Sashe 37
Kwai cikin Kaya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ran Jawaad ya ɓaci da ya dawo ya iske Shahudah bata gida, hakanne ya sakashi kiranta amma saita sanar masa tana gidansu, ya tambayeta da izininwa? tahau kansa da masifa, shine kawai ya yanke wayar ba tare daya gama saurarenta ba.
Sam bayason jin zafinta da yake ya cigaba da girmama cikin ransa, dan haka ya tashi yay shirin fita dukda kuwa lokacin ƙarfe tara da rabi na dare, kuma dawowarsa gidan kenan ko hutawa baiyiba.
Da kansa yaja motar dan yabama gimba damar zuwa ya kwanta ya huta.
Kansa tsaye gidan dattijuwarnan ya nufa, yanabin address ɗin da su Hafez suka bashi dalla-dalla.
A ƙofar madaidaicin gida ya tsaida motar dajin tabbacin nanne, dankuwa duk abinda aka kwatanta masa a jikin gidan ya gansa, kashe motar yay sannan ya fito cikin nuna alamun tsantsar gajiyar dake tattare dashi.
Ya kulle motar amma sai bai fitoba ya fara ƙoƙarin yin kira cikin ƙaramar wayarsa.
Bugu uku aka ɗaga, “Gani a ƙofar gida” ya faɗa idonsa akan murfin gidan.
Bansan amsar da aka bashiba daga can naga dai ya kashe wayar yana fitowa a motar, bindigarsa ya ɗauka ya tura a aljiyu sannan ya rufe murfin motar yana mai kulleta gaba ɗaya.
Dai-dai nan dattijuwa mai aiki gidan Alhaji kokino ta fito sanye da lulluɓi.
Da hannu tai masa nuni alamar su shiga, babu musu ya bita, bayan yaɗan wawwaiga bayansa yaga babu alamar kowa a wajen, dukda ma anguwar babu wani isashen haske saboda rashin wutar lantarki.
Gidan bawani babba bane ammafa yasha gyara, dan fes yake sannan kuma da gani babu ƙananun yaran da zasu ɓata.
Zama yay a farar kujerar roba dake ajiye a bangon yamma da yake ƙyautata zaton kicinne, itama ta zauna a ƙofar kicin ɗin bayan ta kawo masa tea tamkar tasan yana buƙatarsa a halin yanzu.
Godiya yay mata kuwa ya ɗauka yana sha.
“Bani da tabbas amma inaji a jikina kasan inda Alhaji yake”.
Jawaad dake ƙoƙarin kai kofin shayi bakinsa ya dakata yana kallonta, leɓensa na ƙasa ya tura cikin bakinsa yana tsotsa tare da kafeta da wani kallon nazari na seconds biyar, sai kuma yay murmushi yana ƙara damƙe kofin shayin da hannu biyu yakai bakinsa ya kurɓa.
Itama kallonsa takeyi har yanzu, sai dai bata sake cewa komaiba.
Jawaad ya cigaba da shan shayinsa kawai idonsa na kallon yanda iska ke kaɗa labulen ɗakin matar.
Yasha kusan rabin kofin shayin sannan ya ajiye yana sauke ajiyar zuciya, idonsa akanta.
“Mama shekararki nawa kina mata aiki?”.
Murmushi dattijuwa tayi tana kallonsa, “Yarona ai mai son kama fara sammako yakeyi”
“Hakane” Jawaad ya faɗa yana shafa kansa cikin murmushi.
“Miyasa take ɓoyemin kanta har yanzu?”.
“Bani da wannan amsar a zahiri da baɗini”.
Kansa ya rausayar kawai, idanunsa na sake rikiɗewa zuwa ja sosai, sai haɗiyar numfashi yake da zafi, hakan yasaka zuciyarsa gudu tare da tsitstsinkewa.......
Mama ta katse masa tunani da faɗin, “Ta bani saƙo na baka”.
Ɗago kansa yay ya kalleta, amma baice komaiba.
“Tace ka sadaukar, a cikin hakan akwai alamar tambaya? Idan kabi diddigi zaka fahimta”.
“Zanyi biyayya, sai dai zan cutu kuma”.
“Shiyyasa nazo maka da maganin hakan”.
Miƙewa Jawaad yay yana kallon agogon hannunsa, “Ina saurarenki, dan lokacina ƙararrene”.
“Karka damu nima komai inayinsa da ƙa'ida. iya ruwa fidda kai, amaryar alhajice mafitarka”.
