Sashe 7
Kurman Baki Book 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ci gaba tayi da gunaguni,Kusan wannan dabi'arta ce,ta qware wajen mita da gunagunin mai da magana a ciki. Nata ta zuba daban,sai ruqayya ta saka hannu tayi bismillah ta dauki plate din ta soma zubawa tana fatar ta iya kai abincin cikin cikinta. Allah ya sani har cikin zuciyarta tana jin qyamar Zainab,saboda ita din macace da qazantarta bata boyuwa ko kadan. Mafi yawa duk farar mace qazantarta tafi saurin bayyana saboda hasken guraben boye datti da take dashi. Misali yatsu da faratanta zuwa duga dugi,zaka samesu a dafe ne ko yaushe,saboda bata damu data sanyawa qafarta lalle ba koda qanqani,hasalima duk sanda me lallen ruqayya tazo yi musu kallon sakarkaru takeyi su dukka,takan tabe baki tana juya kai da kafada,har cikin zuciyarta tana jin cewa ita dince mace cikakkiya. Kamar wata rana da tayi subutar baki bayan saleem ya gaza daure kyan lallen cikin dogayen yatsun ruqayya masu tsaho duk kuwa da cewa fatarta me dan duhu ce,amma sunyi ma yatsun nata kyau sosai,ya yaba irin yabawar da har zuciyarta taji dadin hakan,sai taji ko nawa ta kashe wajen yin lallen bata fadi ba "Uhmmm,bonono,ana gyaran badini malam wa yake ta zahiri?,an bar qofar gari babu tsaro amma an tafi ana gyaran cikin birni" a nutse ta daga kai ta kalli Zainab. Sau tari tana yawan sake mata magana,saidai ita har zuciyarta tana jin cewa bata da lokacinta,muddin ta biye mata kenan hakan yana nufin ita da ita basu da banbanci kenan. Ba kasafai ta fiya sakin jiki ko hira da saleem ba duk ranar girkin Zainab din. Don a gurin Zainab hakan ma duka laifi ne. Banda tsaiwar ruqayya da baiwa banza ajiyar zainab din,hatta da kwalliyarta bataso saleem ya gani,bayan ita din koda kwalli da zai nuna anihin zatin kyan mace bai dameta ba. Wani irin zaman cin abinci suke mara armashi duk randa ya zamana ita ke da girki,ruqayya na tafiya bisa tsarin hakanne bawai don tana tsoron zainab ba,a'ah......tun asali ita din macace marason hayaniya da kuma tashin hankali,tana da wata irin nutsuwa da hankali wanda ke sake fusgar saleem a tare da ita. Hatta da shi din da ya zama miji a gareta shekaru kusan shida kenan,kusan komai nata da wani irin aji takeyinsa da zai nuna maka meye ainihin ma'anar sanin ciwon kai. K'ididdigaggun lomomi yayi yaji abincin yakai masa ko ina. Yasan dama za'a rina,a lokuttan irin wannan yafi ta'ammali da fruit masu yawa da kuma damammiyar fura. Ko a yanzun ma aje cokalin yayi "Ina nonon da na aiko isma'il ya kawo?" ya fada yana zuba ruwa a cup "Ba'a dama ba" bai damu ba don ya saba da hakan "Dauko ki damamin inaso nasha" sai data cika bakinta da lomar abincin,kamar batasan meye dandanon dadi bisa harshenta ba sannan tace "Kamar fa yara sun shanyeta dazun,sun iso daga makaranta suna jin yunwa aiki yasha kaina,ban ankara ba" ruwan ya dakata da sha yana dubanta. Ba sau daya ba sau biyu ba yasha yaja mata kunne kan irin wannan dabi'ar tata "Sau nawa zan gaya miki ne zainab?,duk sanda yara sukayi amfani da abinda bace a ajjiyemin ki dinga daukan waya kina gayamin kafin na dawo gida na buqaci amfani dashi don na taho da wani?" Kai ta langabe tanason gwada kissar da taga sauran mata nayi,duk da can qasan zuciyarta fal take da haushi,komai fa ruqayya tana gani,kuma uwa uba a yadda