Sashe 5
Jininmu Daya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Abdulmalik ne ya Shiga dakin Hajiya Jamila cikin saurinsa dako sallama baiba duk ya rude jin rashin lafiyar Rufaida yar uwa a garesa, inda Aunty shema'u da Aunty Maimuna sakonta data ya aje mata ganinsa cikin saurin bako sallama yasa ta tanbayar ko lafiya zai shigo mata daki haka yace "Kiya hakuri Umma Rufaida ce yanzu Abba yake fadamin batajin da'di zamu tafi asibiti"Hajiya Jamila da ranta ya gama baci tace tunda gani uwarka banda lafiya aika rude kakasa yimin sallama wallahi Abdulmalik kashiga hankalinka babban kwabo kawai ko Abdussalam da AbdulJabbar bazasuyi haka ba" AbdulMalik yace "kiya hakuri Umma"Aunty Shema'u da sai yanzu tasa baki tace" toma banda iskanci da raini akanta aka fara cuta"Aunty Maimuna da tasa baki itama tace" Haba dan Allah tunda ya amsa laifinsa ai saiku hakura ku kyalesa"kafin Aunty Maimuna ta fada tana karasa zancen da cewa muje Abdulmalik na dubo jikinta dan balallai kuje asibiti kudawo kusamemu bamu tafi ba"Aunty Shema'u tace"lallai Maimuna wannan dakece babbarmu bamusan ikon da zaki nuna akanmu ba"Maimuna da bata saurari yayartata ba dan tasan rai zai iya baci idan takulata dan ita bata goyan bayan rashin gaskiya suka fice itada AbdulMalik Hajiya Jamila ta kalli Shema'un tace" gaskiya Yaya ,Maimuna bansan ina tasamo wannan halinba bare ace yafi 'dan uwa dama da masu asali ake abin tashiga toda da sauki"Aunty Sha'awa tace "ni bama wannan yafi damuna ba kidubafa kiga yadda Abdulmalik ke rudewa akanta karfa yace shima yarinyar nan yakeso wallahi tun wuri kiyi maganinta kar wannan bakar kayar tasake kutso kai zuriyarki tazo ta sake miki shigar sauri"Hajiya Jamila da sai yanzu hankalinta yakai nan tace hakane Yaya amma daraina bazan amince ba in anyi nafarko anyimin fin karfi wannan bazan bari ba kodan duba da banbancin dake tsakaninmu mai dunbin yawa" da wannan firar tasu ta cigaba da wanzuwa har Rukayya ta shigo dakin da za'a barta anan
Aunty Maimuna data kalli Rufaida da take rawar Sanyi tace subhanallah Rufaida zazzabin ne har haka kafin ta bude Sib din jikin bango ta samo mata hijabi tana cewa"anshi maza kisa AbdulMalik yana falo yana jiranki"tare suka fito falon da Rufaida ba wanda take ma iya yiwa magana AbdulMalik cikin nuna tausayi ga matar yayannasu da kasa ta rufesa da take masa takaba yace"Aunty kinga ashe har haka jikin Rufaida yayi zafi"Aunty Maimuna tace"AbdulMalik rasa miji ba abine mai sauki ba dole akwai ciwo da zafi na rabuwa da abokin rayuwarka yanzu dai kayi maza ku tafi asibiti Allah ya bata lafiya idan kun taddamu shikenan"AbdulMalik ya amsa da to Aunty Allah ya saukeku lafiya"duk tare suka fito shida Rufaida sukayi hanyar harabar gidan ya tada mota suka nufi asibitin