Jawaad ya juyo yana kallon dattijuwa hannuwansa duka a cikin wandon jeans ɗinsa, “Mimene nata burin?”.
“Kisa da mallakar abinda ya tara”.
Kansa ya jinjina yana murmushi, ahankali ya furta “Abin birgewa”.
Kallonsa mama tayi tana murmushi itama.
Takowa yay ya dawo gabanta yana ɗan jingina da bango, yace, “Shine kikaji a ranar da kika faɗi kenan?”.
Cikin sauke numfashi mama tace, “Kusan haka yarona, sai dai tsoron ya gauraya ne da cin amanar aure, kuma da makusancinsa”.
Hannu ɗaya Jawaad ya ciro a aljihu yana mai shafa fuskarsa, “Idan babu kuskure a hasashena auren manufa tayi da haɗinkan ƙaninsa kenan?”.
“Hasashenka yana kan dai-dai, kamar yanda sukuma ka ruguza musu nasu a ranar da Alhaji zai dawo daga tafiya shi da ita”.
“Zan samu dukkannin bayanan?”.
“Ƙwarai kuwa, harma da wanda baka tambaya ba” tai maganar tana kunce ƙullin haɓar zaninta ta ciro wani ɗan abu ta miƙa masa.
Amsa yay yana sauke numfashi, “Nagode ƙwarai da gaske mama. A sanar mata ina buƙata matuƙa, sannan ke kuma yaushe aikinki zai ƙare a gidan?”.
“Eh to, inada zaɓi biyu ne, sannan dama ɗaya kacal, a koda yaushe za'a iya nemana a rasa”.
“Shikenan, ni zan wuce, a daren yau zan ƙulle bakin zaren”.
“Kariyar ALLAH ta tabbata a gareka tareda rahamarsa akowane lokaci”.
“Amin ya rabbi mama, nagode sosai, da safe Yazeed zai dawo gida”.
Murmushi kawai tai masa, shikuma ya fara taku cike da kasala ya fice daga gidan.
Buɗe motarsa yay ya shiga sannan ya rufe kansa, ya buɗe hannunsa dake rumtse da abinda mama ta bashi, idanu ya tsira masa yana kallo, kusan mintuna uku sannan ya ajiye yana tada motar ya fice daga anguwar.
Tuƙi yake amma hankalinsa kashi sittin baya a wajen, gefen titi ya samu jikin wani ƙyamiz yay fakin motar, ya cire babbar wayarsa a caji ya danna kiran Jabeer, bugu ɗaya ya ɗauka, sai dai yanda yaji muryarsa ya bashi tabbacin ya fara barci ne.
“Barci kake?”.
Jawaad ya faɗa a ƙasan maƙoshi.
Daga can Jabeer yace, “Wlhy kuwa barcine ya figeni a falo ma, yaya kana office ne?”.
“Eh to badai a cikiba, amma ina akan aikine, inasu Aliyu?”.
“Duk gasu muna a tare”.
“Yauwa ku kasance cikin shiri yanzu nima zan iso”.
Bai jira amsar Jabeer ba ya yanke wayar.
Rose ya kira, itama bugu ɗaya ta ɗauka, ko gaisuwarta bai sauraraba ya fara faɗin, “Yanzun nan ki kira number dana baki ranar, ki kirata da wayar dana baki ki sanar mata tazo bayan kamfanin robobi na kwanar gulbi ta sameki, wannan wayar ta ƙawartace wadda da ita suke haɗa komai, dan haka zatazo da sauri”.
“To amma boss kana ganin zatazo a darennan?”.
Tsawa ya daka mata wadda ta sakata firgita har tana neman yadda wayar, ta daiyi nasarar damƙeta da sauri tana faɗin, “Sorry Boss”.
Tsaki mai ƙarfi Jawaad yaja yana katse kiran, dama zuciyarsa a saman maƙoshi take sosai.
Motar ya tayar yaja da uban gudu zuwa gidansa dasu Aliyu ke ciki, shigowarsa falon yasasu miƙewa su duka cikin girmamawa, hannu ya ɗaga musu kawai ya wuce ɗakin da ke cikin falon, mintuna kamar uku sai gashi ya fito da mace da shekarunta ba zasu gaza talatin da biyu ba.
Dukansu sunsan da zamanta, dan haka basu wani damuba, Jawaad ya ciro waya a aljihunsa yay danne-danne yana miƙa mata, karɓa tayi tana kallonsa a yanayin tsoro-tsoro bariki-bariki....
