Sashe 28
Kwai cikin Kaya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
...........Wai nikam kukan mi kike Sister? Ni yanzufa lamarinki har mamaki yake bani, akan Brother Jawaad duk kin zama wata lusara.
Hararar Aamila Hajiya Humaira tayi, hakan yasa ta ɓame bakinta.
Ta mai da kallonta ga Shahudah dake kwance a kafaɗarta, “Babie na tashi muyi magana”.
Tashi Shuhudah tayi zaune, Hajiya Humaira tace, “miya sakaki kuka?”.
Cikin tsagwaron taɓara Shahudah ta fara magana da shashshekar kuka, “Momy wai ni yau Bb yake iya cewa na zaɓi ciki koshi? Harni yake iya furtama zai saki akan cikin da bai gama zama mutumba ma, dama ashe baya sona ban saniba....”
Ta rushe da kuka tana faɗawa jikinta.
Hajiya Humaira tai murmushi tana buga bayan Shahudah, “Ba sonkine bayayiba Shahudah, wannan abun daya ambata miki ma shine ya nuna yana tsananin sonki, duk wanda yake son haɗa jini da kai aikuwa yana sonka Shahudah”.
Shahudah ta ɗago da sauri baki a kumbure, “Wlhy Momy baya sona, tunda har bazaiso abinda nake soba, ni gaskiya ban shirya haihuwa yanzuba, salon nazo na tsufa yaje yana kallon wasu a waje ko?”.
Dariya Aamilah ta kwashe dashi tana faɗin, “Tab ashe su wata ta kusa komawa jagwal, na rantse karma ki yarda, toke ta yaya kikai sake ciki ya shiga jikinki ma?”.
“Zanci ubanki Aamila, tashi kibar ɗakinnan” Hajiya Humaira ce tai maganar a zafafe.
Hakan yasa Aamila tashi ta fita tana ƙunƙuni da buga ƙafa na rahin samun isashshiyar tarbiyya.
“Mamana karki biyema Aamila kinji, ki kwantar da hankalinki akan wannan cikin tunda yazo a kuskure, koshi kaɗai kika haifa ya isa haka, zuwa nan gaban idan kinso saiki ƙara ɗin, kinsan dai Jawaad yanada Zuciya idan aka ƙure haƙurinsa, kaɗan daga aikinsa ya aikata dukkan abinda ya faɗa, kuma Abbanku ma yaji faɗa zai miki, insha ALLAH haihuwar wannan cikin sai dai ya ƙara miki daraja a wajen Jawaad badai ya rage mikiba, ALLAH yasa ki haifa mana little Jawaad dai mu shine babban fatanmu”.
Shahudah dai da maganar bata gama shigarta ba tace, “Yanzu kowa dai baya sona a gidannan, ni wlhy barmuku ƙasar zanyi to, dama saboda shi na dawo cikinta, tunda ya fara wulaƙantani gara nai gaba abuna”.
“Kefa wata sa'in baki da man kai Shahudah, lokacin da ake nuna miki Annabi saiki ta ƙoƙarin rimtse idonki haba, banason shashanci mana, to wlhy ki tabbata inhar kika zuba da cikinnan ba Jawaad kaɗaiba hatta ni da Abbanku mantawa zamuyi dake shasha kawai mai girman banza”.
Yanda Hajiya Humaira ta fusata sai abun ya bama Shahudah mamaki, hakane yasaka ta tsura mata ido kawai, miyasa kowa kejin haushinta akan wannan cikin? Tana kallo Hajiya Humaira ta fice ta barta, kwanciya tai ta rushe da kuka, sai da tayi mai isarta sannan dabarar kiran Qaseem tazo mata.
Bugu ɗaya kuwa ya ɗaga, cikin kuka ta sanar masa da duk abinda ke faruwa.
Da farko shima kamar zai mata masifa akan zubda cikin sai kuma yay saurin haɗiyewa ya kwantar da murya.
“Haba Shahudah na, manta kawai da batunsu, koni banso kika ɗauki ciki yanzuba, amma kuma yaya muka iya, ni badan ina tsoron akan ance idan mata sukaje zubda ciki suna mutuwa ba da dakainama zan kaiki a zubar dashi gaskiya”.
