← Book details Jininmu Daya Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 23 OF 57

Sashe 23

Jininmu Daya Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read

Da taimakon Rufaida da take masa kwatance ya kaisu har kofar gidan gidanta maikyau da karamin gate dinsa ,yayi parking din motarsa suka fito su Hudu Rufaida,Nasiba,Zainab,Iklima
Yatsaida Rufaida daya fito daga motar
"Zanje gida zan kiraki wayar Nasiba,ki gaida Aunty idan batayi barci ba idan na kira zaki hadamu"
"To Allah ya kaika lafiya"
"Amin nagode sarauniyar mata"
Da haka tabar gurin tabi bayansu Nasiba
Shima murmushi yayi yabi bayanta da kallo yayi waajen motarsa yaja yabar gurin
"Yam mata har kungama hirar"
Zainab ta furta haka bayan sun kai kofar gidan Aunty Zainab da suke cewa Aunty da Nasiba ke kokarin kiran Aunty Zainab da Ummi Hauwa'u ta turo musu Number dinta.
"Zee banasan wulakanci..."
Wake wulakancin Aunty Zainab da taji Rufaida na fadar haka da ta fito bude musu kofar gate din,shiga sukayi ta rufo kofar"
"Wallahi Aunty Zee ce daga mun gaisa da wani wanda ya kawomu nan yanzu take min maganarsa"
Aunty ta 'dan ha'de rai kana ta furta
"Ni banasan kula kulan nan na abokan anguna ya wanci dukda matansu wasu kuma da wadanda zasu aura ko idan sunada auran da wadanda zasu kara bakuba sakarci ne yawanci yakesa kawayen amarya soyayya da abokan ango gurin bikin kawarsu har su amince musu kuma yawanci da angama bikin zasu manta da yarinyar idan ta zurfafa ita zata jiyo kusan mutuncin kanku" tana maganar tana kokarin tura kofar falon su Rufaida suna biye da ita
Jin tayi shiru yasa Nasiba tayi caraf ta karfe zancen
"Aunty saurayin Rufaida ne abokin Ahmad ne,tun kafin biki suka ha'du da shi da bikin ne soyayyarsu ta kara kulluwa"
Murmushi Aunty Zainab tayi ranta tana yiwa 'yar dan uwan nata Allah yasa na kirki ne ya kuma tabbatar musu da alkhairi
shiga cikin falon sukayi duk suka jefar da jakarsu a saman kujerar falon suna maida gajiya
Rufaida tana ganin Asad 'dan Aunty Zainab a falo ta daukesa tana masa wasa
Ruwa da abinci ta kawo musu suka ci daganan suka gaishe da Aunty Zainab da take musu tsiyar busu fadamata Dinner din ba aida taje wayar Nasiba ce tayi kara ta mika hannu inda ta aje ta ta duba mai kiran ganin Ra"uf ne yasata mikawa Rufaidha wayar saida sukayi yar fira yace taba Aunty su gaisa sosai Aunty zainab taji Ra'uf ya kwanta mata arai nan ta yi wa Rufaida addua a ranta Allah yasa da gaske yake da aure yazo gareta ya kuma kareta da fadawa tarkon mayaudara suna gama wayar Aunty Zainab tayi zaman dirshan suna fira kamar duka tasansu alhalin Nasiba kawai ta sani bayan Rufaidan da haka mijinta Haris ya shigo ya samesu sannu da zuwa suka masa tare da gaishesa ya amsa fuska sake kana yace wa Rufaida
"Ansha Dinner baki gayyace mamarki Ba bare nasa ran zaki gayyace ni ,da mukayi waya da Yaya Aliyu da Mamarku suke sanarda mu zaku zo anjima ku Kwana anan yanzu kuna wajen dinner"
"Uncle Haris ayimin afuwa yanzu Aunty taga ma mana maganar walllahi mantawa nayi kuma kaga bamu baro Sokoto da wuri ba"
"Zaki tuna ne ai Allah ya sanya Alkhairi"
Ya na gama furta haka yabar wajen da Asad a hannunsa da yana shigowa ya daukesa shigewa ciki yayi Aunty Zainab tami ke tabi bayansa
Da Amin suka bi addu'arsa suka cigaba da fira
Rufaida ta dubi Nasiba ta fara magana
"Wai niko Nasiba ina duriyar Sir Abdul-Rahman"
"Ke dai bari mun rabu da waya tun waccen ranar amma bari nakira mana shi mugaisa"
Ta karashe maganar tana mika hannunta inda ta aje wayarta ta dannan number din Abdul-Rahman Ringing biyu tayi ta katse baifi sakan biyu ba wayarta tayi kara ta duba taga Abdul-Rahman ne ta 'daga ta kunna karar wayar da zolaya ya fara yana
"Amare to ya hidindimun biki"
"Sir Alhamdulillah,ina yini"
"Lafiya lau ya biki"
"Alhamdulillah sir"
"Ina Amarya"
"Wallahi Sir tana gidanta yau aka kawota mukuma muna gidan Kanwar Abbansu Rufaida sai zuwa gobe zamu dawo Kano insha Allah"
"To Allah ya tabbatar da Alkhairi ya kaimu naku,ina Rufaidan da take bata"
"Amin"
Nasiba ta mikawa Rufaida waya suka gaisa sukayi sallama.
Aunty Zainab ta dawo falon tace su koma daki suyi shirin kwanciya.

