Sashe 30
Jininmu Daya Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Rufaida da ta shigo 'dakinsu gado kawai ta fa'da tana kuka, karar wayar ta da taji ne ya sata mi'ka hannu domin nemo inda take wadda kafin ta hango ta kan drower gefen gado har ta katse ta na dauka kira a kalla goma ta gani da duk dai number 'din Ra'uf ce da ta ganesa da sunan data sa masa YAYA RA'UF, Wani kiran nasa ne ya 'kara shigowa bata tsaya 'bata lokaci ba ta 'dauka muryarsa taji cikin 'bacin rai amma duk da haka yadda yake maganar sa babu hargowa haka yake yin ta a tsanake yace
"Rufaida ban ta'ba tunanin ahalina sun cancanci tozartawa a gurin ahalinki ba, sannan ba zan gushe ba face ina miki fatan samuwar rayuwa mai inganci a rayuwar ki ta nan gaba bai saurari wani abu da zata ce ba ya kashe wayarsa gaba 'daya ma duk da ya san Rufaida ba zata kira saba hasali ma yadda ya fahimta ita ba mai damuwa bace da son su ri'ka waya sosai dan sai yace tun da suka fara waya sau 'daya ta kira sa shima Ra'is ne ya dameta ta kira shi su gaisa, yana ajiye wayar sai a sannan hawaye masu zafi suka zubo masa, domin ya san zai yi wuya ya 'kara samun mace kamar Rufaida nutsatstsiya mai sanin ya kamata mai kawaici, tabbas iyayensu basu zamo masu kyautuwa a karon farko a gare shi ba, hawayen nasa ne suka ci gaba da zubowa, daga bisani ya mi'ke ya shiga ban'daki ya 'dauro alwala ya fara nafilfilo da kai kukansa ga mahaliccinmu da neman tuba izuwa ga Allah. Yana idarwa kuma ya fara azkar kafin ya 'dauki alqur'an ya ci gaba da karantawa a hankali yaji damuwarsa tana raguwa, Sai dai kuma garin kano ta masa zafi ba zai iya kwana a cikinta ba a yau , Mukhtar driver ya kira bayan ya shirya kayansa ya zo ya 'dauka yasa a boot, dakin Momy Hannatu kai tsaye Ra'uf ya nufa ya 'kwan'kwasa mata, Ta basa izinin shiga da take a falonta ta zuba ta gumi da alama ita ma tana cikin damuwa, a kujerar dake kusa da Momy ya zauna ya dubi Momy ya na cewa
"Momy dan Allah kada damuwar rabuwa ta da Rufaida ta dame ki Allah ne ya ha'damu dama, yanzu kuma Allah bai sa dama zamu yi rayuwa mai tsawo da ita ba, Amma Momy Kano ta yi min zafi haka ma Nigeria na yanke shawarar zan bi Ammi jibi mu koma Delhi tare".
"Haka ne Ra'uf Allah ya yi maka albarka, Amma ba na son ka tafi domin shi kansa Dady ba zai so haka ba bare kuma ni"
"Amin Momy, sai dai tafiyar tawa itace zata sa na manta da komai in dai Allah ya so na manta 'din dan Allah Momy ki barni na tafi".
Ba dan ta so ba ta amince da tafiyar tasa
Har mota ta raka sa ita da Husna da take magiyar kar ya tafi kallon Husna ya yi yace "banda abin Husna ai kema Dady zai kawoki Delhi idan jarabawarku ta fito".
Motar su ce ta bar gidan
Inda Momy ke hawayen rabuwa da Ra'uf 'dan 'yar uwa a gare ta ba tare da ya cika burinsa ba na auren Rufaida, Da take ganin ina ita 'din da namiji ce kuma tana da iko akan aurawa Ra'uf Rufaida da sai ta yi 'ko'karin aura masa Rufaida.
"Mukhtar ka yi kwana ina so naje Danbatta yi wa Yakumbo sallama". Ra'uf ya ce haka da sai yanzu ya tuna al'kawarin da ya yi wa Yakumbo cewa zai je mata sallama idan zai koma.