“Ki kira number nan, ki sanar masa kina tare da Alhaji Kokino, yanzunnan tazo bayan kamfanin robobi na kwanar gulbi ta sameki, kuma yanzunnan”.
Bakinta ta taɓe tana kallon Jawaad ɗin, “Yallaɓai to miyasa zanyi hakan? Bayan kasani na sani Alhaji baya tare dani?”.
Bindiga ya ɗora mata a saman kai ba tare daya ce komaiba.
Take jikinta ya fara mazari, ta shiga ƙoƙarin yin abinda yace.
Yace, “Ki tabbatar muryarki ta fita normal babu gargada a cikinta”.
Zufar data fara jiƙa goshinta ta goge tana haɗiye yawu da ƙyar ta saka wayar a kan kunnenta.
Duk yanda Jawaad ya shaida mata haka tayi, su dai su Hafiz suna tsaye suna kallonsu duk da sun kasa gane kan abokin nasu ma, tunda bai musu bayanin komaiba.
Bayan ta kammala wayar Jawaad ya maida bindigarsa a aljihu yana kallon su Hafeez.
“Zan barta tare daku, nanda mintuna ashirin zan iya kiranku, zakuzo bayan kamfanin kuma ku sameni”.
A tare suka jinjina masa kawuna, ya fice da hanzarinsa.............✍🏻
*_Kutayani da addu'a nabar wannan ragwantakar typing ɗin🤦🏻♀, ni kaina sainaji kamar baniba🙁, sai bayan kwana bibbiyu fa nake iya tafo shafi ɗaya😞🙆🏻ɗaya, koda yake kuma naga maba buƙata kukeba, dan Comments ma wahalaryi yake muku, shi kuma comments yana karama marubuci ƙwarin gwiwa ne, masuyi ina godiya sosai😘😍, kuma masu karantawa ku wuce ngd😆, mu tafi abinmu kawai a haka, randa na samu dama na ringa tafo muku⛹♀🤸🏻♀🤸🏻♀_.*
*_ZAFAFA SABON KAFCE SUN DAWO GAREKU_*
_KADA KU MANTA MARUBUTAN DAI SUNE WANDA SU KA RUBUTO MUKU ZAFAFAN LITTATTAFAN NA BAYA, A YANZU MA SUN SAKE YUNKUROWA DA WASU SABBIN MASU SABON SALO_
_*KAUNARMU:* 💋❤️NA MAMUH GEE_
_*DAURIN GORO:* 💋❤️NA HAFSAT RANO_
_*ALKAWARIN ALLAH::* 💋❤️SAFIYYA HUGUMA_
_*GUDU DA WAIWAYE:* 💋❤️NA BILLYN ABDUL_
_*IGIYAR ZATO:* ❤️💋NA MISS XOXO_
_CANCADI DOMIN DUKKANIN LITTAFAN NAN ZAKA/KI IYA MALLAKAR SU A NAIRA DARI BIYAR_
_GUDA DAYA DARI BIYU_
_GUDA BIYU DARI UKU_
_GUDA UKU DARI HUDU_
_GUDA HUDU DARI HUDU DA HAMSIN_
_DOMIN MALLAKAR SU SAI A TUNTUBE MU TA HANYAR_
*_ZAKU BIYA KUDI TA BANKI TA WANNAN ACCOUNT DIN👇👇_*
2260792279
_MARYAM SANI_
_ZENITHBANK_
saiku tura shaidar biyanku ta maana screenshot ta wannan layin👇👇
*07067124863*
*_GA MASU TURA KATIN MTN SAISU TURA KATINSU ZUWA GA WANNAN NUMBER TAREDA TURA MATA SHAIDA_*👇👇
*09032345899*
_Sayen nagari, maida kuɗi gida masoyan asali😉😻🥰🥰😍😍😘😘👌🏻💃🏻💃🏻_
Mucigaba da shakatawa da wannan dan yanzune aka fara kafta WASAN😁👉🏻📻
_Sannan akwai tashoshinmu na Youtobe da zasu fara kawo muku daɗaɗan labarai bisa tsaftataccen karatu, kuyu azamar garzayawa tashar *ALƘALAMI TV & MANHA HAUSA NOVELS* domin samun wannan gara ɓasa, a danna mana subscribing domin nuna ƙauna ta musamman masoyan gaskiya.😃🥰🥰💃🏻👌🏻_.