“Broth da gaske wai ana mutuwar dan ALLAH?”.
“Da gaskene fa Dear”.
“Tab wlhy banson na mutu, amma kuma ai itama haihuwar wlhy ance ana mutuwa”.
“Eh amma ai kinga bakamar idan za'a zubar da cikiba, ki kwantar da hankalinki kawai kinji Sweetsister, ke dai kawai kina haihuwar wannan ki ɗauki mataki kinji”.
Haka yayta lallaɓata da kalamai masu sanyi harta aminta da zancensa.
Bayan sun ajiye wayar yay ƙwafa, wlhy badan shima yana da buri akan cikinnan na jikin Shahudah ba da sai ya sakata zubdawa koda ya baƙanta ran Jawaad, dan yasan zubda cikinnan ba ƙaramin sukar zuciyarsa zaiyiba, amma babu komai, idan yasha a wannan ai bazai sha ba anan gaba.
Itakam Shahudah shawarar Qaseem ce ta sakata yarda zata bar ciki, amma wlhy saita rama wulaƙancin da duk Jawaad yay mata a gidannan, bazata sake ɗaga masa ƙafaba daga yanzu....
_______________________
BILKEESU
_______________________
Gidan nasu bawani mai ƙyau bane, ginine dai irin na masu ƙaramin ƙarfi, darene shiyyasa bazan iya ƙarar da komai ba dan gane da tsarinsa, gashi anguwar babu wuta.
Mun shiga da sallama bayan ya ajiye napep ɗinsa inda yakan ajiyeta, gidan shiru kamar babu kowa, sai muryar mutum ɗaya da najiyo ta amsa, ta fito tana ƙoƙarin ɗaura zaninta, amma ganinmu sai ta tsay turus tana haɗe fuska.
“Wannan fa?” ta faɗa muryar ta na ɗaukar zafi.
Ina jinsa yay gajeren tsaki, kamar bazai bata amsaba sai kuma naji yace, “Inna tai barcine?”.
“Ni ban saniba” tai maganar tana juyawa fuska a kumbure.
Kansa kawai ya girgiza ya nufi ɗakin dake can wani ɗan lungu yana min nuni dana biyosa.
Munyi sallama amma ba'a amsaba, ya ƙarasa shiga ɗakin nima ina biye dashi a baya.
“Inna harkun kwantane?”
Tsohuwar dake kwance mai tsananin kamanni da Innata ta ɗaga masa hannu cikin yanayin barci tana faɗin, “Uhm, ka dawo da wuri haka?”.
“Eh wlhy inna, amma ina tare da baƙuwane”.
Babu shiri ta tashi zaune, takai hannu ta ƙara hasken fitilar dake ajiye saitin fuskarta ɗakin yay fayau.
“Aibo baƙuwa daga ina kuma a tsohon darenan?”.
Sai da gabana ya faɗi dajin furucinta, amma amsar da naji ɗan nata na bata ce ta sakani sauke ɓoyayyar ajiyar zuciya.
“Inna zan miki bayani da safe, yanzu dai gata nan bara na samo mata abinci wajen Lawusa”.
Kamar zatai magana sai kuma ta fasa, ta kalleni fuska babu walwala tana min nuni da wajen zama, zama nayi jikina duk a sanyaye, dan banga alamun zan samu karɓuwa ananba kam.
Muna zaune shiru kaina a ƙasa saiga Shu'aibu ya dawo ɗauke kula, a gabana ya ajiye yana faɗin, “ƙanwata maza kici saiki samu ki kwanta kinji”.
Godiya nai masa, na buɗe kular dan yunwa nakeji, Taliya da wakene a ciki, ban cutama kainaba naci na ƙoshi, dan rabon da na samu nutsuwar cin abinci haka tun ranada zan buge Jazuga.
Tabarma Inna ta bani, na shimfiɗa inda nake zaune na kwanta, filoma sai da ledar da Sani ya bani wadda bansan ko minene a cikina nai filo, kafin kace kwabo barci mai nauyi yay awon gaba dani.
Ban sake sanin halin da ake cikiba sai da asuba da inna ta tasheni nayi sallah.