Da murmushi matashin likitan mai suna Zahraddin ya dago kai daga rubutun da yake zaune a daya daga cikin kujerun office din yana cewa"Malam AbdulMalik lafiya kuwa Zahraddin ya fada yana bawa AbdulMalik hannu da likitan bayan sunyi musabihar ne ,suka zauna a kujerun dake gefen na Zahraddin din kafin AbdulMalik yace"Eh Wallahi zahraddeen nine Matar Yayana da yarasu kwana 4 nakawo bata jin dadi ya nuna masa Rufaida "Zahraddin yace" Allah sarki Mama ta fadamin rasuwar to Jiya nadawo daga Kano shine banzo gaisuwa ba banma ko a waya ba tunda naje ban huta ba wani aiki ne aka turamu Allah ya jikansa ita kuma Allah ya bata lafiya ya fada yana kallen fuskar Rufaida da yaji lokaci guda tausayinta ya kama shi "AbdulMalik yace "Amin abokina babu komai nagode amma ban yarda ba saikazo yimin har gida" Zahraddeen yace" to shikenan zanzo yau din nan ma in Allah ya amince amma waima tsaya kasan da abotar kaki shigowa koka kirani a waya nazo har gida koka fadamin kuna nan a waje nasa a shigo daku yanzu da yadda nace nagama duba kowa da saina fito naganku naji kunya"AbdulMalik yayi murmushi yace"abokina kenan yanzu muka zo badadewa mutane kadan na tarar idan kuma na shigo kaga zan shiga hakkinsu ,idan nayi haka kuma kaga bankyautaba bansan uzurin kowa ba ,kuma bawai alfarmace ko matsayi ace dan kasan wani a guri kai tsaye bawani dalili kazo ka wuce wasu guri kuma bayan sun rigaka zuwa kaga akwai hakkinsu akanmu da munyi hakan"murmushi Zahraddin yayi yace"Uztaz AbdulMalik kenan"AbdulMalik yayi murmushi yace"gaskiya ce ba wani uztaz ni duba min mara lafiyata mu tafi na biyema hirarmu bazata kare ba bare muyi abinda zai anfanemu"Murmushi Zahraddin kawai yayi ya juya ga Rufaida ya mata tanbayoyi ya gwada Blood pressure dinta ya rubuta mata magunguna yace ta rage damuwa sannan ya mata nasihohi kafin su mike su fito Zahraddin yana cewa sai ya karaso zuwa anjima koda yamma ne
Daki kawai Rufaida ta shiga bayan fitowarta mota da ledojin magungunan da yoghurt da AbdulMalik ya siya mata da zata sha maganin dashi da tuni lokacin su Aunty Maimuna sun dau hanyar Nasarawa tana shan magungunan gado kawai ta haye ta kwanta AbdulMalik ya da'de a motar kafin ya fito a ranshi yana matukar jin tausauyin Rufaida tunanin da zuciyarsa ta fara shiyashi sakin murmushi ya fito daga motar ya wuce bangaren mahaifinshi don alokacin ya tabbatar su Aunty Maimuna sun tafi don yaga message din data turamasa har ran AbdulMalik yakeso Auntynsu Maimuna saboda tafita daban a cikin yan uwan mahaifiyartashi gwarama Haulatu ba laifi da nata kirkin saidai zugata da yan uwanta keyi shine yake sauya ta dandanan gata da daukar zafi lokaci guda ita ko Aunty Maimuna tana da kafiya akan gaskiya.*JININMU 'DAYA*
By Sadiya Ibrahim Khali(Sadiya Khali)
5
