɓanin shine kawai dace wajen banbance nagartacciya ko gurɓatacciya.
A yau dai ga ni a matsayin marainiya, wadda babu ɗumin duka mahaifa guda biyu, sannan babu bangon jingina daga tsatson zuminci ko guda ɗaya. Rayuwata ta cigaba da tafiya a hannun mutanen kirki ahalin fiddausi, sun zamemin uwa da uba bayan ƙasa ta rufe idanun nawa, yanzu sune ci na sune shana da dukkan buƙatun rayuwa da aljihunsu sai iya ɗauka.
Zuciyata na kewar iyayena, amma jarumtata na ɓoye hakan a koda yaushe, haƙuri kuma ya zamemin sandar jagora yayin tafiya ba tare da na lalubi hanya ba saboda makantar zuci.
Tabbas rayuwar gidanmu ta canjamin ta kowanne ɓangare, dan a lokacin da iyayena na raye akanji shakkar min wani abun, amma yanzu kam ƙiri-ƙiri wasu kan nuna ƙyamata ko hantara ta ma kai tsaye, idanun maman firdausi ne kawai kan hana wasu cin zarafina koda da harara ne, amma da zaran babu ita a tsakar gidan to kare ma ya fini daraja.
Matsala ta farko dana fara cin karo da ita a gidan mai ƙona zuciya da barin tabon da ba'a mantawa shine zuwan mai gidan Alhaji lado naira, koda iyayena suka rasu bana tunanin Alhaji lado yazo gidan gaisuwa sam, amma rana tsaka sai gashi danƙyas-danƙyas yazo koramin bayanin na kwashe kayana daga ɗakinmu zai zuba ƴan haya.
Cikin ƙarfin hali da dogaro da kuɗin hayarmu na shekarar basuyi ko rabi ba na shiga kora masa bayani akan ai da sauran lokacin tashinmu.
Alhaji Lado ya bankamin harara tare da watsamin yatsun hannunsa biyar cif alamar zagi (daƙuwa) “Kinci uwarki, kujimin lalatacciyar yarinya, yo ko yau kuka biya tunda wanda yay biyan ya tafi barzahu ai kuɗinku sunyi isfaya (expire) kuma, to dan shelen uwarki ma😱, gidan tsohonki ko nawa da har zaki zauna jamin sharaɗi. Maza tashi kiyo waje da komai tafe nake da mai fenti, ki zauna wannan bacar har kuɗin su kare, dan itama zaki fara biyan kuɗin hayane tunda yanzu ƙofar ɗakin wasune”.
Kasare nai ina kallonsa tamkar wata wawuya ko sokuwa, wasu da ga jama'ar gidan ko dariya suketa tuntsurawa, ƙalilanne basu ji daɗin lamarin ba, amma babu wanda yace ma Alhaji lado baiyi dai-dai ba, dan sunajin tsoron ya shuka musu shika-shikan rashin arziƙinsa suma, kaɗanma da ga aikinsa yace kaima ka tashi ka bashi ɗakinsa. Baka da yanda zakai dashi kuma dolenka ka tashi, inba hakaba ya saka yaransa subi tsakkiyar rana ko duhun dare su naɗa maka na jaki🤦🏻‍♀️.......
Tsawar da ya dakamin ce ta sakani zabura na miƙe tsaye, ya nunamin ƙofar ɗakinmu yana haɗe fuska tamkar kashin ƙato na farar safiya.
Jikina na ɓari na nufin ɗakin, dan fuskar Alhaji lado tafi baƙin kashin shanu barazana idan ya murkite ta, ina shiga itama firdausi na shigowa, itace ta taimaka min wajen haɗe kayan muka ƙuƙƙulle ina sharar ƙwalla, sauƙina ɗaya ma kayan bawani uban yawane da suba, marasa amfanin ciki kuma sunfi masu amfanin yawa.
Bayan mun gama haɗesu ta taimaka min muka fiddosu zuwa cikin bacar da muke kwana, wadda kayan suka mamaye kusan rabinta, dan dama bawani girman azo agani bane da ita.
Alhaji Lado bai kuma bi takaina ba sai ma yaransa da suka shiga suka fara fente ɗakin da fenti mai ƙyau da ya bama kowa mamaki, dan duk ɗakunan gidan da farar ƙasa aka shafesu maimakon fenti🤦🏻‍♀.