SADIYA KHALIL🖊️😊*JININMU 'DAYA*
NA SADIYA IBRAHIM KHALIL
Wattpad Sadiya Ibrahim Khalil
SHAFI NA TALATIN DA BIYU 32
KUYI HAKURI MASOYAN LITTAFIN JININMU DAYA BAZAKU RIKA SAMUN TYPING DINA KO YAUSHE BA,SANNAN A WATTPAD BAN FARA UPDATING BA ANA UKU NAKE A WATTPAD MASU SO DAGA FARKO SU RIKA DUBAWA ACAN.IDAN SUNAYI SABODA ANAMIN MAGANA BANASAMUN DAMAR TUROWA.
Minti na da basu wuce arba'in ta sada su da garin Danbatta a, a kofar wani gida suka yi parking 'din motarsu gidan siminti ne sai dai babu shafe a kofar gidan Yara ne suka baibaye motar domin suga mai fitowa a ciki Ra'uf ne ya fito da gudu yaran da suka san shi mata da maza suka baibaye shi suna masa oyoyo, Hannun yaron ya rike suka isa kofar cikin gidan da gidan yake 'bangare uku 'bangaren yakumbo ne farko said 'bangaren kawu sunusi da na kawu Lami'do gidajen ginin zamani ne bangaren Yakumbo ya nufa kai tsaye sai da ya 'kwan'kwasa mata 'kofarta ta 'karaso 'kofar tana fa'din ince dai wannan yaron ba ne Salmanu ta'karasa maganar ta na bu'de 'kofa, Ganin Ra'uf ya sata saurin matsawa ta basa hanya ya shigo ciki cikin 'dakuna ne guda uku a biranda sai kuma kitchen da 'bandak a daga gefe da kuma 'karamin 'daki
Cikin fara'a take cewa"lale marhabin da babban ba'ko, a garin Danbatta" Tana ko'karin shinfi'damasa tabarma a saman tiles 'din dake barandar gidan da take share, Tsaftar yakumbo tana birge Ra'uf dan shi dama mutum ne mai son tsafta
Zama yayi yana cewa"Yawwa Yakumbo sarkin tsaftar garin Danbatta"
"Kai rufamin asiri ina ni ina zama mai tsaftar Danbatta gaba 'daya , Ko ka 'dauka 'kan'kantarta kamar garin jajayen fatar nan ne
" A'a Yakumbo Allah Delhi ta lin'ka Danbatta sau million ma"
"kada fa karaina Danbatta dan nanne dai asalinka ko ka'ki ko kaso"
"Eh haka ne , Amma kuma gaskiya na fa'da ta lin'ka Danbatta sau 'dari ko fiye da haka,Kuma Allah Yakumbon mu mai tsaftace "
"Ahaf ka dai fa'di gaskiyya da kace ta linka Danbatta sau million To ai yaro tsafta cikon Addini ce, Allah yasa dai Matar taka mai tsafta ce, Ba irin yaron yanzu ba masu 'dan karon son jiki, Dai dai da abinci ma 'danye suke yin shi, Bare a saran shara da wanke wanke"
Bai ce komai ba har yaron da suke shigo da kayan tsarabar da ya tsaya a hanya suka siya da Mukhtar su kashigo da ita , Mukhtar ya na ta yasu, Tsarabar ya bawa yaran suka fice da murnarsu suka nufi gida suna nunawa
Sai a sannan suka gaisa da Yakumbo
Yake tanbayarta ina Baffa
"Tun safe ya tafi gona shida kawunka sai zuwa ya manyar nan muke saran dawowar su"
"Allah ya dawo dasu lafiya , Amma ya kama ta Baba ya daina zuwa gona Amma har yau ya'ki ha'kura"
"Amin , Kai kajini da yaro idan baya motsa jikinsa wacce lafiya zaiyi jini baya yawo yadda ya kama ta"
Mukhtar da ke gefe zaune kusa da Ra'uf dariya yayi
Ya gaishe da Yakumbo yana cewa, "Kwarai kuwa yakumbo kin fa'di gaskiyya