Ina daga inda nai sallar ne na gaisheta.
Ta amsa min cikin halin ko in kula ta fice abinta, lallai nasan akwai matsala, a yanzuma batasan koni wacce ba ban damu karɓa daga gareta ba inaga ta ji wacece ni?.
Haka na zabga tagumi ina komawa duniyar tunanin yanda rayuwa take tamkar juyawar ƙarfunan agogo, wani lokacin sai kaga komanka nata maimaici bisa ga matsalolin rayuwa, idan kai wasa tuni kake aikata saɓo koda afurucine.
Shigowa inna da Shu'aibu ta katse mani tunani, na gaida shi bayan sun zauna.
Cike da fara a ya amsa yana tambaya ta ya baƙunta?.
Nai ɗan murmushi mai sauti ba tare dana iya cewa komaiba.
Hankalinsa ya maida ga inna daketa faman taɓe baki tana kallonmu, “Inna kinsan wacece kuwa wannan?”.
“Yazan sani baka faɗaba Aibo”.
Ƴar dariya yayi yana gyara zama, yace, “Kalleta da ƙyau dawa tai miki kama?”.
Kallona Inna tayi, sai kuma taɗan taɓe baki, “Yo kai banda abinka Aibo ina nake ganin fuskarta, tunda ta shigo gidannan banda sinne kai da take kamar sabuwar amarya mi takeyi”.
Saurin ɗago kaina nai na kalleta, sai dai kuma ban jureba na janye idanuna, amma dai nasan yanzu zataga fuskar tawa kamar yanda take buƙata.
Inajin yanda idanunta ke yawo a jikina, zuwa wasu mintuna kamar biyu tace, “Ina gano kamannin Zubairu da Asiya tare da ita kuwa Aibo”.
Dandanan bakin Shu'aibu ya washe, cike da zumuɗi yace, “Masha ALLAH, ai ɗiyar Inna Asiyar ce kuwa inna”.
“Ɗiyar Asiya? Kai ina ka samota haka?”
Inna ta faɗa cike da mamaki.
Murmushinsa ya faɗaɗa, tas a yanda muka haɗu jiya sai ya sanar mata, sai jinjina kan mamaki takeyi, ta juyo gareni tana tambayata daga ina nake haka har shi Shu'aibu ya ganoni?.
Da farko nayi niyyar faɗa musu gaskiya, amma yanayin Inna da naga har sannan bawani ɗokin ganina taiba saina canja zancena kawai, na faɗa musu iya abinda zasu iya amsata game da nemnsu kawai na fitoyi dan nagaji da zama ni kaɗai.
Kai inna ta jinjina, babu ko jin nauyina tace, “Amma kai Aibo kana ganin riƙon babbar budurwa kamar wannan bazai zamar mana wani tawayaba? Mu dai ba kuɗin aurar da ita ke garemu ba kaima kasan haka, ga ɗan karen kishin matarka da batason ganin wata mace ta raɓeka, inaga mu taimaka mata da wani abun ta koma inda ta fito tai haƙuri kamar yanda kowa keyi a nasa gida.
Murmushi nayi mai ciwo hawaye na taruwa cikin idona, wato sai yanzu na fahimci abinda yasa dangina ke gudun ɗaukata, ashe hidimar aurar danice damuwarsu kawai, to nida banida ko saurayi wane maganar aurena za'ayi kuma?, maganar shu'aibu ta katseni.
“Haba inna, wannan wace irin maganace haka, koba komai ai Bilkisu abar tausayice, ALLAH kuma shine zai buɗa mana mu sauke dukkan nauyinta gwargwadon iko, dan riƙe maraya ba ƙaramin alkairi bane da falala ga bawa, amma yanzu sai kowa ke gudun hakan, kifa tuna mahaifinku ɗaya da inna Asiya, na tabbata kuma da itace a raye zata riƙe naku ƴaƴan ai, sa......”
“Nikam naji gwanin iya magana, tunda kaji ka gani ta zauna ga fili nan, ni dama dai kai nake tausayi, tunda dukkan ƙarfin riƙe gidannan kaine keyi”.
