← Book details Kwai cikin Kaya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 21 OF 75

Sashe 21

Kwai cikin Kaya Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Dariyar su ƴar daɓas ce ta sani maida kallona garesu, Nazy tace, “Ƴar daɓas da alama fa Balki hajiya ta fara kaita network, irin wannan suman zaune haka”.
Dariya suka sake kwashewa dashi suna taɓawa.
“Dan ALLAH kumin bayani mana?”.
Cikin dariya ƴar daɓas tace, “bakya bukatarsa a yanzu Balkisu, ki kwantar da hankalinki zaki fahimci komai, mudai fatanmu ki riƙe wannan harkar, dan harkace mai cike da ƴanci, babu ruwanki da wulaƙancin wani banza shi namiji, jinsin dake kallonki a ƙasƙance, ya aureki ya kaiki gidansa yana wulaƙantawa, bakida wani muhimmanci saina haifa masa ƴaƴa da gadin gida, wannan kuwa gashin kanki zakici, sai kinso wata ta saka miki zoben mallaka ma”.
Nikam sunma ƙara ruɗar dani, hakan yasa nai shiru ban sake tambayaba.
Muna nan zaune sai da gidan kusan kashi biyu bisa ukun mutanen gidan suka fice, tsurarun mazan wajenma sun ɗauki ƴammata sun fice, muma tashi mukai muka fito domin komawa gida........

_______________________
JAWAAD
_______________________

...............A yau Jawaad bai koma gidaba, bai kuma nema Shahudah ba, dan tun fitowarsa ya fahimci bata kwana a sashen nasuba, hakan ba wani sabon abu bane a wajensa, dan abu kaɗanne zai haɗasu taje takai ƙararshi.
A wannan daren suka tsara abubuwa masu yawa shi da su Hafeez Umar akan kubutar da Alhaji Sadi kokino (ba giyar yaroba), yanda tsarin nasu yazo komai ya gamsar dasu, dan haka suka kwanta cike da farinciki bayan sun gamawa Jawaad tsiya akan yatashi ya tafi wajen matarsa.
Murmushi kawai yayi, danshi mutumne mai yawan zurfin ciki, bai yarda kowa yasan matsalar gidansaba komai kusancinsa da kai, shiyyasa ko kararsa Shahudah ta kai, idan aka kirasa abinda kawai suke iyaji daga bakinsa shine (ba komai), har ƙannen mahaifiyarsa su Umma bai taɓa zama ya sanar musu matsalar Shahudah ba, sai dai ƴan gidan su Jawaad su kawo musu gulmar.
Jabeer dake gefensa yace, “Boss mufa da gaske mukeyi bazaka kwanar mana ananba, kaje wajen amarya taimaka tausar gajiyar da ka sha yau, mun yafe mata”.
Harara Jawaad ya watsa masa, yaja filo yana kwanciya saman Sofar dake cikin ɗakin tare da zungurin Jabeer da kafa, tashi Jabeer yay a kusa dashi yana dariya da riƙe gefen ƙugunsa da Jawaad ya shura.
Cikin danne abinda ke sukar ransa yace, “Waini korata kukeyine? To babu inda zanje, itace ai tace muyi hirar yaushe gamo”.
Carab Aliyu ya amshe da cewa, “A lallai Shahudah, amaryar tamu mai haƙurice wlhy, mun kwa gode mata, kuma tunda mun fito sai an sake mana sabon biki da bamu ganiba”.
Duk dariya sukayi banda Jawaad daya ɗauke kansa tamkar baisan sunayi dashi bane.....
“Alhaji kayi shiru?” cewar Jabeer yana zungurinsa da biron hannunsa da suka gama rubuce-rubuce”.
Baki Jawaad yaɗan tabe, sai kuma ya tashi zaune yana faɗin, “Kunga kubar wannan shirmen malamai, ya kamata gobe fa kowa yaje yaga iyalansa koda a ɓoyene, kafin komai ya dai-daita”.
Dukansu kallonsa suke da murmushi a fuskarsu, ƙaunarsa na sake shiga musu rai, Aliyu yay karfin halin amsa masa,
“Amma kana ganin babu damuwa Jay? Da kawai an haƙura munbi dukkan sharadin nasu yanda suka faɗa”.
Ajiyar zuciya Jawaad yayi, yace, “Aliy dokarsu ni bata wani dameniba, kawai abinda ya cancanta nake dubawa”.
Kansu duk suka jinjina masa saboda gamsuwa da maganarsa, Hafeez ya miƙe tsaye ya dawo kusa dasu, sai da ya zauna yana kallonsu kafin yace,
“Anya kuwa Jay kana ganin mahaifin Surayya zai bani damar ganinta ita da Suhail?”.
Shiru sukai su duka, kusan sakwan goma Jawaad ya ɗago kansa, guntun murmushi yayi yana dafa kafaɗar Hafeez ɗin, “Karka damu Broth, namaka alƙawarin zan kawo maka Surayya har gidannan itada Suhail, kuma Aliyu da Jabeer hakan inaga ya dace muyi”.
Bai jira amsarsu ba ya tashi ya shige bayin dake cikin ɗakin, duk binsa sukai da kallo a wani irin yanayi mai wahalar fassara.

