Sashe 2
Hurriya Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Ban taba sanin baka da hankali ba, sai yau Yasir ka kaita ta fadawa Iyami abun da ya faru kamar baka san halin da Iyami take ciki ba? Ciki ne fa a jikinta kuma tsohon ciki idan ta fadi ta rikice wani abu ya same ta ko ya samu abun da ke cikinta kai zaka mata magani? Wani irin shashanci ne wannan?”
Yasir yayi shiru sai a lokacin shi ma yake ganin abun da yayi na kai Hurriya a irin wannan lokacin be dace ba. Hajiya Kaltume ta fashe da kuka.
“Haba Alhaji wake da Iyami yanzu an dauke min yar shawalwalar yarinyar, mace ce fa, al kara ma Hamad namiji ne”
Appa ya tashi ya fice, Yasir ya bi bayansa, daga gidan station suka nufa daman kamin su isa Appa ya kira CP ya fada masa abun da ya faru, suna isa ya saka aka shigar da report kamin yan sanda da suke sashen kidnapping su tafi gidan aka kwaso duka yaran, ana tambayarsu yadda abun ya faru suna fada. Babban cikin su dake tambayar ya kalli Namra da ta kare nata bayanin ya ce.
“Wacece Hurriya? Ina ita Huriyyar take?”
“Tana gidansu”
“Okay ita ba yar'uwarku ba ce?”
Appa yayi gyaran murya dan ya san Namra zata iya wata kwabar.
“Yata ce, ni na haifeta amma yanzu tana gurin mahaifiyarta da ta koma gida haihuwa”
“To zamu iya ganin ita Huriyyar? Domin ga dukan alama ita aka zo dauka, ita da Ruma din a yadda na fahimta Hamad din tsautsayi ne ya rutsa da shi, rashin samun Hurriyya sai suka dauke Hamad din, dole akwai tambayoyin da nake son yi mata”
“Ni ma na yi wannan tunanin duba da irin labarin da suka ba ni, zan je na zo da ita”
Appa ya fada sannan ya kalli Yasir.
“Idan an gama ka maida su gida, ni zan je na taho da Huriyya”
“To Appa”
Yasir ya amsa cikin ladabi da biyayya, Appa ya ma Officer sallama ya fice. Tare da direbansa suka isa gidan Gwaggo, a waje suka faka motar direban ya fito ya bude masa mota ya fito. A ransa yana son shiga amman jin hake kamar ana tsikara masa allura a zuciya saboda ya doso gurin da Amma take.
“Bala, ka sallamo Hurriyya”
“Toh ranka ya dade”
Malam Bala ya wuce cikin gidan, Appa kuma ya jingina da mota, Malam Bala be dade ba ya dawo yana sanar masa Gwaggo tace ya shigo tana son magana da shi. Rasa yayi me zai ce, shi dai be isa ya juya yayi tafiyarsa ba, kuma yana jin kunyar hada ido da iyayenta ita kanta Amma a yanzu kunyarta yake ji. Haka dai ya daure ya danne duk wani abun azabar da yake ji ya shiga cikin gidan, sai da ya hada da addu'a sannan ya samu courage din shiga har cikin falon Gwaggo. Be zauna ba sai da ya risina ya gaishe da ita kamar yadda ya saba, ba dan ta girme shi ba, sai dai ma shi ya girme ta, yana bata girmata ne tun a lokacin da ta zama sukurukarsa a yanzu ma be yada girmanawarba, domin har a yanzu sun din suna da kima da daraja a idonsa.
“Hurriya ta shigo tana ta kuka, amman bata yi magana ba har yanzu ta kasa fadar abun da ya faru, a baki Rukayya muka ji cewar Yasir ne ya kawo ta ma, kuma da kayan makaranta ta shigo, babu gilashi a idonta, yanzu kuma sai ga Malam Bala ya shigo wai kana kiran Hurriya shiyasa na ce ya shigo da kai ciki mu ji abun da ya faru domin mu ma hankalinmu duk a tashe yake”
“Gwaggo, ni ma kaina ban san abun da ya faru ba. Shiyasa na kira Hurriyar na ji ta bakinta”
“Can gida ba su fada maka komai ba.?”
Appa ya ki yarda su hada ido.
“Ba su fada min ba, Hurriya tana kusa?”
“Eh tana dakin mahaifiyarta, bari a kirata”
Gwaggo ta tashi ta fita. Bata jima ba Iyami ta shigo falo tana sanye da digon Hijab har kasa Hurriya na rike da hannunta. Appa na kallonsa sai gashi ya mike tsaye yana kallon cikin dake jikinta cikin wani yanayi na rashin jindadi.
“Na fada maka babu uwar da zata so yayan wasu kamar nata, yanzu wannan tashin hankali duk na minene? Ba komawa gidanka nake bukata ba kwanciyar hankalin yayana kawai nake bukata a yanzu...”
