← Book details Jininmu Daya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 25 OF 57

Sashe 25

Jininmu Daya Part 1 Complete Hausa Novel · about 5 min read

5pm Suka shirya suka fito gidan Aunty Samina ita da Aunty Samira da Nasiba da Ra'uf ya turo Mukhtar Driver ya kaisu gida,kasancewar mijin Aunty Samira baya gari a lokacin shine dalilin shiga motar ya ajeta a gidanta da take rijiyar zakin itama da sai ka fara zuwa gidansu Rufaida kafin nata
******
"Oyo oyo Yaya Rufaida munyi kewarki"
Su Rafi'a suka cacimeta suna fa'dar haka
"Nima nayi kewarku,gashi ba nida waya bare mu riqa gaisawa"
"Dama dole kiyi kewarsu gashinan harkuna angijemin dana ba"
Ummi Hauwa'u ta karasa maganar tana karasowa gurin da Ra'is yake yana kuka da yake can gefe da shima hardashi a rugowa tarar yayartasu da akayi gefe dashi
Daukarsa tayi ta'aje jakar hannunta tana"Ummi yi hakuri kinsan halin dai su Rumaisa da Rafi'a"tayi maganar tana shiga cikin falon da ta zauna kujera
"Kodai halinki ba"Ummi Hauwa'u tayi maganar itama ta nemi guri cikin kujerun falon ta zauna
Murmushi Rufaida tayi kawai ta gaisheda Ummintasu da Abbansu da shigowarsa gida kenan,Rumaisa kuma ta kinkimi jakar Rufaida tayi Upstairs(saman bene)da ita
Da murmushi Abba Aliyu ya dubeta bayan sun amsa gaisuwartata
"Wato saida kuka huta gidan Samina kukayo hanyar gida ko saida Umminku tagama girkin tarbarki kika zarce gidan Auntynku"
Dariya tayi "ni bangama Yaya Abdul 'din ba" d shine ya kira Nasiba sanda suka dawo har suke shaidamasa suna gidan Aunty Samina,
"Eh yanzu suka fita shida Abdul-Rashid Umminku ta aikesu,da naji yana zasu biya daukokuma keda Nasiba"
Sallamarsu Abdul ita ta katse maganar da Ummi ke kokarin yi
Amsa musu suka yi ya shigo falon
Abdul ya dubi Rufaida da take masa sannu da zuwa yana fa'din
"Yar rainin wayau bazan amsa miki ba,banda rainin wayau kinsan tahowa zakuyi kika samu wahala kukace zaku jira nazo daukarku saida muka je Aunty Samina tace drivern daya kawoku yadawo kaiku gida"
"Yi hakuri Yaya Abdul mun kikkiraka mu fadama bata shigaba"
Abdul yace dama mana haka zakice waye yakawoku gidan ne,Aunty Samina tana fadamin ko driven Ra'uf ko waye bandaiji sosaiba"
Rufaida tace"Eh drivern gidansu Ahmad ne mijin Samiha"
Shiru suka yi nawani lokaci
Ummi Hauwa'u ta katse shirun da cewa nasan dai kuncika cikinku gidan Samina bakya bukatar abinci yanzu"
Murmushi tayi tace" Wallahi Ummi a cike cikina yake,maikika girkamin"
Ummi Hauwa'u tace"Alala"
"Allah Ummi zanci zubomin ko dayane"
Harararta Ummi Hauwa'u tayi
"ni zan zubomiki ma lallai yarinya,nida ko tsaraba baki kawowa 'dana bama"
"Rufaida tace" Ummi kinsan banida kudi,yanzu Aunty Samira data siyawa Kalim chocolate a flyover ta bani nakawowa Ra'is tana jaka ta"
Abba Aliyu yacewa Abdul-Rafi
Kaga Abdul taho mu hau sama naga an manta damu uwa da 'ya sai fira suke ba'asamu ciki"
Rufaida tace
"Yi hakuri Abba bahaka bane"
"Kinga kyalesu Rufaida,muje dining kici abincinki"
Cewar Ummi Hauwa'u
Abdul dai baice komaiba dan har lokacin Ummi Hauwa'u bata daina fushi da shiba kan maganar da yayi akan saurayin Rufaidan,wanda shikuma a ganinsa addu'a yayi ma yar uwartasa"
Maganar Abba Aliyu ita ta katse tunanin Abdul
"Shikenan gwara ku tashi kubarmu muyi firarmu muma"
Dining Area su Ummi Hauwa'u suka koma Rufaida ta zuba alalan tafaraci suna taba firar da Ummintasu

