← Book details Hurriya Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 70 OF 133

Sashe 70

Hurriya Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

“Karya kike ki fada min wannan, tun kamin a haifeki na ke kula da dana, ni na san fadi tashinsa ba ke ba, ke kullun kara hauka kike ba hankali ba yayanki ma gasu nan kin fara koya musu irin tarbiyarki”

Hajiya Kaltume zata sake yin magana wata yayarta ta rufe mata baki, tana bawa Hajiya Binta hakuri.

“Babba babba ne ko yayane, dan Allah Hajiya ki yi hakuri, wani lokacin Kaltume bata iya rike halshe, kar idonki ya rufe Hajiya ayi babu dadi a nan?”

“Babu dadi na nawa kuma? Ita da yarta ta mutu idonta be bude ta yi hankali ta natsu ba? Me ye bata fada min ba? Ai wannan yar bata da albarka sam...”

Hajiya Kaltume ta mike tsaye ta daki kirjinta dake mata zafi da ciwo a lokaci daya tana kuka mai karfi ta ce

“Ba yar albarka ba ce ni Hajiya Binta, ki aura masa yar albarka ki kawo, ni kuma ki saka bindiga ki halbeni ni da yayana”

Hajiya Binta ta kashe ido tana kallon surukar dake mata rashin albarka ta ce.

“Idan kin kwana da aure yau Kaltume na kwana a mace...! Sai na nuna miki ruwan nono ya fi karfin wulakantawar”

Hajiya Binta ta kalli Maryam da ke tsaye gefe daya tana karewa Khairy da Maama kallon daukar fansa ta ce.

“Wuce mu tafi yarinya...”

Maryam ta juya ta fice tare da Cousin dinta, Khairy da Maama kuma suna jin kamar su rufe Hajiya Binta da duka babu hali, Ruma ce kadai ke rusar kuka saboda abun da ke faruwa baya mata dadi sam. Hajiya Fatee da wasu yan'uwan Hajiya Kaltume suka bita suna bawa Hajiya Binta hakuri amman ba ta sauraresu ba ta fice. Yayarta ce ta dawo dakin tana fadar.

“To yanzu me ye amfanin haka? Jiya kin ci mutuncin yarinya yau kin ci ta wannan yarinyar kuma abun be tsaya iya kansu ba sai da ya kai ga uwar miji? Haba Kaltume, mutuwa tana saka mutane natsuwa amman ke kamar ana turaki?”

“Anty Hauwa ki bar ni da bakincikin da yake cikin raina, ni na san me nake ciki, ni na san irin halin da nake ciki”

Ta fashe da kuka mai karfi. Maama da Khairy ma sai da suka yi kuka saboda ganin mahaifiyarsu na kuka, daman kuma zafin mutuwar yar'uwarsu be isa barin zuciyarsu ba. Sai bayan Sallah La'asar lokacin mutane sun dan fara ragewa, daman wasu sai dai su zo su yi gaisuwa su tafi, Appa ya aiko ya aiko kiran Hajiya Kaltume tare da Khairy da Maama da Ruma, suna jin haka suka san ba dalilin kiran, Hajiya Kaltume gabanta ko faduwa baya yi saboda zuciyarta ta riga da dake, yadda abubuwa suka riccabe mata bata fargabar faruwar komai a yanzu. Can cikin uwar dakin Appa suka shiga, Appa yana zaune kana ganin fuskarka kasan ransa a nace yake. A kasa Maama da Khairy har Ruma suka zauna, Hajiya Kaltume ta zauna a kujerar sofa daya dake dakin idonta a kumbure ga wani ja da suka yi tsabar kuka da bakinciki da suka rumgume.

“Akan wani dalili yarinya zata zo tun daga nesa ki ci mutuncinta ke da yayanki?”