Cikin jin daɗi yace, “Nagode da amincewarki inna, ALLAH ya tayamu riƙo”.
Hararar Aamila Hajiya Humaira tayi, hakan yasa ta ɓame bakinta.
Ta mai da kallonta ga Shahudah dake kwance a kafaɗarta, “Babie na tashi muyi magana”.
Tashi Shuhudah tayi zaune, Hajiya Humaira tace, “miya sakaki kuka?”.
Cikin tsagwaron taɓara Shahudah ta fara magana da shashshekar kuka, “Momy wai ni yau Bb yake iya cewa na zaɓi ciki koshi? Harni yake iya furtama zai saki akan cikin da bai gama zama mutumba ma, dama ashe baya sona ban saniba....”
Ta rushe da kuka tana faɗawa jikinta.
Hajiya Humaira tai murmushi tana buga bayan Shahudah, “Ba sonkine bayayiba Shahudah, wannan abun daya ambata miki ma shine ya nuna yana tsananin sonki, duk wanda yake son haɗa jini da kai aikuwa yana sonka Shahudah”.
Shahudah ta ɗago da sauri baki a kumbure, “Wlhy Momy baya sona, tunda har bazaiso abinda nake soba, ni gaskiya ban shirya haihuwa yanzuba, salon nazo na tsufa yaje yana kallon wasu a waje ko?”.
Dariya Aamilah ta kwashe dashi tana faɗin, “Tab ashe su wata ta kusa komawa jagwal, na rantse karma ki yarda, toke ta yaya kikai sake ciki ya shiga jikinki ma?”.
“Zanci ubanki Aamila, tashi kibar ɗakinnan” Hajiya Humaira ce tai maganar a zafafe.
Hakan yasa Aamila tashi ta fita tana ƙunƙuni da buga ƙafa na rahin samun isashshiyar tarbiyya.
“Mamana karki biyema Aamila kinji, ki kwantar da hankalinki akan wannan cikin tunda yazo a kuskure, koshi kaɗai kika haifa ya isa haka, zuwa nan gaban idan kinso saiki ƙara ɗin, kinsan dai Jawaad yanada Zuciya idan aka ƙure haƙurinsa, kaɗan daga aikinsa ya aikata dukkan abinda ya faɗa, kuma Abbanku ma yaji faɗa zai miki, insha ALLAH haihuwar wannan cikin sai dai ya ƙara miki daraja a wajen Jawaad badai ya rage mikiba, ALLAH yasa ki haifa mana little Jawaad dai mu shine babban fatanmu”.
Shahudah dai da maganar bata gama shigarta ba tace, “Yanzu kowa dai baya sona a gidannan, ni wlhy barmuku ƙasar zanyi to, dama saboda shi na dawo cikinta, tunda ya fara wulaƙantani gara nai gaba abuna”.
“Kefa wata sa'in baki da man kai Shahudah, lokacin da ake nuna miki Annabi saiki ta ƙoƙarin rimtse idonki haba, banason shashanci mana, to wlhy ki tabbata inhar kika zuba da cikinnan ba Jawaad kaɗaiba hatta ni da Abbanku mantawa zamuyi dake shasha kawai mai girman banza”.
Yanda Hajiya Humaira ta fusata sai abun ya bama Shahudah mamaki, hakane yasaka ta tsura mata ido kawai, miyasa kowa kejin haushinta akan wannan cikin? Tana kallo Hajiya Humaira ta fice ta barta, kwanciya tai ta rushe da kuka, sai da tayi mai isarta sannan dabarar kiran Qaseem tazo mata.
Bugu ɗaya kuwa ya ɗaga, cikin kuka ta sanar masa da duk abinda ke faruwa.
Da farko shima kamar zai mata masifa akan zubda cikin sai kuma yay saurin haɗiyewa ya kwantar da murya.
“Haba Shahudah na, manta kawai da batunsu, koni banso kika ɗauki ciki yanzuba, amma kuma yaya muka iya, ni badan ina tsoron akan ance idan mata sukaje zubda ciki suna mutuwa ba da dakainama zan kaiki a zubar dashi gaskiya”.
“Broth da gaske wai ana mutuwar dan ALLAH?”.