SADIYA KHALIL*JININMU 'DAYA*
NA SADIYA IBRAHIM KHALIL
Wattpad :Sadiya Ibrahim Khalil
26
*WANNAN SHAFIN NAKI NE AISHA UMAR IBRAHIM(AUI) ALLAH YABADA SA'A YA KARA BASIRA A'I..MARUBUCIYAR ZANJIRATA ,DA NABARWA ZUCIYATA ALLAH YA BAR ZUMUNCI*

*Shafi na Ashirin da shidda 26*

Sallamar da Rufaida taji Ummi Hauwa'u tayi yasa ta aje Alqur'anin da take Karantawa kan sallayar data idar da sallar isha tayi hanzarin amsa mata ciki ummi Hauwa'u takarasa shigowa ta dubi Rufaida cikin kulawa tace
"Tilawa kike ne"tayi karasa maganar tana zama bakin gado"
"Eh Ummi"
"To Allah ya taimaka su Rumaisa sunyi sallah ko nagansu sun sauka kasa suna kallo"
"Eh Ummi sunyi tarema mukayi"
"To shikenan kizo Abbanku yana kiranki Ummi Hauwa'u takarasa maganar tana mikewa
Rufaida Alqur'an din ta dauke tasa cikin loka tabi bayan Ummin nasu

*****
Assalamu Alaikum Rufaida ta gabatar da sallamar a kofar dakin mahaifinsu saida ta jira aka amsa ta tashiga cikin dakin a zaune ta samu Ummi Hauwa'u saman Carpet da shigar ta kenan itama kusada mahaifiyar tata ta zauna tana cewa "Abba Sannu da hutawa"
Ya amsa
"Yawwa Rufaida"
Kafin yayi gyaran murya ya soma magana
"Rufaida Alhaji Hashim ya kirani yayimin maganar wani yaro kun hadu wajen bikin Samiha ya nuna yana sanki shine ya kira Alhaji Hashim ya nemar masa izinin fara zuwa fira wajenki,kuma yace daga gobe zai fara zuwa,ina fatan dai da izininki yayi maganar kuma kinasanshi kar azo yafara zuwa zance yayi karfi azo asamu Matsala dukda cewar ba a fatanta"
Murmushi tayi bata ce komaiba dan ita bata San mai zatace ba ga dokin San ganin Ra'uf da take don akwana dayan harta fara sabawa dashi saboda ya iya kalamai masu tausasa zuciya
Jin tayi shiru yasa Ummi Hauwa'u cewa
"Ai Abban Abdul ta amince tunda kaji tayi shiru"
Abba Aliyu ya girgiza kai
"A'a ki barta dai tayi magana shiru aiba amincewa kadai yake nufi ba akwai shirun da zakayi ba son abinda aka fadama kawai kake nufi ba,ki bata wayarki ta turomin message idan takoma dakinsu"
Ummi Hauwa'u tace"to amma wayar na gurin Rumaisa tana game"
"Na hanaki bawa yaran nan waya bakyaji ko wacce irin game ace har Rumaisa sai anbata....da wannan fadan da Abbansu yakewa mahaifiyarsu tabar dakin.
Kai tsaye kasa ta sauka ta amsa wayar gurin Rumaisa da yaya Abdul ke musu karatun hadisi amma Rumaisan hankalinta nakan waya saida ta mangareta ta amsa wayar danma bataso ta hadata da yaya Abdul din zama tayi nan ta turawa Abba Aliyu text ta amince anan ta cigaba da zama anan karatun da ita a zuciyarta tanajin sha'awar rayuwar gidansu dukda mahaifiyarsu ita kadai gurin iyayenta baisa sun lalatamata tarbiya ba sunbata tarbiya da suma yanzu Ummintasu ce jagaba gurin basu saida

Abba Aliyu da yakaranta text message din ya kalli Ummi Hauwa'u data fito bandakin da taje hadawa Abba Aliyu ruwan wanka yace
" kinga message (sakon)Rufaida tace ta amince"
Itama murmushi tayi tace
"Dama nasan da saninta tayi maganar munyi waya da Zainab a jiya da safe tace saurayin Rufaidan sun gaisa da yaxo daukarsu jiya da suka kwana gidanta"
"Eh dukda hakan kinsan dai zuciya Hauwah zata iya sauyamata tunani mudai yanzu fatanmu Allah ya tabbatar musu da Alkhairi ya kawar da dukkan sharruka"
"Amin ya Allah"cewar Ummi Hauwa'u
Chapter 25 · 0% Book details