"Ra'uf yace sai kaje kai ta zuga su"
Ruwan hannunsa ya a jiye yana kallon Mukhtar da ke gefen sa saman tabarma yace "Yakumbo bari muje muyi sallar la'asar naga a nata shiga masallaci"
"A dawo lafiya "
A 'kofar fita gidan suka ci karo da Kawu Lami'do 'kanin mahaifiyarsa, Har 'kasa su ka durkusa gurin gaishe sa, Ya amsa musu cikin sakin fuska "yana cewa a'a Ku tashi",
Bayan sun fito gidan Lami'do ya kalli Ra'uf da shima ya fito tafiya masallaci yana cewa "wata saban gani gani yaushe rabanka da zuwa Danbatta sai nace anyi shekara biyu ko anfi haka ma"
"A'a kawu shekara biyu kenan"
"A fa'dar ka ba", Mukhtar shekara nawa raban Ra'uf da zuwa"
Mukhtar yace"Kawu shekara biyu kenan"
"Wato kaima ka biye ta tashi kenan, Dan kaima kaga ba zuwa ka ke ba"
Da haka suka shiga cikin masallacin da baida nisa da gidan
Ra'uf ne ya hangi su Baffa da suke fito wa daga masallaci da fatanya a rataye a kafa'darsu, Saurin 'karasawa gurin su yayi kafin su Mukhtar su 'karasa fitowa gaishe su, cikin ha'din baki suka amsa, Inda Baffa yace
"A'a wa nake gani kamar Abdul-Ra'ufu , Sunusi dubamin shi nagani, Baffa ya fa'di haka"
"Kwarai kuwa nine babu ko kwanto Baffa"
Baffan yace "yaushe Raban duniya da aiya raye", su Kawu Lami'do na 'karasowa, Suka gaisa da Mukhtar su ka shiga cikin gidan"
'Bangaren Baffa suka shiga Fa'da suka sameta ta nayi da yaran da suka shigo 'bangarenta tana cewa su fita karsu 'batama ta gida su koma suyi wasan gurin iyayensu, Ba za'a turo mata su ba su 'bata mata gida ba iyayensu sun gyara nasu gurin, Su ko sunyi shiru suna cigaba da wasa, Da 'kara ta bisu 'kofar 'Bangaren nata inda yayi dai-dai da shigowar su Ra'uf 'din bayan su suka 'boye kada ta dokesu, Karan tayar ta koma ciki, Da yaran suka shigo Baffa da kawu Lami'do suka ajiye fatanyar a biranda, suka shiga falo suka zazzauna, Ra'uf ya kalli yaran da suke zaune kusa da shi da suke su hu'du, mata biyu maza biyu, Yace musu ku Kyale yakumbo idan na sake dawowa tare zamu tafi na maida ku gurin Ammi, Tsalle suka farayi inda Yakumbo ta shigo musu da abinci ta samesu suna tsallen murna tsaki tayi musu tace
"Wannan 'kauyawan za'a kai birni"
"Kwarai kuwa Yakumbo tunda Ammi bata da 'kananun yara ga shi ba kya barinsu suyi wasa a bangarenki"
"Ahaf ai wa'dannan yaron idan ka kaisu wannan 'kasar sai ka kirani ka fa'damin 'barnarsu kuwa"
"Ai yakumbo mun daina ki tambayi su umman mu kiji" yaran suka ha'da baki gurin cewa haka
Kawu Lami'do yace wato su salmanu ana son tafiya birnin india, ya fa'da yana dariya
Abinci suka ci Kafin ya fito su shiga zaga dangi da yawanci suna zaune a kauyen kunya kauyen Danbattan da yake yawanci kauyeb Fulani ne duk inda yaje da irin alkhairun da yake musu da yara ke raka shi a motar sa