AHajiya Jamila ta dan dubi Aunty Amina da Duke zaune Suna karyawa a falo tace Amarya Ruqayya zaki mikawa abincinta kibawa Rufaida ta mika mata"Abba Bukar da baice komai ba sai da yaji karashen maganar Hajiya Jamila yace "kamar ya a mikawa Ruqayya abincinta?ita bazata iya fitowa ta ciba"Hajiya Jamila ta 'dan yatsina kafin tace masa" kasan tunda akayi rasuwar nan yarinyarnan Ruqayya bata cikin nutsuwarta gani take data fito falon na ganin wancen yaron zatayi"Ganin ya gane AbdulAhad take nufi yace mata"dakata Jamila ita Ruqayya AbdulAhad din mijintane ita matartasa daya mutu ya bari take masa takaba ita ta fito take cin abincin da ita yaushe ta warware ince Jiya har asibiti aka kaita"ganin kowa na falon jin amsar zata bayar yake yasata cewa"Ba haka bane Abba kaima kasan akwai banbanci tsakaninta da Rufaida mai tazara saboda ita Rufaida ta auresa tana zaune dashi ita kuma Ruqayya yarasu tana son aurensa"shiru Abba Bukar yayi yana tunanin halayyar matarsa kiri-kiri take fito da komai yace" Wasila jeki kira min Ruqayyan danni tun fil azal iyalina guri 'daya sukecin abinci bakuma za'a ware ba saboda zuwanta ya fada"Wasila datake cin dankali ta ajiye ta mike tana cewa "to Abba "sai da yaga shigowar Rukayyan falo da take ta sissinke kai ya mike yabar dakin da Ruqayyan take gaisheshi ya bita da lafiya lau ya fice daga gidan yaran suna binsa da adawo lafiya Aunty Amina ta bisa yi masa Rakiya Aunty Amina ta dubesa tace"amma Abba abinda Ummansu Abdussalam take sainaga kamar bata kyautawa akan yarinyar nan kuma a gabanta take komu inzamuyi mata kamata yayi ta hanamu tunda koma menene matsayin surikarta take dukda mai rabawa ta raba" nisawa yayi yace "hakane Amina zanyiwa tufkar hanci da wuri kuma kema karki sa baki dukdai kulawar da kukaga yakamata a matsayinku na iyaye gareta Ku bata tunda koba komai Aliyu da Hauwa'u na wane" tace masa hakane Insha Allah zamu kara datse damtse fiye da yanzu"yana murmushin jin da'di yace yawwa Amina"Allah yayi miki Albarka" tace "Amin" da haka yaja motarsa ya fice ya nufi gurin aikinshi.
Rufaida da take zaune a gurin tanaji yadda Hajiya Jamila suke fira itada Ruqayya ko daya batasa baki ba dan ko tasama gwaleta zatayi jefi-jefi dai take sauraran firar tasu hirar ragowar yaran dakin take shiga da kusan ta karatu sukeyi hakan yasa ta sake tsunduma cikin tunanin rayuwarta yau babu ginshikan rayuwarta dukda suna raye,amma akwai tazara mai dunbin yawa a tare dasu, Yasir shida Ubaidullah suke wasa 'dan Aunty Amina dukda Ubaidun ya girmema Yasir da wajen shekara 'daya da wani abu,AbdulMalik ya dubi Rufaida yace"kinsha maganinki kuwa" tace "Eh Yaya nasha" yace mata yawwa kinsan Zahraddin yace ki riqa shan magani akan lokaci Allah ya kara sauki dazu da mukayi waya yace a gaisheki"tace"Amin Yaya AbdulMalik to ina amsawa" da haka suka cigaba da firarsu zuwa wani 'dan lokaci.