“Da gaskene fa Dear”.
“Tab wlhy banson na mutu, amma kuma ai itama haihuwar wlhy ance ana mutuwa”.
“Eh amma ai kinga bakamar idan za'a zubar da cikiba, ki kwantar da hankalinki kawai kinji Sweetsister, ke dai kawai kina haihuwar wannan ki ɗauki mataki kinji”.
Haka yayta lallaɓata da kalamai masu sanyi harta aminta da zancensa.
Bayan sun ajiye wayar yay ƙwafa, wlhy badan shima yana da buri akan cikinnan na jikin Shahudah ba da sai ya sakata zubdawa koda ya baƙanta ran Jawaad, dan yasan zubda cikinnan ba ƙaramin sukar zuciyarsa zaiyiba, amma babu komai, idan yasha a wannan ai bazai sha ba anan gaba.
Itakam Shahudah shawarar Qaseem ce ta sakata yarda zata bar ciki, amma wlhy saita rama wulaƙancin da duk Jawaad yay mata a gidannan, bazata sake ɗaga masa ƙafaba daga yanzu....
_______________________
BILKEESU
_______________________
Gidan nasu bawani mai ƙyau bane, ginine dai irin na masu ƙaramin ƙarfi, darene shiyyasa bazan iya ƙarar da komai ba dan gane da tsarinsa, gashi anguwar babu wuta.
Mun shiga da sallama bayan ya ajiye napep ɗinsa inda yakan ajiyeta, gidan shiru kamar babu kowa, sai muryar mutum ɗaya da najiyo ta amsa, ta fito tana ƙoƙarin ɗaura zaninta, amma ganinmu sai ta tsay turus tana haɗe fuska.
“Wannan fa?” ta faɗa muryar ta na ɗaukar zafi.
Ina jinsa yay gajeren tsaki, kamar bazai bata amsaba sai kuma naji yace, “Inna tai barcine?”.
“Ni ban saniba” tai maganar tana juyawa fuska a kumbure.
Kansa kawai ya girgiza ya nufi ɗakin dake can wani ɗan lungu yana min nuni dana biyosa.
Munyi sallama amma ba'a amsaba, ya ƙarasa shiga ɗakin nima ina biye dashi a baya.
“Inna harkun kwantane?”
Tsohuwar dake kwance mai tsananin kamanni da Innata ta ɗaga masa hannu cikin yanayin barci tana faɗin, “Uhm, ka dawo da wuri haka?”.
“Eh wlhy inna, amma ina tare da baƙuwane”.
Babu shiri ta tashi zaune, takai hannu ta ƙara hasken fitilar dake ajiye saitin fuskarta ɗakin yay fayau.
“Aibo baƙuwa daga ina kuma a tsohon darenan?”.
Sai da gabana ya faɗi dajin furucinta, amma amsar da naji ɗan nata na bata ce ta sakani sauke ɓoyayyar ajiyar zuciya.
“Inna zan miki bayani da safe, yanzu dai gata nan bara na samo mata abinci wajen Lawusa”.
Kamar zatai magana sai kuma ta fasa, ta kalleni fuska babu walwala tana min nuni da wajen zama, zama nayi jikina duk a sanyaye, dan banga alamun zan samu karɓuwa ananba kam.
Muna zaune shiru kaina a ƙasa saiga Shu'aibu ya dawo ɗauke kula, a gabana ya ajiye yana faɗin, “ƙanwata maza kici saiki samu ki kwanta kinji”.
Godiya nai masa, na buɗe kular dan yunwa nakeji, Taliya da wakene a ciki, ban cutama kainaba naci na ƙoshi, dan rabon da na samu nutsuwar cin abinci haka tun ranada zan buge Jazuga.
Tabarma Inna ta bani, na shimfiɗa inda nake zaune na kwanta, filoma sai da ledar da Sani ya bani wadda bansan ko minene a cikina nai filo, kafin kace kwabo barci mai nauyi yay awon gaba dani.
Ban sake sanin halin da ake cikiba sai da asuba da inna ta tasheni nayi sallah.
Ina daga inda nai sallar ne na gaisheta.