take mace me jajircewa da gyaran kanta dukkan ire iren wadannan tirjiyar bai kamata ta dinga fuskantarsu daga saleem din ba "To gashi na musanya maka da zobo ko?,kayi haquri ka sha" ta fada tana miqa masa bayan ta zuba. Duk da ransa ya riga ya baci,amma ya sani abune mai bata rai qwarai mace tayi abu don saboda kai ka wofantar kaqi amfani da shi,don haka ya danne zuciyarsa ya amsa din. Sanda ya fara shi ji tayi kaman anyi mata bushara da aljanna,farincikinta ya gaza boyuwa har saman fuskarta "Lallai da alama yau bazanyi asarar kudina ba" ta fada cikin zuciyarta tana jin wani dadi yana ratsata. Duk yadda tazo taci abicin ya gaza wuce mata saboda zallar rashin ma'anarsa,dole ta ajjiye ta dauki wayarta dake ajjiye gefe tana fadin "Nidai zan wuce,sai da safenku" cup din ya dire ya miqe kaman yadda ya saba "Muje na taka muku" maganar ta fusgi zainab, fargabar kada yaje ya jima wani abu ya faru ya sanyata miqewa "Nikam dama kin tafi dasu haneefa wallahi" tayi maganar cikin son cusa wasi wasi a zuciyar ruqayyan "Ba school ne gobe?,nakega bacci ya kamata su kwanta ko?" Saleem din ya fada yana duba agogon wayarsa. Ido ta kanne masa guda daya,ta matsa dab dashi sosai suna gogar juna "Na maka tanadi ne dear,inason space" dan dauke kansa yayi gefe kadan ya kuma yi taku biyu baya kadan ya rabeta yana yin gaba idanunsa akan ruqayya wadda har tayi gaba abinta. Yana mamakin yadda gaba daya baki da jikinta baya cikin damuwar da zata zanya damuwarta a kanta,baisan dsga safe har zuwa dare me takeyi da zata gagara tsaiwa gyara jiki da bakinta ba "Suyi kwanansu a nan din" ya gadi yana qarasa ficewa. Qwafa taja tana dauke kanta daga bakin qofar,bata karanci komai a fuskar ruqayya ba dangane da maganar ds tayi,taso qwarai taga adadin tasirin da maganar tayi mata,taso ta kwana da abun ya hanata bacci, gobe da safe kuma taga sauyin da zai qarasa gigitata. Zaune yake daga gefan gadonsa,calculator da wasu qananun takardu ne a hannunsa yana lissafin kasuwa. Sallama zainab tayi cikin doki tana shigowa dakin bayan ta kora su haneefa dakinsu. Kai ya daga ya kalleta yana amsa sallamar,bai qara koda second biyu ba ya ajjiye kan nashi yaci gaba da aikinsa. Gaba gadi taci gaba da takowa cikin dakin da daurin qirjin da ta sakeyi bayan ta cire rigar data maqala a dazun. Har ta gama abinda zatayi ta wuce gadon ta sheme bai motsa ba yana qarasa lissafinsa. "Daddyn haneefa.....kai nake jira fa,ka ajjiye aikin ka tashi ka cire kayanka mu kwanta" ta fada tana daga kwancen. Kansa ya daga haushi da takaici yana taso masa,kamar wanda zasuyi aikin gini ko na kauda itace,tana magana gatsau ba wani salo me jan hankalin miji a ciki?. Idanunsa yakai kan qafafunta dake saman cotton bedsheet din nasa,wanda asali ruqayya ce ta siyesu har guda shida tace ga guda daya kyauta ta bashi,saidai kuma a duk sanda yake kwananta ne ire irensu take canza masa a bedroom dinsa dake sashenta. Ba komai a qafartata face baqi da datti kwance qasan tafin qafartata,ga kaushi da qananun faso da suka tsatsagata suka bawa datti muhallin zama me kyau. Daga saman singalalin qafarta kuwa shima kaushinne da fata kanyi sanadin busawar sanyi sanyi da kuma rashin bata muhimmanci wajen shafa mata mai akai akai. Da ya maida dubansa ga zanin jikinta kuwa,farin siririn layin dake qasan bakin