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*😭🙏🏻*_Typing📲_*
*_🧺ƘWAI_* _cikin_ *_ƘAYA!!🧺_*
*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*
*_Wattpad:-_* _BilynAbdull😉_
*______________________________________*
*_BOOK ONE_*
_Shafi na ashin da ɗaya_
*______________________________________*
Sam bayason jin zafinta da yake ya cigaba da girmama cikin ransa, dan haka ya tashi yay shirin fita dukda kuwa lokacin ƙarfe tara da rabi na dare, kuma dawowarsa gidan kenan ko hutawa baiyiba.
Da kansa yaja motar dan yabama gimba damar zuwa ya kwanta ya huta.
Kansa tsaye gidan dattijuwarnan ya nufa, yanabin address ɗin da su Hafez suka bashi dalla-dalla.
A ƙofar madaidaicin gida ya tsaida motar dajin tabbacin nanne, dankuwa duk abinda aka kwatanta masa a jikin gidan ya gansa, kashe motar yay sannan ya fito cikin nuna alamun tsantsar gajiyar dake tattare dashi.
Ya kulle motar amma sai bai fitoba ya fara ƙoƙarin yin kira cikin ƙaramar wayarsa.
Bugu uku aka ɗaga, “Gani a ƙofar gida” ya faɗa idonsa akan murfin gidan.
Bansan amsar da aka bashiba daga can naga dai ya kashe wayar yana fitowa a motar, bindigarsa ya ɗauka ya tura a aljiyu sannan ya rufe murfin motar yana mai kulleta gaba ɗaya.
Dai-dai nan dattijuwa mai aiki gidan Alhaji kokino ta fito sanye da lulluɓi.
Da hannu tai masa nuni alamar su shiga, babu musu ya bita, bayan yaɗan wawwaiga bayansa yaga babu alamar kowa a wajen, dukda ma anguwar babu wani isashen haske saboda rashin wutar lantarki.
Gidan bawani babba bane ammafa yasha gyara, dan fes yake sannan kuma da gani babu ƙananun yaran da zasu ɓata.
Zama yay a farar kujerar roba dake ajiye a bangon yamma da yake ƙyautata zaton kicinne, itama ta zauna a ƙofar kicin ɗin bayan ta kawo masa tea tamkar tasan yana buƙatarsa a halin yanzu.
Godiya yay mata kuwa ya ɗauka yana sha.
“Bani da tabbas amma inaji a jikina kasan inda Alhaji yake”.
Jawaad dake ƙoƙarin kai kofin shayi bakinsa ya dakata yana kallonta, leɓensa na ƙasa ya tura cikin bakinsa yana tsotsa tare da kafeta da wani kallon nazari na seconds biyar, sai kuma yay murmushi yana ƙara damƙe kofin shayin da hannu biyu yakai bakinsa ya kurɓa.
Itama kallonsa takeyi har yanzu, sai dai bata sake cewa komaiba.
Jawaad ya cigaba da shan shayinsa kawai idonsa na kallon yanda iska ke kaɗa labulen ɗakin matar.
Yasha kusan rabin kofin shayin sannan ya ajiye yana sauke ajiyar zuciya, idonsa akanta.
“Mama shekararki nawa kina mata aiki?”.
Murmushi dattijuwa tayi tana kallonsa, “Yarona ai mai son kama fara sammako yakeyi”
“Hakane” Jawaad ya faɗa yana shafa kansa cikin murmushi.
“Miyasa take ɓoyemin kanta har yanzu?”.
“Bani da wannan amsar a zahiri da baɗini”.
Kansa ya rausayar kawai, idanunsa na sake rikiɗewa zuwa ja sosai, sai haɗiyar numfashi yake da zafi, hakan yasaka zuciyarsa gudu tare da tsitstsinkewa.......
Mama ta katse masa tunani da faɗin, “Ta bani saƙo na baka”.
Ɗago kansa yay ya kalleta, amma baice komaiba.
“Tace ka sadaukar, a cikin hakan akwai alamar tambaya? Idan kabi diddigi zaka fahimta”.
“Zanyi biyayya, sai dai zan cutu kuma”.
“Shiyyasa nazo maka da maganin hakan”.
Miƙewa Jawaad yay yana kallon agogon hannunsa, “Ina saurarenki, dan lokacina ƙararrene”.
“Karka damu nima komai inayinsa da ƙa'ida. iya ruwa fidda kai, amaryar alhajice mafitarka”.
Jawaad ya juyo yana kallon dattijuwa hannuwansa duka a cikin wandon jeans ɗinsa, “Mimene nata burin?”.
“Kisa da mallakar abinda ya tara”.
Kansa ya jinjina yana murmushi, ahankali ya furta “Abin birgewa”.