Jingina kansa da jikin kujerar dake office din yayi sanyin Ac na ratsasa yana tuna abun da haryau ya kasa mantawa dashi a rayuwarsa dukda shekarun da suka fara tafiya amma baya tunanin ya manta da wancen ran da yasa shi a sahun mai sa'a a rayuwarsa a hankali ya fara tunano wayarsu da Ahmad da yakasa fahimtar yanzu menene a cikin ransa dukda yadda ya da'de da yanke tsammani kuma har yau baya tsammanin cikar muradinsa ABDURRA'UF RJM kwararran likita MEDICAL DOCTOR kenan matashi mai kimanin shekaru talatin da 33zuwa 34
Mi'kewa yayi da wannan tunanin nasa ganin baida sauran marasa lafiyar da zai duba key din mota ya dauka kawai yana kokarin ficewa daga office 'din yana kallon agogon hannunsa 2:pm dai dai yayi mamakin kaiwarsa karfe 2 bai koma gida ba gurin wayarsa da take caji ya karasa yana kokarin cireta daga cajin yaga kiran Safiyya karasa cirewa yayi inda yayi caraf ya 'daga wayar yana murmushin mugunta dan yasan flashing Safiyyan tayi ako bangarenta cewa tayi cikin yarensu Na India tana cewa" kai Yaya Ra'uf daga flashing harka kama dama ammi ce tace na kiraka karma taho kamanta sakonta"ya dan saki fuska kamar tana kallonsa yace"ai ban ta'ba ganin 'kanwa tana gudun yayanta yaci ku'din wayarta ba sai akanki"jin yaji sakon yasa Safiyya katse wayar tana murmushi shiko Ra'uf da yake jiran amsar Safiyya jin shiru ne yasa shi duba wayar ganin ta katse yasa shi murmushi ya bude kofar office 'din ya fice yana tura kofar office din yasa key ya rufe " a harabar asibitin ya tsaya kiran waya bai jima yana wayarba ya katse ya karasa gun motarsa ya tayar yabar asibitin sa'ko Ammi ya tsaya ya amsa daba komai bane face turare daganan kai tsaye gida ya nufa
Aunty Maimuna data kalli Rufaida da take rawar Sanyi tace subhanallah Rufaida zazzabin ne har haka kafin ta bude Sib din jikin bango ta samo mata hijabi tana cewa"anshi maza kisa AbdulMalik yana falo yana jiranki"tare suka fito falon da Rufaida ba wanda take ma iya yiwa magana AbdulMalik cikin nuna tausayi ga matar yayannasu da kasa ta rufesa da take masa takaba yace"Aunty kinga ashe har haka jikin Rufaida yayi zafi"Aunty Maimuna tace"AbdulMalik rasa miji ba abine mai sauki ba dole akwai ciwo da zafi na rabuwa da abokin rayuwarka yanzu dai kayi maza ku tafi asibiti Allah ya bata lafiya idan kun taddamu shikenan"AbdulMalik ya amsa da to Aunty Allah ya saukeku lafiya"duk tare suka fito shida Rufaida sukayi hanyar harabar gidan ya tada mota suka nufi asibitin
Da murmushi matashin likitan mai suna Zahraddin ya dago kai daga rubutun da yake zaune a daya daga cikin kujerun office din yana cewa"Malam AbdulMalik lafiya kuwa Zahraddin ya fada yana bawa AbdulMalik hannu da likitan bayan sunyi musabihar ne ,suka zauna a kujerun dake gefen na Zahraddin din kafin AbdulMalik yace"Eh Wallahi zahraddeen nine Matar Yayana da yarasu kwana 4 nakawo bata jin dadi ya nuna masa Rufaida "Zahraddin yace" Allah sarki Mama ta fadamin rasuwar to Jiya nadawo daga Kano shine banzo gaisuwa ba banma ko a waya ba tunda naje ban huta ba wani aiki ne aka turamu Allah ya jikansa ita kuma Allah ya bata lafiya ya fada yana kallen fuskar Rufaida da yaji lokaci guda tausayinta ya kama shi "AbdulMalik yace "Amin abokina babu komai nagode amma ban yarda ba saikazo yimin har gida" Zahraddeen yace" to shikenan zanzo yau din nan ma in Allah ya amince amma waima tsaya kasan da abotar kaki shigowa koka kirani a waya nazo har gida koka fadamin kuna nan a waje nasa a shigo daku yanzu da yadda nace nagama duba kowa da saina fito naganku naji kunya"AbdulMalik yayi murmushi yace"abokina kenan yanzu muka zo badadewa mutane kadan na tarar idan kuma na shigo