“Me yasa zata zo? Ba abun kunya ba ne dubi kamar kai ace zaka auri kawar yarka? Wato Hajiya ta zo ta tsara maka maka komai, so ake a hada min zafi ta ko'ina kamar ni na haifowa duniya bakin duhu”

Ta fara kuka da karfi. Appa ya maida dubansa gurin Khairy da Maama.

“An fada min abun da kuka yi, kuma abun da kuka yi ba kowa kuka yi ma sai ni, ni kuka ciwa mutunci ni kuka wulakanta, sannan kun bar magana a bakin kowa, yar'uwarku ta mutu yau kwana daya amman wuni na buyu amman kuna dukan kawarta saboda ta zo gaisuwa, jiya ma ance kun yi ma Rukayya saboda rashin hankali da kikanci irin naku, to daga sai yau ko kare na kawo kuka tsallaka shi sai na yi muku abun da ba ku taba mafarkin ba, idan ita uwarku kishi take ku me kuke yi? Kar wanda ta sake tunkarata da wata bukata tata na yanke, du wata dawaniniya da nake da ku daga yau ta kare, idan har baku san darajata ba babu amfanin cigaba da yi muku komai, ke Maama ki tattara ki koma gidan mijinki zaman gaisuwa na kashe daga yau, domin gobe ban san abun da za su sake yi ba, ke kuma Khairy ki sani nan da kwanaki kadan zan aurar dake, ke tafi can gidan mijin ki yi hankali”

“Appa....”

Khairy zata yi magana ya daka mata tsawa.

“Shut up ku tashi ku ba ni guri”

Suka tashi jiki na rawa suka fice daga dakin suna kuka. A lokacin ne Appa ya kalli Hajiya Kaltume ya ce.

“Ke kuma ki yi zaman ƴaƴanki, kin ci mutuncina kin ci mutuncin kanki, kin ci mutuncin yayanki duk haka be miki ba sai da kika tsallaka kika ci mutuncin Hajiyata, matar da ta yi silar zuwana duniya, matar da ta rumgume tun bana iya tsayawa da kafafuwana, to kin kai karshe, ko da ace Hajiya bata ba ni umarnin aikata abun da na aikata a yanzu ba, zan aikata a karan kaina jin abun da kika yi mata Hallayenki sun isheni Kaltume, kin kawo min nan”

Ya kama makogaronsa da hannuna yana nunawa.

“Dan haka na iyankance alakata da ke a yau Kaltume, NA SAKE KI SAKI DAYA....”

Hajiya Kaltume ta sauko daga kam kujera tana taba kirjinta.

“Ka sake ke ni Alhaji? Ni Kaltume yau ni ka saka? Ehhhhhhh ehhhhhhh ehhhhhhh hmmmmmmmm”

Ta dora hannu akai tana dukan kanta kamar wata bayarabe.

“Ehhhooooooooo ehhhhwoooooooo hoooooo ni niiiiiiii hmmmmm kilkilkil ni aka saka? Lallai wani bakincikin sai namiji, bani bakin cikin sai namiji, yata ta mutu kuma ka sake ni, namiji dan kunama Haruna mai siyar da yadi ka ji kunya ka yi abun kunya, yau kam na tabbatar Binta bata kaunata yau na tabbatar da waye kai Haruna mai yadi, Mai yadi Haruna, tun baka da taro da sisi nake tare da kai, tun aka siyar da yadin uku da sisin kwabo, tun kana siyar da yadin mutuwa yadin likkafani nake tare da kai Haruna, yau ni ka saka saboda zaka auri yarinya sa'ar yarka? Lallai namiji ba dan goyo ba ne, namiji dan kunama, duk macen da ta ce namiji uba ne sai ta kwana marainiya”

Babu kalar gorin da bata yi ba Appa ba, dan Alhaji ma da take masa alkunya yau bata saka ba saboda bakar zuciyarta ta mutanen farko ta tashi, halin na mata masu bakin kishi da bakar zuciya ya motsa, tana murzar kafa a kasa tana kuka tana ihu arzikinsa daya dakinsa ba mai daukar magana ba ne sai an bude. Appa ya mike tsaye sai ta matsa da jan jiki ta riko rigarsa tana zuba masa rashin mutuncin.