Kallonsa mama tayi tana murmushi itama.
Takowa yay ya dawo gabanta yana ɗan jingina da bango, yace, “Shine kikaji a ranar da kika faɗi kenan?”.
Cikin sauke numfashi mama tace, “Kusan haka yarona, sai dai tsoron ya gauraya ne da cin amanar aure, kuma da makusancinsa”.
Hannu ɗaya Jawaad ya ciro a aljihu yana mai shafa fuskarsa, “Idan babu kuskure a hasashena auren manufa tayi da haɗinkan ƙaninsa kenan?”.
“Hasashenka yana kan dai-dai, kamar yanda sukuma ka ruguza musu nasu a ranar da Alhaji zai dawo daga tafiya shi da ita”.
“Zan samu dukkannin bayanan?”.
“Ƙwarai kuwa, harma da wanda baka tambaya ba” tai maganar tana kunce ƙullin haɓar zaninta ta ciro wani ɗan abu ta miƙa masa.
Amsa yay yana sauke numfashi, “Nagode ƙwarai da gaske mama. A sanar mata ina buƙata matuƙa, sannan ke kuma yaushe aikinki zai ƙare a gidan?”.
“Eh to, inada zaɓi biyu ne, sannan dama ɗaya kacal, a koda yaushe za'a iya nemana a rasa”.
“Shikenan, ni zan wuce, a daren yau zan ƙulle bakin zaren”.
“Kariyar ALLAH ta tabbata a gareka tareda rahamarsa akowane lokaci”.
“Amin ya rabbi mama, nagode sosai, da safe Yazeed zai dawo gida”.
Murmushi kawai tai masa, shikuma ya fara taku cike da kasala ya fice daga gidan.
Buɗe motarsa yay ya shiga sannan ya rufe kansa, ya buɗe hannunsa dake rumtse da abinda mama ta bashi, idanu ya tsira masa yana kallo, kusan mintuna uku sannan ya ajiye yana tada motar ya fice daga anguwar.
Tuƙi yake amma hankalinsa kashi sittin baya a wajen, gefen titi ya samu jikin wani ƙyamiz yay fakin motar, ya cire babbar wayarsa a caji ya danna kiran Jabeer, bugu ɗaya ya ɗauka, sai dai yanda yaji muryarsa ya bashi tabbacin ya fara barci ne.
“Barci kake?”.
Jawaad ya faɗa a ƙasan maƙoshi.
Daga can Jabeer yace, “Wlhy kuwa barcine ya figeni a falo ma, yaya kana office ne?”.
“Eh to badai a cikiba, amma ina akan aikine, inasu Aliyu?”.
“Duk gasu muna a tare”.
“Yauwa ku kasance cikin shiri yanzu nima zan iso”.
Bai jira amsar Jabeer ba ya yanke wayar.
Rose ya kira, itama bugu ɗaya ta ɗauka, ko gaisuwarta bai sauraraba ya fara faɗin, “Yanzun nan ki kira number dana baki ranar, ki kirata da wayar dana baki ki sanar mata tazo bayan kamfanin robobi na kwanar gulbi ta sameki, wannan wayar ta ƙawartace wadda da ita suke haɗa komai, dan haka zatazo da sauri”.
“To amma boss kana ganin zatazo a darennan?”.
Tsawa ya daka mata wadda ta sakata firgita har tana neman yadda wayar, ta daiyi nasarar damƙeta da sauri tana faɗin, “Sorry Boss”.
Tsaki mai ƙarfi Jawaad yaja yana katse kiran, dama zuciyarsa a saman maƙoshi take sosai.
Motar ya tayar yaja da uban gudu zuwa gidansa dasu Aliyu ke ciki, shigowarsa falon yasasu miƙewa su duka cikin girmamawa, hannu ya ɗaga musu kawai ya wuce ɗakin da ke cikin falon, mintuna kamar uku sai gashi ya fito da mace da shekarunta ba zasu gaza talatin da biyu ba.
Dukansu sunsan da zamanta, dan haka basu wani damuba, Jawaad ya ciro waya a aljihunsa yay danne-danne yana miƙa mata, karɓa tayi tana kallonsa a yanayin tsoro-tsoro bariki-bariki....
“Ki kira number nan, ki sanar masa kina tare da Alhaji Kokino, yanzunnan tazo bayan kamfanin robobi na kwanar gulbi ta sameki, kuma yanzunnan”.