*SADIYA KHALILULLAH🖊️*️*JININMU 'DAYA*
*BY SADIYA IBRAHIM KHALIL*
*(SADIYA KHALIL)*

*PAGE 24*
*WANNAN SHAFIN NAKUNE SADIYA KHALIL CONVERSATION ROOM,DA JININMU 'DAYA FAN'S GASHINAN KUYI YADDA KUKESO DASHI MASU COMMENT KU CIGABA DA COMMENT'S KU CIGABA DA SAMUN CIGABAN LITTAHIN🥰🥰SADIYA KHALIL NAGODIYA*

*PAGE 24*

***
9am
Suka gama shirinsu suka fito kofar gate din gidan da Ra'uf yazo yake jiransu su fito ya kaisu gidan amarya Aunty Zainab itada mijinta Haris har kofar gida sukayi musu rakiya Ra'uf da ya fito ya gaishesu cikin girmamawa da Aunty Zainab taji kunya sosai tunda ya girmeta kuma taji ya kwanta mata a rai haka suka shiga mota ya jasu ran Aunty Zainab ba dadi bataso tafiyarsu ba.
Ra'uf suka gaisar ya amsa yana tada motarsa
Saida suka soma tafiya ya cewa Nasiba da take gaban motar
"Yana ji Rufee Sarauniyar mata shiru kodai kun mata laifi ne"
Nasiba ta juya ta kalleta daga bisani ta furta
"Ko 'daya ba laifin da aka mata kasan miskilace budurwar taka,saika riqa hakuri"
Dariya yayi ya furta
"Baruwana keda kawarki kuma tana jinki"
"Ai tasan hakane"
Rufaida da tana jinsu tayi banza dasu dan Nasiba akwai surutu sunsan halinta
Basu jima suna tafiya ba suka karasa Isa kaita Road suka shige kwanar gidan Samiha saida Ra'uf ya fita ya bude gate din gidan kasancewar basuda mai gadi kafin yakoma yaja motar zuwa cikin gidan a harabar gidan suka tarar da su Aunty Samina da har sun shirya tafiya Ahmad ya kira Drivernsu zai maidasu gida Sokoto da Samiha harta fara kuka na tafiyarsu kamar wata yarinyar goye bayan basu duka zasu tafi a lokacinba
Sai da suka gaisa kafin Yaya Balki ta furta
"Ku kuma sai yanzu zaku dawo kun daka tasu Rufaida da ita Rufaida a gida take"
"Mama bahaka bane abokin ango ne baizo da wuri ba"Zainab tayi maganar da sigar tsokana
"Ba wani laifinsa basai kun shirya zaku kirasa ba,ku wuce ku shiga mota keda Iklima"
Ra'uf yaji dadi da yaga Yaya Balki bata goyi bayansu ba ya kuma fahimci Zainab da wasa tayi maganar dako anan yana kyautata zaton ya samu shiga murmushi yayi
Da haka su Zainab suka shige suma sauran matan da Yaya Balki suka shige motar har jikin motarsu su Rufaida sukaje yi musu rakiya sukuma suna zolayar Rufaida said bikinta zasu zo Kano itadai murmushi tayi Ra'uf da matso shima yayiwa su Zainab da iyayensu sallama bayan sunyi ne ya zaro kudi masu yawa ya mika musu sunji godiya suka yi masa da haka motarsu tabar gidan motarsu
Cikin gidansu Aunty Samina suka koma da ita da Aunty Samira da Nasiba su sai anjima Ahmad yace musu Ra'uf zai ajesu gida da shima yau zaikoma Kano
Chapter 23 · 0% Book details