Da daddare munacin abinci a ɗakin su Firdausi innarsu ke bani haƙurin abinda ya faru da rana, dan ɗazun bata da sukunin nuna tausayina suma ta shafesu, shiyyasa sukai gum da ga ita har baba.
Murmushi nai mai ciwo ina faɗin, “Babu komai inna, ALLAHN da ya bashi muma bai manta da muba ai”.
“Hakane Bilkisu” inna ta faɗa tana murmushi, ta dafa kafaɗa ta tana ƙara nuna min muhimmancin haƙuri da amfaninsa.
Naji daɗin bayaninta, dan naƙara samun ƙwarin gwiwar ɗaura ɗammarar zama jaruma akan kaina.

★★★★★★

Faruwar hakan da kwanaki biyu kacal waɗanda zasu zauna a ɗakin suka tare.
Abinda ya tada hankalin dukkan jama'ar gidan, shine wanda zai tare a ɗakin da muka zauna.
Kusan sha biyun rana saiga ƙattai suna shigowa da kaya cikin gidan, waɗanda kallo ɗaya zakai musu ka fahimci addu'a kawai rayuwarsu take buƙata. Sune suka saka komai a ɗakin suka gyarashi tsaf, duk da bamu shigaba munsan dolene ya haɗu, dan kayan da akaita shiga dasu babu ma mai kwatankwacinsu a cikin gidanmu.
Mun daɗe bamu da wutar nefa a gidanmu, amma sai gashi anzo a ranar an gyara, washe gari kuma sai ga masu gyaran fanfo tunda farar safiya.
Irinmu da bamusan wanene zai tare a ɗakinba dai mamaki ya matuƙar kamamu, burinmu muga wanene zai zauna a ɗakin kawai.

Da yamma gan da magriba mun dawo islamiyya mukaci karo da baƙon lamarin da sam ada babu kwatankwacinsa a gidanmu. Kana kusanto gidan kunnenka zai fara jiyo maka sautin kiɗa da ke tashi da ƙarar Janareto (Genretor).
Kallon juna mukai ni da firdausi, dan munsan dai babu wani shagali da akeyi a gidan, koma anayi ba'a taɓa kalar wannanba.
Badai muce komaiba muka shigo da sallama a bakunanmu. Fetal tsakar gidan yake tamkar babu wani mahaluki mai numfashi, gidanmu da idan ka shigo da yamma zaka ɗauka biki muke sai gashi tsitt, idanunmu suka sauka akan matasan samari da adadinsu zai kai goma sha uku acan jikin ɗakinmu da muka tashi, wanda bacar da muke kwana ni da firdausi take kallonsa, Mutum ɗaya ne zaune a kujera kawai yana zuƙar sigari, sauran kuma duk suna saman tabarna babba da aka shinfiɗa, wasu karta sukeyi, wasu kuwa zaune suke suna kallon masu kartar, sai ɗaya dake matsama na zaune saman kujerar ƙafa tamkar wani sarki.
Kallon juna muka sake yi ni da firdausi, yayinda suma matasan samarin suka zubo mana idanu su duka.
Gyaran murya da na kan kujerar yayne ya saka dukkan samarin saurin nutsuwa kowa yana sunkuyar da kai.
Baice uffanba shikam, sai zuba mana idanu da yay yana ƙare mana kallo da ga sama har ƙasa duk da sanye muke cikin hijjabai har kusan ƙasa.
Firdausi ce tai ƙarfin halin kama hannuna muka cigaba da takawa dogon tsakar gidan muna dosar inda samarin suke, dan ɗakin su firdausi shine jikin nami dama can, sannan bacarmu a tsakanin ƙofar su firdausi da ɗakinmu na da inda samarn suke yanzu take, hakan yasa samarin suke zaune har ƙofar bacarmu da gaban ɗakin iyayen firdausi.
Duk da munga a yanayin da suke da bana mutanen kirkiba, ga kuma kiɗan dake tashi da bamu da tabbacin zasujimu, hakan bai hanamu gaishesu ba. A mamakinmu sai mukaji suna amsawa kuwa, wanda ke kan kujerarne kawai bai amsaba, kuma har yanzu idanunsa na kanmu.
Wanda ke zaune saman ƙofar su firdausi ne ya matsa mana fahimtar da yay kamar nan zamu shiga, cikin sassarfa muka faɗa ɗakin kuwa da hanzarinmu ko sallama babu.
Maman firdausi dake zaune ta miƙe zumbur tana nufomu, hannunmu ta kama zuwa tabarma jikinta har rawa yake.
Mamaki ya sake kamamu, mun buɗe baki zamuyi magana tai azamar mana nuni da muyi shiru. Shirun kuwa mukayi muna cigaba da binta da kallo.