Yakumbo ce ta kallesa da ta shigo ta zauna a falo inda Ra'uf da Baffa suke ciki Ra'uf ta duba tace "a lallai Ra'uf yau ansha yawo"
"Wallahi ko Yakumbo ai yau na zaga gari ji nake kamar duka kunya da Danbatta danginmune"
"Baffa yace kai Ra'uf Danbatta fa ba 'kauye bace mai gida nan sai kayi gaba ka tarar da wani,dama kunyan kace saina yadda
"Rufaida ban ta'ba tunanin ahalina sun cancanci tozartawa a gurin ahalinki ba, sannan ba zan gushe ba face ina miki fatan samuwar rayuwa mai inganci a rayuwar ki ta nan gaba bai saurari wani abu da zata ce ba ya kashe wayarsa gaba 'daya ma duk da ya san Rufaida ba zata kira saba hasali ma yadda ya fahimta ita ba mai damuwa bace da son su ri'ka waya sosai dan sai yace tun da suka fara waya sau 'daya ta kira sa shima Ra'is ne ya dameta ta kira shi su gaisa, yana ajiye wayar sai a sannan hawaye masu zafi suka zubo masa, domin ya san zai yi wuya ya 'kara samun mace kamar Rufaida nutsatstsiya mai sanin ya kamata mai kawaici, tabbas iyayensu basu zamo masu kyautuwa a karon farko a gare shi ba, hawayen nasa ne suka ci gaba da zubowa, daga bisani ya mi'ke ya shiga ban'daki ya 'dauro alwala ya fara nafilfilo da kai kukansa ga mahaliccinmu da neman tuba izuwa ga Allah. Yana idarwa kuma ya fara azkar kafin ya 'dauki alqur'an ya ci gaba da karantawa a hankali yaji damuwarsa tana raguwa, Sai dai kuma garin kano ta masa zafi ba zai iya kwana a cikinta ba a yau , Mukhtar driver ya kira bayan ya shirya kayansa ya zo ya 'dauka yasa a boot, dakin Momy Hannatu kai tsaye Ra'uf ya nufa ya 'kwan'kwasa mata, Ta basa izinin shiga da take a falonta ta zuba ta gumi da alama ita ma tana cikin damuwa, a kujerar dake kusa da Momy ya zauna ya dubi Momy ya na cewa
"Momy dan Allah kada damuwar rabuwa ta da Rufaida ta dame ki Allah ne ya ha'damu dama, yanzu kuma Allah bai sa dama zamu yi rayuwa mai tsawo da ita ba, Amma Momy Kano ta yi min zafi haka ma Nigeria na yanke shawarar zan bi Ammi jibi mu koma Delhi tare".
"Haka ne Ra'uf Allah ya yi maka albarka, Amma ba na son ka tafi domin shi kansa Dady ba zai so haka ba bare kuma ni"
"Amin Momy, sai dai tafiyar tawa itace zata sa na manta da komai in dai Allah ya so na manta 'din dan Allah Momy ki barni na tafi".
Ba dan ta so ba ta amince da tafiyar tasa
Har mota ta raka sa ita da Husna da take magiyar kar ya tafi kallon Husna ya yi yace "banda abin Husna ai kema Dady zai kawoki Delhi idan jarabawarku ta fito".
Motar su ce ta bar gidan
Inda Momy ke hawayen rabuwa da Ra'uf 'dan 'yar uwa a gare ta ba tare da ya cika burinsa ba na auren Rufaida, Da take ganin ina ita 'din da namiji ce kuma tana da iko akan aurawa Ra'uf Rufaida da sai ta yi 'ko'karin aura masa Rufaida.
"Mukhtar ka yi kwana ina so naje Danbatta yi wa Yakumbo sallama". Ra'uf ya ce haka da sai yanzu ya tuna al'kawarin da ya yi wa Yakumbo cewa zai je mata sallama idan zai koma.