Bakinta ta taɓe tana kallon Jawaad ɗin, “Yallaɓai to miyasa zanyi hakan? Bayan kasani na sani Alhaji baya tare dani?”.
Bindiga ya ɗora mata a saman kai ba tare daya ce komaiba.
Take jikinta ya fara mazari, ta shiga ƙoƙarin yin abinda yace.
Yace, “Ki tabbatar muryarki ta fita normal babu gargada a cikinta”.
Zufar data fara jiƙa goshinta ta goge tana haɗiye yawu da ƙyar ta saka wayar a kan kunnenta.
Duk yanda Jawaad ya shaida mata haka tayi, su dai su Hafiz suna tsaye suna kallonsu duk da sun kasa gane kan abokin nasu ma, tunda bai musu bayanin komaiba.
Bayan ta kammala wayar Jawaad ya maida bindigarsa a aljihu yana kallon su Hafeez.
“Zan barta tare daku, nanda mintuna ashirin zan iya kiranku, zakuzo bayan kamfanin kuma ku sameni”.
A tare suka jinjina masa kawuna, ya fice da hanzarinsa.............✍🏻
*_Kutayani da addu'a nabar wannan ragwantakar typing ɗin🤦🏻♀, ni kaina sainaji kamar baniba🙁, sai bayan kwana bibbiyu fa nake iya tafo shafi ɗaya😞🙆🏻ɗaya, koda yake kuma naga maba buƙata kukeba, dan Comments ma wahalaryi yake muku, shi kuma comments yana karama marubuci ƙwarin gwiwa ne, masuyi ina godiya sosai😘😍, kuma masu karantawa ku wuce ngd😆, mu tafi abinmu kawai a haka, randa na samu dama na ringa tafo muku⛹♀🤸🏻♀🤸🏻♀_.*
*_ZAFAFA SABON KAFCE SUN DAWO GAREKU_*
_KADA KU MANTA MARUBUTAN DAI SUNE WANDA SU KA RUBUTO MUKU ZAFAFAN LITTATTAFAN NA BAYA, A YANZU MA SUN SAKE YUNKUROWA DA WASU SABBIN MASU SABON SALO_
_*KAUNARMU:* 💋❤️NA MAMUH GEE_
_*DAURIN GORO:* 💋❤️NA HAFSAT RANO_
_*ALKAWARIN ALLAH::* 💋❤️SAFIYYA HUGUMA_
_*GUDU DA WAIWAYE:* 💋❤️NA BILLYN ABDUL_
_*IGIYAR ZATO:* ❤️💋NA MISS XOXO_
_CANCADI DOMIN DUKKANIN LITTAFAN NAN ZAKA/KI IYA MALLAKAR SU A NAIRA DARI BIYAR_
_GUDA DAYA DARI BIYU_
_GUDA BIYU DARI UKU_
_GUDA UKU DARI HUDU_
_GUDA HUDU DARI HUDU DA HAMSIN_
_DOMIN MALLAKAR SU SAI A TUNTUBE MU TA HANYAR_
*_ZAKU BIYA KUDI TA BANKI TA WANNAN ACCOUNT DIN👇👇_*
2260792279
_MARYAM SANI_
_ZENITHBANK_
saiku tura shaidar biyanku ta maana screenshot ta wannan layin👇👇
*07067124863*
*_GA MASU TURA KATIN MTN SAISU TURA KATINSU ZUWA GA WANNAN NUMBER TAREDA TURA MATA SHAIDA_*👇👇
*09032345899*
_Sayen nagari, maida kuɗi gida masoyan asali😉😻🥰🥰😍😍😘😘👌🏻💃🏻💃🏻_
Mucigaba da shakatawa da wannan dan yanzune aka fara kafta WASAN😁👉🏻📻
_Sannan akwai tashoshinmu na Youtobe da zasu fara kawo muku daɗaɗan labarai bisa tsaftataccen karatu, kuyu azamar garzayawa tashar *ALƘALAMI TV & MANHA HAUSA NOVELS* domin samun wannan gara ɓasa, a danna mana subscribing domin nuna ƙauna ta musamman masoyan gaskiya.😃🥰🥰💃🏻👌🏻_.
*_ALLAH ka gafartama iyayenmu_*😭🙏🏻*_Typing📲_*
*_🧺ƘWAI_* _cikin_ *_ƘAYA!!🧺_*
*_Bilyn Abdull ce🤙🏻_*
*_Wattpad:-_* _BilynAbdull😉_
*______________________________________*
*_BOOK ONE_*
_Shafi na ashin da ɗaya_
*______________________________________*