★★★★★★★

Kamar yanda yay alƙawari washe gari da safe sai da ya cika, dan kuwa duk sai gashi da matansu da ƴayansu, Aliyu ne kawai matarsa bata haihuba, dan aurensu da wata uku abin ya faru, Jabeer kam da yarinyarsa ɗaya Fatima, sai cikin daya barta dashi ta haifi namiji aka saka masa sunansa.
Hafeez kuma yaronsa ɗaya Suhail.
Sunyi murna sosai da ganin juna, hartakai saida Jawaad yay musu hawaye, zare jikinsa yay shima ya nufi gida wajen nasa iyalin dukda yasan ba lallai ya tarar da abu mai daɗiba.

★★★★★★

Zuwa tashin hantsi Shahudah ta koma normal kamar ba itace keta amai da safe ba, faɗan da mama Atika taimata ne ya tilastata saka doguwar rigar jallabiya baƙa a jikinta, amma sai ƙorafi take wai zafi yamata yawa.
Tun mama Atika na tanka mata har tai banza da ita, a haka gayyar ƴan gidansu suka isketa harda mamansu.
Rungume Shahudah tayi tana murna, takai hannu kan cikin Shahudah tana shafawa.
Ƙwaɓe fuska Shahudah tayi tana wani turo baki, “Momy wai kema kina nufin son cikin kikeyine?”.
Hajiya Humaira ta faɗaɗa murmushinta tana zama saman kujerar dake kallon ta mama Atika ba tare data bama Shahudah amsar maganarta ba.
Mahaifiyarsu ta shiga gaidawa, mama Atika ta amsa, tare da faɗin, “Wannan lalatacciyar ƴar taku saikun saita mata zama akan wannan cikin, inba hakaba wlhy zata ɓata komai”.
Wani guntun murmushi Hajiya Humaira tayima mama Atika, “Mama manta da batunta, zamuyi maganar daga baya, idan kuma bataso ai sai a zubar ko”.
Kafin mama Atika ta bada amsa Shahudah tai carab ta cafke maganar, “Yauwa Momy na, ashe kin gane, dama nasan kekam zaki bani goyon baya, kuma zaki saka wancan uban taurin kan Jawaad ya yarda akan hakan, danni a tsarina saina shekara goma gidan miji zan haihu, shima ƴaƴa biyu kawai nake bukata, mace ɗaya namiji sun wadatar dani, idan son samunema na haifesu ƴan biyu kawai, kunga shikenan”.
Babu wanda ya tanka mata a wajen sai Hajiya Humaira da tace, “Tsarinki mai ƙyaune mamana, kuma ni na amince dashi”.
Wannan magana ta Hajiya Humaira taima Shahudah daɗi, saitaji zuciyarta ta samu nutsuwa, tunda mahaifiyarta ta bata goyen baya ko Jawaad bai isa hanata yin yanda tasoba.

Babu wanda ya sake tada zancen har washe gari, sundai aika kiran Jawaad da daddare aka iske bai dawoba, hakan yasakasu fahimtar bazai kwana a gidaba kenan.
Yau ma Shahudah a sashen mama Atika ta kwana, duk da taso ta koma sashenta sai mama Atikar ta hana gudun kar Shahudah taje ta aikata musu ganganci akan yunkurin zubar da cikin, dan tunda ta ambata to zata aikata kuwa.