kowacce atamfa dake dauke da sunan atamfar ya sirka laifinsa. Alamu dake nuna dattin atamfa da kuma neman agajin wanki da takeyi. Hannunta na ajjiye daga qugunta,fararen faratanta da babu digon Jan lalle ko baqi ko misqala zarratin na shimfide a jikinta. Sake gyara kwanciyarta tayi tana jin farinciki cikin ranta,kallon da yake mata sai zuciyarta ta fara qissimamata lallai maganin ke aiki a jikinsa. Eh zai iya cewa tunda ya zauna a gurin yakejin sauyin a jikinsa,saidai kuma a yanzun da yake kallonta ya rasa wani abu guda da zaiyi masa tasirin da zai shauqantu zuwa gareta. Tana murmushin haqoranta da suka komawa ruwan madara qarfi fa yaji suka bayyana,ta miqa hannunta tana sosai gashinta dake a cunkushe wanda yaci arziqi saboda zuwanta ta shafeshi da man gelo fes,abinda yasa yake fesar da wani qamshi mara dadi kenan "Yanzu kin gama shirin bacci kenan?" Idanunta ta fiddo waje "Eh mana,kai nake jira" ta fada tana murmushi dadi yana ratsata. Kansa ya mayar ga aikinsa yana jin buqata tana tasiri a jikinsa "Ki shiga toilet dina kiyi wanka ki fidda zanin nan,ki bude wardrobe dina akwai wata rigar bacci black and white,ki dauki black din. "Wanka kuma yanzu?,bayan tuni nayi wanka na?, gaskiya dare yayi" ta fada tana jin wata muguwar ganda da qyuya tana ratsata. Ita batasan me yake damun saleem ba,ya fiya zafafawa da yawa,shegen sanabe da tsafta kamar d'an kwad'i "Umarni nake baki" ya fadi bayan ya dago idonsa ya zube a kanta. Batason tayi asarar kudinta shine babban dalilin da ya sanyata ta jawo jikinta ta sauko ba don taso ba. Ya bita da kallo yana girgiza kai. Wanka ma na shiga dakin miji sai ance da mace tayi,wacce irin rayuwa ce a wannan. A sassan ruqayya shi ake sanyawa yayi wankana,amma a nan sashen abun yasha banban. Ko minti hudu batayi ba sai gata ta fito daure da maqalallen zanin da ya rasa na meye,ta qarasa wardrobe din ta ciro rigunan kamar yadda yace,ta farke baqar tana dagata sannan ta dubeshi "Daddyn haneefa,rigace wannan ko matacin koko?" "Shafa kiji" kawai yace mata saboda takaici,abinda yakeji cikin jikinsa zuwa yanzu ya fara haukata,sai ya fara tattare kayan aikin nasa yana zubawa a bedside drawer dinsa. "Nifa wadan nan rigunan banga wani amfaninsu ba,banda asarar kudi,abu kamar sange(ragar net),da kudin aka baka ka qaro maganin harka da baifi ba wannan me zata tsinana maka,bakaci a bakinka ba ba baka matsa a qasanka ba sai kuma ace tana da amfani" ta fada cikin qunaquni. Qunaqunin da tsaf ya jita amma yayi banza da ita. Sai data gama qananun mitocinta sannan ta saka rigar. Rigar tayi sama abinta,saboda bata bada hankalinta wajen daidaitata a jikinta ba,gurin breast curves din yayi sama breast din kuma yana a qasanshi. Gwanace gurin shan magungunan mata,amma sai bata taba lura da cewa breast na daya daga cikin abinda ke tafiya da hankalin saleem din ba,itadai can qasan shine muhallin harinta ko da yaushe. Duk wani lungu da saqo dake isar da saqo a jikin mace yayi qoqarin ya aika saqo can,saidai da ya cusa kai ko harshensa wani qaqqarfan abu ke ingizoshi waje. Yayi wani irin rudewa da gigicewar da shi kansa ya dinga tuhumar kansa abinda ke faruwa,saboda a yadda yasan jikinsa yanayin da yake cikin ya wuce dabi'arsa. Duk sanda aka koroshin sai zuciyarsa ta tunasar dashi BA RUQAYYA BACE. dole daga qarshe ya