kaga zan shiga hakkinsu ,idan nayi haka kuma kaga bankyautaba bansan uzurin kowa ba ,kuma bawai alfarmace ko matsayi ace dan kasan wani a guri kai tsaye bawani dalili kazo ka wuce wasu guri kuma bayan sun rigaka zuwa kaga akwai hakkinsu akanmu da munyi hakan"murmushi Zahraddin yayi yace"Uztaz AbdulMalik kenan"AbdulMalik yayi murmushi yace"gaskiya ce ba wani uztaz ni duba min mara lafiyata mu tafi na biyema hirarmu bazata kare ba bare muyi abinda zai anfanemu"Murmushi Zahraddin kawai yayi ya juya ga Rufaida ya mata tanbayoyi ya gwada Blood pressure dinta ya rubuta mata magunguna yace ta rage damuwa sannan ya mata nasihohi kafin su mike su fito Zahraddin yana cewa sai ya karaso zuwa anjima koda yamma ne
Daki kawai Rufaida ta shiga bayan fitowarta mota da ledojin magungunan da yoghurt da AbdulMalik ya siya mata da zata sha maganin dashi da tuni lokacin su Aunty Maimuna sun dau hanyar Nasarawa tana shan magungunan gado kawai ta haye ta kwanta AbdulMalik ya da'de a motar kafin ya fito a ranshi yana matukar jin tausauyin Rufaida tunanin da zuciyarsa ta fara shiyashi sakin murmushi ya fito daga motar ya wuce bangaren mahaifinshi don alokacin ya tabbatar su Aunty Maimuna sun tafi don yaga message din data turamasa har ran AbdulMalik yakeso Auntynsu Maimuna saboda tafita daban a cikin yan uwan mahaifiyartashi gwarama Haulatu ba laifi da nata kirkin saidai zugata da yan uwanta keyi shine yake sauya ta dandanan gata da daukar zafi lokaci guda ita ko Aunty Maimuna tana da kafiya akan gaskiya.*JININMU 'DAYA*
By Sadiya Ibrahim Khali(Sadiya Khali)
5
AHajiya Jamila ta dan dubi Aunty Amina da Duke zaune Suna karyawa a falo tace Amarya Ruqayya zaki mikawa abincinta kibawa Rufaida ta mika mata"Abba Bukar da baice komai ba sai da yaji karashen maganar Hajiya Jamila yace "kamar ya a mikawa Ruqayya abincinta?ita bazata iya fitowa ta ciba"Hajiya Jamila ta 'dan yatsina kafin tace masa" kasan tunda akayi rasuwar nan yarinyarnan Ruqayya bata cikin nutsuwarta gani take data fito falon na ganin wancen yaron zatayi"Ganin ya gane AbdulAhad take nufi yace mata"dakata Jamila ita Ruqayya AbdulAhad din mijintane ita matartasa daya mutu ya bari take masa takaba ita ta fito take cin abincin da ita yaushe ta warware ince Jiya har asibiti aka kaita"ganin kowa na falon jin amsar zata bayar yake yasata cewa"Ba haka bane Abba kaima kasan akwai banbanci tsakaninta da Rufaida mai tazara saboda ita Rufaida ta auresa tana zaune dashi ita kuma Ruqayya yarasu tana son aurensa"shiru Abba Bukar yayi yana tunanin halayyar matarsa kiri-kiri take fito da komai yace" Wasila jeki kira min Ruqayyan danni tun fil azal iyalina guri 'daya sukecin abinci bakuma za'a ware ba saboda zuwanta ya fada"Wasila datake cin dankali ta ajiye ta mike tana cewa "to Abba "sai da yaga shigowar Rukayyan falo da take ta sissinke kai ya mike yabar dakin da Ruqayyan take gaisheshi ya bita da lafiya lau ya fice daga gidan yaran suna binsa da adawo lafiya Aunty Amina ta bisa yi masa Rakiya Aunty Amina ta dubesa tace"amma Abba abinda Ummansu Abdussalam take sainaga kamar bata kyautawa akan yarinyar nan kuma a gabanta take komu inzamuyi mata kamata yayi ta hanamu tunda koma menene matsayin surikarta take dukda mai rabawa ta raba" nisawa yayi yace "hakane Amina zanyiwa tufkar hanci da wuri kuma kema karki sa baki dukdai kulawar da kukaga yakamata a matsayinku na iyaye gareta Ku bata tunda koba komai Aliyu da Hauwa'u na wane" tace masa hakane Insha Allah zamu kara datse damtse fiye da yanzu"yana murmushin jin da'di yace yawwa Amina"Allah yayi miki Albarka" tace "Amin" da haka yaja motarsa ya fice ya nufi gurin aikinshi.