Motar Jawaad na shigowa family house ɗin ana kaima mama Atika labarin dawowarsa, hakan yasa ta aika a kira matashi, amma saiya maido ɗan aiken da saƙon yana zuwa kawai.
Sunta zuba idon ganinsa amma sukaji shiru, har kusan awa biyu da rabi sai gashi..........✍🏻

https://youtu.be/6YuGtf5lQF8

Maza garzaya domin sauraren cigaban littafin *KARAYAR ARZIƘI* Na Bilyn Abdull a *MANHA HAUSA NOVEL'S*.

Ku danna Subscribing domin nuna ƙaunarku garemu, tare da ƙararrawar sanarwa dan samun shirye-shiryenmu a duk lokacin da muka ɗora.

MANHA HAUSA NOVEL'S (Ƙyautar ALLAH).

*takuce, kuma natane, ta hanyar kasancewa da itane zamu sake tabbatar da wanene yafi son wani😉👌🏻😻😻😍😍🥰💃🏻*

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*😭🙏🏻*_Typing📲_*

*_🧺ƘWAI_* _cikin_ *_ƘAYA!!🧺_*

*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*

*_Wattpad:-_* _BilynAbdull😉_

*______________________________________*
*_BOOK ONE_*
_Shafi na goma sha uku_
*______________________________________*

.............“Alhaji akwai matsala fa”.
Jikin Alhaji lado na ɓari yace, “Yallaɓai matsala kuma? Akan mi? Yarinyarce ta gagareku samune ko yaya?”.
“Alhaji ba wannan bane, yarinya kam muna kan nemanta, insha ALLAHU kuma zamu sameta, matsalar danake faɗa akan ɗanka take, harbine a damtsen hannunsa, binciken likita ya tabbatar mana kuma jami'an tsarone suka harbesa a wajen, kuma da alama harbin anyisane bayan awa goma sha ɗaya kafin faruwar rigimarsa da yarinyar, lallai idan labarin nan yaje kunnen manyanmu reshe ne zai juye da mujiya, komai kuma zai iya ɓaci”.
Zufar data jiƙa alhaji lado yasa hannu ya sharce, harshensa har sarƙewa yake yace, “Yanzu miye mafita?”.
“Shine nima abinda na kasa haɗawa a raina gaskiya”.
Alhaji Lado yay shiru yana kallon ɗan sandan, sai buga hannunsa daya dunƙule yake cikin ɗayan, cikin taune leɓe yace, “Ni ga tawa shawaran”.
“Ina saurarenka Alhaji”. ‘Cewar ɗa sandan yana kallonsa’.
“Mizai hana shi likitan mu ƙara masa kuɗi ya rufe zancen da dabarunsa, dan gaskiya inason a kamo wannan yarinyan, cikin abokansa sun tabbatar min akwai abinda yarinyar tagani a ɗakin my son kwana bakwai da suka shuɗe, kwana biyar kafin faruwar wannan abun kenan, sannan rashin kamata barazanane a garemu baki ɗaya”.
“To Alhaji ka kawo shawara mai ƙyau, sai dai matsalar da nake hasashe kar yazam waɗanda suka harbi yaronka sun san fuskarsa ko wani abu dangane dashi, hakanne kawai zai kawoma shirinmu rashin tasiri”.
Nanma shiru Alhaji Lado yayi, zuwa wani lokaci ya saki wani nishi da ƙarfi, gaba ɗaya ya rasa wane irin tunani kuma zaiyi, yana ƙaunar Jazuli, sam baya buƙatar rasashi, gashi dama har yanzu baima farfaɗoba cikin hankalinsa, dan sosai bugun da Bilkisu tai masa akai ya shigesa har can cikin kansa.
Basu samo mafitaba a wannan zaman, hakan yasa Alhaji lado yace ɗan sandan ya bashi lokaci zuwa safiya zaiyi tunani akai.

_________________________
JAWAAD
_________________________
Chapter 21 · 0% Book details