“Ka tsaya mana mai abun kunya, saboda kana takama da arziki, arzikinka na banza, saboda kana takamar kana da kudi sai ka aure yar aiki yanzu kuma zaka auro kawar yarka, kuma duk a ni Kaltume bakincikin zai kare, ni zaka nunawa bakinciki? Allah ya saka ka auro mai farar kafa, idan arzikin ya kare sai ka ga zata zauna da kai ko kuma sai Hajiya Kaltume mai zuciyar karfe? Wallahi sai ka yi nadamar sakin da Binta ta saka ka yi min yau Haruna mai yadi”

Appa ya buge hannunta ya fisge rigarsa.

“Albakarcin fadin sunan uwata da kika sake yi da kuma addu'ar da kika yi, na kara miki saki daya, dazun saki daya na yi miki yanzu kuma na kara miki daya, Kaltume NA SAKE KI SAKI BIYU”

Hajiya Kaltume ta fadi kwance kasa tana burzar da yawu tana ware hannaye sama kamar wata mai aljannu.

“Shi ke nan na mutun yau an dandana min bakinciki ďa namiji yau an dandana bakinciki, so ake na mutu gaba daya”

Appa ya kabe mata rigarsa ya fice daga dakin yana jin kamar ya kara mata wani sakin, daman abun haka yake idan mace ta yi magani duk ranar da abun ya karye namiji zai tsaneta irin tsanar da be taba yi ba. Ficewa yayi daga bangare gaba daya domin baya son sauraren kalamanta da kukanta dake kara masa bacin rai, kuma baya son hankalin mutanen dake waje ya kai garesu. Yana tafiya hannayensa a baya yana tuna lokacin da ya saki Iyami, yarinya a cikin matansa amman bata yi wannan haukan da cin mutuncin da Kaltume ta yi masa da uwarsa ba, yana tuna lokacin da ya bata takardar sakinta a rubuce ta karba, har ta yi masa addu'ar Allah yasa hakan shi ne mafi alheri kuma ya ba shi ikom kula da Hurriya da Hamad. A yanzu yake tambayar kansa me yasa ya saketa? Why? Me ta yi masa? Me yasa ya rabu da matarsa abar kaunarsa? Har ya isa bangaren na Momy be samu amsar tambayarsa ba. Cikin yanayin damuwa da ya kasa boyuwa a fuskarsa ya murda kofar dakin ya tura ya shiga, ba zai iya fadar abun da ya kawo shi bangaren ba, kawai dai ya baro na shi bangaren ne saboda Hajiya Kaltume, ba zai iya barin gidan a yanzu da ake amsar gaisuwar yarsa ba, sai dai arba da tawayensa dake wasa a falon Momy suna mata tsalla akan kujeru Hurriya na kokarin hanasu sannan na fahimci kewar yaran da ya kasa zuwa ganinsu ya kasa karbarsu ya rumgume su a lokacin da aka haife su ce take kiransa.

“Salamu Alaikum”

Yayi sallama muryarsa na isar da rauninsa dake idonsa na arba da yaransa kanana da yayi, sai kuma ya samu kansa da kunyarsu damuwar abun da yayi musu ta yi kamar zata fadar da shi a tsakar falon. Hurriya da Namra suka amsa masa Namra na murmushi Hurriya kuma na faduwar gaba, tana addu'ar Allah yasa ba wani abun aka cewa Appa ta yi ba. Ya zauna kan kujera yana kiran Hamid dake tsalle yana rike da kwalbar lemu.

“Husaini baka tsoron ka fasa kwalbar ka ji ciwo”

Hurriya ta kalli mahaifinta da saurin jin da ganin yadda ya nunawa kanenta kulawa, Namra kuma ta dan hararesu ta ce.
Chapter 70 · 0% Book details