Rufaida da take zaune a gurin tanaji yadda Hajiya Jamila suke fira itada Ruqayya ko daya batasa baki ba dan ko tasama gwaleta zatayi jefi-jefi dai take sauraran firar tasu hirar ragowar yaran dakin take shiga da kusan ta karatu sukeyi hakan yasa ta sake tsunduma cikin tunanin rayuwarta yau babu ginshikan rayuwarta dukda suna raye,amma akwai tazara mai dunbin yawa a tare dasu, Yasir shida Ubaidullah suke wasa 'dan Aunty Amina dukda Ubaidun ya girmema Yasir da wajen shekara 'daya da wani abu,AbdulMalik ya dubi Rufaida yace"kinsha maganinki kuwa" tace "Eh Yaya nasha" yace mata yawwa kinsan Zahraddin yace ki riqa shan magani akan lokaci Allah ya kara sauki dazu da mukayi waya yace a gaisheki"tace"Amin Yaya AbdulMalik to ina amsawa" da haka suka cigaba da firarsu zuwa wani 'dan lokaci.
Jingina kansa da jikin kujerar dake office din yayi sanyin Ac na ratsasa yana tuna abun da haryau ya kasa mantawa dashi a rayuwarsa dukda shekarun da suka fara tafiya amma baya tunanin ya manta da wancen ran da yasa shi a sahun mai sa'a a rayuwarsa a hankali ya fara tunano wayarsu da Ahmad da yakasa fahimtar yanzu menene a cikin ransa dukda yadda ya da'de da yanke tsammani kuma har yau baya tsammanin cikar muradinsa ABDURRA'UF RJM kwararran likita MEDICAL DOCTOR kenan matashi mai kimanin shekaru talatin da 33zuwa 34
Mi'kewa yayi da wannan tunanin nasa ganin baida sauran marasa lafiyar da zai duba key din mota ya dauka kawai yana kokarin ficewa daga office 'din yana kallon agogon hannunsa 2:pm dai dai yayi mamakin kaiwarsa karfe 2 bai koma gida ba gurin wayarsa da take caji ya karasa yana kokarin cireta daga cajin yaga kiran Safiyya karasa cirewa yayi inda yayi caraf ya 'daga wayar yana murmushin mugunta dan yasan flashing Safiyyan tayi ako bangarenta cewa tayi cikin yarensu Na India tana cewa" kai Yaya Ra'uf daga flashing harka kama dama ammi ce tace na kiraka karma taho kamanta sakonta"ya dan saki fuska kamar tana kallonsa yace"ai ban ta'ba ganin 'kanwa tana gudun yayanta yaci ku'din wayarta ba sai akanki"jin yaji sakon yasa Safiyya katse wayar tana murmushi shiko Ra'uf da yake jiran amsar Safiyya jin shiru ne yasa shi duba wayar ganin ta katse yasa shi murmushi ya bude kofar office 'din ya fice yana tura kofar office din yasa key ya rufe " a harabar asibitin ya tsaya kiran waya bai jima yana wayarba ya katse ya karasa gun motarsa ya tayar yabar asibitin sa'ko Ammi ya tsaya ya amsa daba komai bane face turare daganan kai tsaye gida ya nufa