Ta amsa min cikin halin ko in kula ta fice abinta, lallai nasan akwai matsala, a yanzuma batasan koni wacce ba ban damu karɓa daga gareta ba inaga ta ji wacece ni?.
Haka na zabga tagumi ina komawa duniyar tunanin yanda rayuwa take tamkar juyawar ƙarfunan agogo, wani lokacin sai kaga komanka nata maimaici bisa ga matsalolin rayuwa, idan kai wasa tuni kake aikata saɓo koda afurucine.
Shigowa inna da Shu'aibu ta katse mani tunani, na gaida shi bayan sun zauna.
Cike da fara a ya amsa yana tambaya ta ya baƙunta?.
Nai ɗan murmushi mai sauti ba tare dana iya cewa komaiba.
Hankalinsa ya maida ga inna daketa faman taɓe baki tana kallonmu, “Inna kinsan wacece kuwa wannan?”.
“Yazan sani baka faɗaba Aibo”.
Ƴar dariya yayi yana gyara zama, yace, “Kalleta da ƙyau dawa tai miki kama?”.
Kallona Inna tayi, sai kuma taɗan taɓe baki, “Yo kai banda abinka Aibo ina nake ganin fuskarta, tunda ta shigo gidannan banda sinne kai da take kamar sabuwar amarya mi takeyi”.
Saurin ɗago kaina nai na kalleta, sai dai kuma ban jureba na janye idanuna, amma dai nasan yanzu zataga fuskar tawa kamar yanda take buƙata.
Inajin yanda idanunta ke yawo a jikina, zuwa wasu mintuna kamar biyu tace, “Ina gano kamannin Zubairu da Asiya tare da ita kuwa Aibo”.
Dandanan bakin Shu'aibu ya washe, cike da zumuɗi yace, “Masha ALLAH, ai ɗiyar Inna Asiyar ce kuwa inna”.
“Ɗiyar Asiya? Kai ina ka samota haka?”
Inna ta faɗa cike da mamaki.
Murmushinsa ya faɗaɗa, tas a yanda muka haɗu jiya sai ya sanar mata, sai jinjina kan mamaki takeyi, ta juyo gareni tana tambayata daga ina nake haka har shi Shu'aibu ya ganoni?.
Da farko nayi niyyar faɗa musu gaskiya, amma yanayin Inna da naga har sannan bawani ɗokin ganina taiba saina canja zancena kawai, na faɗa musu iya abinda zasu iya amsata game da nemnsu kawai na fitoyi dan nagaji da zama ni kaɗai.
Kai inna ta jinjina, babu ko jin nauyina tace, “Amma kai Aibo kana ganin riƙon babbar budurwa kamar wannan bazai zamar mana wani tawayaba? Mu dai ba kuɗin aurar da ita ke garemu ba kaima kasan haka, ga ɗan karen kishin matarka da batason ganin wata mace ta raɓeka, inaga mu taimaka mata da wani abun ta koma inda ta fito tai haƙuri kamar yanda kowa keyi a nasa gida.
Murmushi nayi mai ciwo hawaye na taruwa cikin idona, wato sai yanzu na fahimci abinda yasa dangina ke gudun ɗaukata, ashe hidimar aurar danice damuwarsu kawai, to nida banida ko saurayi wane maganar aurena za'ayi kuma?, maganar shu'aibu ta katseni.
“Haba inna, wannan wace irin maganace haka, koba komai ai Bilkisu abar tausayice, ALLAH kuma shine zai buɗa mana mu sauke dukkan nauyinta gwargwadon iko, dan riƙe maraya ba ƙaramin alkairi bane da falala ga bawa, amma yanzu sai kowa ke gudun hakan, kifa tuna mahaifinku ɗaya da inna Asiya, na tabbata kuma da itace a raye zata riƙe naku ƴaƴan ai, sa......”
“Nikam naji gwanin iya magana, tunda kaji ka gani ta zauna ga fili nan, ni dama dai kai nake tausayi, tunda dukkan ƙarfin riƙe gidannan kaine keyi”.
Cikin jin daɗi yace, “Nagode da amincewarki inna, ALLAH ya tayamu riƙo”.