SADIYA KHALIL🖊️😊*JININMU 'DAYA*
NA SADIYA IBRAHIM KHALIL
Wattpad Sadiya Ibrahim Khalil
SHAFI NA TALATIN DA BIYU 32
KUYI HAKURI MASOYAN LITTAFIN JININMU DAYA BAZAKU RIKA SAMUN TYPING DINA KO YAUSHE BA,SANNAN A WATTPAD BAN FARA UPDATING BA ANA UKU NAKE A WATTPAD MASU SO DAGA FARKO SU RIKA DUBAWA ACAN.IDAN SUNAYI SABODA ANAMIN MAGANA BANASAMUN DAMAR TUROWA.
Minti na da basu wuce arba'in ta sada su da garin Danbatta a, a kofar wani gida suka yi parking 'din motarsu gidan siminti ne sai dai babu shafe a kofar gidan Yara ne suka baibaye motar domin suga mai fitowa a ciki Ra'uf ne ya fito da gudu yaran da suka san shi mata da maza suka baibaye shi suna masa oyoyo, Hannun yaron ya rike suka isa kofar cikin gidan da gidan yake 'bangare uku 'bangaren yakumbo ne farko said 'bangaren kawu sunusi da na kawu Lami'do gidajen ginin zamani ne bangaren Yakumbo ya nufa kai tsaye sai da ya 'kwan'kwasa mata 'kofarta ta 'karaso 'kofar tana fa'din ince dai wannan yaron ba ne Salmanu ta'karasa maganar ta na bu'de 'kofa, Ganin Ra'uf ya sata saurin matsawa ta basa hanya ya shigo ciki cikin 'dakuna ne guda uku a biranda sai kuma kitchen da 'bandak a daga gefe da kuma 'karamin 'daki
Cikin fara'a take cewa"lale marhabin da babban ba'ko, a garin Danbatta" Tana ko'karin shinfi'damasa tabarma a saman tiles 'din dake barandar gidan da take share, Tsaftar yakumbo tana birge Ra'uf dan shi dama mutum ne mai son tsafta
Zama yayi yana cewa"Yawwa Yakumbo sarkin tsaftar garin Danbatta"
"Kai rufamin asiri ina ni ina zama mai tsaftar Danbatta gaba 'daya , Ko ka 'dauka 'kan'kantarta kamar garin jajayen fatar nan ne
" A'a Yakumbo Allah Delhi ta lin'ka Danbatta sau million ma"
"kada fa karaina Danbatta dan nanne dai asalinka ko ka'ki ko kaso"
"Eh haka ne , Amma kuma gaskiya na fa'da ta lin'ka Danbatta sau 'dari ko fiye da haka,Kuma Allah Yakumbon mu mai tsaftace "
"Ahaf ka dai fa'di gaskiyya da kace ta linka Danbatta sau million To ai yaro tsafta cikon Addini ce, Allah yasa dai Matar taka mai tsafta ce, Ba irin yaron yanzu ba masu 'dan karon son jiki, Dai dai da abinci ma 'danye suke yin shi, Bare a saran shara da wanke wanke"
Bai ce komai ba har yaron da suke shigo da kayan tsarabar da ya tsaya a hanya suka siya da Mukhtar su kashigo da ita , Mukhtar ya na ta yasu, Tsarabar ya bawa yaran suka fice da murnarsu suka nufi gida suna nunawa
Sai a sannan suka gaisa da Yakumbo
Yake tanbayarta ina Baffa
"Tun safe ya tafi gona shida kawunka sai zuwa ya manyar nan muke saran dawowar su"
"Allah ya dawo dasu lafiya , Amma ya kama ta Baba ya daina zuwa gona Amma har yau ya'ki ha'kura"
"Amin , Kai kajini da yaro idan baya motsa jikinsa wacce lafiya zaiyi jini baya yawo yadda ya kama ta"
Mukhtar da ke gefe zaune kusa da Ra'uf dariya yayi
Ya gaishe da Yakumbo yana cewa, "Kwarai kuwa yakumbo kin fa'di gaskiyya
"Ra'uf yace sai kaje kai ta zuga su"
Ruwan hannunsa ya a jiye yana kallon Mukhtar da ke gefen sa saman tabarma yace "Yakumbo bari muje muyi sallar la'asar naga a nata shiga masallaci"