Haka mukai kwannan yau babu wani sikuni ga jama'ar gidan, kowa ya maƙure a ɗakinsa yana tsoron fitowa, mu kanmu yau a ɗaki ɗaya muka kwana da iyayen firdausi, baba ya hanamu zuwa bacarmu.

*MAFARIN MATSALA*

Baƙon dai da ya tare a ɗakin da na taso tun ƙuruciya na ganni a ciki matsayin namu, ɗan Alhaji Lado Naira mai suna Jazuli (Jazuuuga) ne ya tare.
Jazuli ko nace Jazuuuga ɗane na huɗu ga Alhaji lado, shine namiji da aka fara haifa masa a gidansa, yana matuƙar ƙaunar yaron tun yana ƙaraminsa, hakanne yasa ya tashi a sangarce, sam Jazuuuga bayaji tun bai kai girma ba, tun yana secondary sukul ya haɗa dabarsa, yana da yara masu take masa baya da haɗarinsu ya sa ake matuƙar tsoronsa, duk yanda kuke tunanin takadaranci irinna Jazuli abin ya wuce gaban nan, bayan ya kammala sakandire dinne kuma baban nasa ya ƙarama sheɗancin nasa armashi ta hanyar fiddashi karatu can kudancin ƙasar, acewarsa zaifi samun ilimi acan.
Karku tunanin ilimin Jazuli ya nema koda yaje can ɗin, sam yama manta karatune ya kaishi, ya shige cikin manyan marasa jin magana yay kane-kane yana ɗaukar nasa karatun acan, tsawon shekara biyar iya abinda ya ƙaro ilimi a kansa kenan, idonsa ya matuƙar sake bushewa, ya zama jan wuya na sosai.
Abinda ya maido Jazuuuga gida kuwa kashe oga kwata-kwata na ƙungiyarsu da yay ne, hakanne ya sakashi gudowa ya dawo gida dan yasan dai idan yazo nan ya tsira.
Duk da hankalin Alhaji Lado ya tashi akan halin da ɗansa ya sake ƙwarewa a kai hakan baisa ya daina masa gata ba, saima ya ninka, a cewarsa ai hakanne zaisa ya shiryu.
Ɓarin kuɗin da Alhaji Lado kema Jazuli ne ya bashi damar jan ra'ayin yara takadarai irinsa, wasuma abun nasu ƙaramine, amma saiya horar dasu matsayin sojojinsa, ya haɗa ƙungiya mai matuƙar haɗari da barazana.
Akwai dalilin da yasa Jazuuga ya dawo gidan hayar na mahaifimsa, dukda gidansu kuwa yaci yluban wannan sau fiye da goma, ga kayan alatu da morewar rayuwa a cikinsa, amma saboda son samun cikar burinsa shine ya cema mahaifinsa nan yakeson zama, babu ɓata lokaci kuma Alhaji Lado ya zo ya tada Bilkisu da ga ɗakinsa aka gyarama Jazuuuga...............✍🏻

*_ALLAH ka gafartama iyayenmi_*😭🙏🏻*_Typing📲_*

*_🧺ƘWAI_* _cikin_ *_ƘAYA!!🧺_*

*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

*_Wattpad:-_* _BilynAbdull😉_

*______________________________________*
*_BOOK ONE_*
_Shafi na bakwai_
*______________________________________*

*_JAWAAD_*

............Cikin ƙunar zuciya da ɗacin da ya keji akan halayyar Shahudah yay shirin fita a gaggauce domin komawa Office. Bai bawani ɓata lokaci ba ya fito cikin shigar ƙananun kaya sai zabga ƙamshi yakeyi.
Chapter 10 · 0% Book details