"A dawo lafiya "
A 'kofar fita gidan suka ci karo da Kawu Lami'do 'kanin mahaifiyarsa, Har 'kasa su ka durkusa gurin gaishe sa, Ya amsa musu cikin sakin fuska "yana cewa a'a Ku tashi",
Bayan sun fito gidan Lami'do ya kalli Ra'uf da shima ya fito tafiya masallaci yana cewa "wata saban gani gani yaushe rabanka da zuwa Danbatta sai nace anyi shekara biyu ko anfi haka ma"
"A'a kawu shekara biyu kenan"
"A fa'dar ka ba", Mukhtar shekara nawa raban Ra'uf da zuwa"
Mukhtar yace"Kawu shekara biyu kenan"
"Wato kaima ka biye ta tashi kenan, Dan kaima kaga ba zuwa ka ke ba"
Da haka suka shiga cikin masallacin da baida nisa da gidan
Ra'uf ne ya hangi su Baffa da suke fito wa daga masallaci da fatanya a rataye a kafa'darsu, Saurin 'karasawa gurin su yayi kafin su Mukhtar su 'karasa fitowa gaishe su, cikin ha'din baki suka amsa, Inda Baffa yace
"A'a wa nake gani kamar Abdul-Ra'ufu , Sunusi dubamin shi nagani, Baffa ya fa'di haka"
"Kwarai kuwa nine babu ko kwanto Baffa"
Baffan yace "yaushe Raban duniya da aiya raye", su Kawu Lami'do na 'karasowa, Suka gaisa da Mukhtar su ka shiga cikin gidan"
'Bangaren Baffa suka shiga Fa'da suka sameta ta nayi da yaran da suka shigo 'bangarenta tana cewa su fita karsu 'batama ta gida su koma suyi wasan gurin iyayensu, Ba za'a turo mata su ba su 'bata mata gida ba iyayensu sun gyara nasu gurin, Su ko sunyi shiru suna cigaba da wasa, Da 'kara ta bisu 'kofar 'Bangaren nata inda yayi dai-dai da shigowar su Ra'uf 'din bayan su suka 'boye kada ta dokesu, Karan tayar ta koma ciki, Da yaran suka shigo Baffa da kawu Lami'do suka ajiye fatanyar a biranda, suka shiga falo suka zazzauna, Ra'uf ya kalli yaran da suke zaune kusa da shi da suke su hu'du, mata biyu maza biyu, Yace musu ku Kyale yakumbo idan na sake dawowa tare zamu tafi na maida ku gurin Ammi, Tsalle suka farayi inda Yakumbo ta shigo musu da abinci ta samesu suna tsallen murna tsaki tayi musu tace
"Wannan 'kauyawan za'a kai birni"
"Kwarai kuwa Yakumbo tunda Ammi bata da 'kananun yara ga shi ba kya barinsu suyi wasa a bangarenki"
"Ahaf ai wa'dannan yaron idan ka kaisu wannan 'kasar sai ka kirani ka fa'damin 'barnarsu kuwa"
"Ai yakumbo mun daina ki tambayi su umman mu kiji" yaran suka ha'da baki gurin cewa haka
Kawu Lami'do yace wato su salmanu ana son tafiya birnin india, ya fa'da yana dariya
Abinci suka ci Kafin ya fito su shiga zaga dangi da yawanci suna zaune a kauyen kunya kauyen Danbattan da yake yawanci kauyeb Fulani ne duk inda yaje da irin alkhairun da yake musu da yara ke raka shi a motar sa
Yakumbo ce ta kallesa da ta shigo ta zauna a falo inda Ra'uf da Baffa suke ciki Ra'uf ta duba tace "a lallai Ra'uf yau ansha yawo"
"Wallahi ko Yakumbo ai yau na zaga gari ji nake kamar duka kunya da Danbatta danginmune"
"Baffa yace kai Ra'uf Danbatta fa ba 'kauye bace mai gida nan sai kayi gaba ka tarar da wani,dama kunyan kace saina yadda