“Iyami zauna”
Amma har ta yi kamar ta ce masa ba zata zauna ba, domin niyarta ta kawo Hurriya kuma ta jadda masa amanar yayanta ta koma, sai kuma ta zauna domin bata saba musa masa a komai ba. Sai da ta zauna sannan shi ma ya zauna.
“Ba wani abu aka yi mata ba, ki daina saka kishi da son cusa kiyayyar Kaltume ko Nafisa a zuciyar yayanki, ba dukan Hurriya aka yi ba, ba wata bakar magana aka fada mata ba, babu wanda ya mata komai, ba mutuwa aka yi ba”
“To miyasa ta zo tana min kuka? Kuma Yasir da ya kawo ta be shigo gidan ba ya fita?”
“Ni ma shi na zo tambayarta”
Amma ta kalli Hurriya har lokacin hawaye take sai dai ba kamar dazun ba. Ta kalli Appa
“Ina Hamad...!”
Appa ya ji tambayar kamar saukar aradu. Appa ya kalleta ya kasa cewa komai.
“Ina Hamad Appan Hurriya?”
“Dan Allah kin kwantar da hankalinki”
“Kamar ya na kwantar da hankalina? Miye abun tashin hankali a tambayar Hamad? Ko kuma shi ya aikata wani laifin?”
“be aikata laifin komai ba Wallahi, ki ba mu guri zamu yi magana da Hurriya”
Amma ta kalli Hurriya kamin ta mike tsaye ya fice daga falon. Appa ya tashi daga inda yake zaune ya koma kusa da Hurriya ya zauna ya rika yarsa.
“Hurriya”
“Na'am Appa”
“Ki kwantar da hankalinki kin ji, Hamad zai dawo soon da yardar Allah, babu abun da zai same shi, kuma na ji dadin da baki fadawa Iyami abun da ya faru ba, kin ga tana da ciki zata iya daga hankalinta,”
Ta daga kai ta kama hannun Appa ta jimke da karfi.
“Appa bana ganin komai yanzu, bana ganin komai sai abun da ya faru, me yasa suka dauke Hamad? Me yayi musu?”
“Wallahi dukanmu ba su sani ba, amman dai an san ba zai wuce su ce a ba su kudi ba, kamar yadda suka yi ma Kaltume kuma shi ma za su sako shi”
“Hadda Ruma aka kama”
“Na sani duka zamu biya kudi mu karbo su Da yardar Allah, amman yanzu zamu tafi dake gurin police za su miki tambayoyi akan abun da ya faru, saboda kun sanar da ya sanda, kamin nan kuma ina son ki min alkawarin ba zaki fadawa Iyami ba, kuma ki daina kukan nan har sai mun karbo shi”
Kamin Hurriyya ta dauki alkawarin suka jiyo Amma daga jikin curtains din kofar dakin tana furta.
“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un.
Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un
Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un”
Daga Appa har Hurriya ba su san Amma ta yi labe ba sai a lokacin. Appa ya taso ya fito da sauri yayinda Gwaggo ma ta fito da sauri daga dakin Amma ta nufota.
“Gwaggo sun dauke min Hamad, su biyu Allah ya ba ni sun dauke daya, kashe shi za su yi Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un”
Gwaggo ma ambaton Allah ta shiga yi tare da rike Amma dake shirin faduwa.
“Allah yasa kaddara ba musanya zata min ba, Allah yasa ba Hamad za a dauke a ba ni wani ba, La'ilaha Illallahu, Allah kasa kari zan samu ba musanya ko ragi ba, su wa suka dauke shi? Na san ďana be jin magana amman su yi hakuri dan Allah idan wani laifin yayi, kowa ya min haka be kyauta min ba, me suke so Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un”
Gwaggo ma sai da ta fashe da kuka saboda kukan da Amma take yi. Appa kuma yayi tsaye a gurin hopeless yana kallon tsohuwar matarsa dake dauke da cikinsa ya rasa me zai yi.
Littafin nan kudi ne biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660
________________
https://chat.whatsapp.com/F1ch00M9VNvFxrVVgCEeXo
Ina Yan uwan Yan gayu makotan Masu Kudi?
Daku nake Magana.
Matan da suka san ciyon kansu masu hada goma ta zamo ishirin kuzo ku sari Kaya acikin sauki da rahusa a Ummu Ahmad store muna kawo kayan mu ne daga Lagos masu quality da karancen farashi akwai kayan kitchen akwai shoes and bags, Akwai kayan abinci na awo laces,kayan yara,da sauransu
Sannan akwai kayan gyara irin su tsimi kala kala gumbar mata daban daban maganin sanyi
Akwai kaza me rubutu da wadda akeyi da sanyun magani
Akwai taimako na haihuwa ga wadda taje asibiti akace batada matsalar komai akwai rubutun da muke badawa Wanda idan ta gama Al adarta zatayi amfani dashi za adace da yardar Allah
Akwai kayan kamshin daki da na jiki
Location dinmu zamfara
Muna tura Kaya a koina kk cikin aminci da yardar Allah payment validate ur order Ummu Ahmad 08032350261
Ni Khadeeja Candy nake tabbatar muku ba zaku taba nadamar siyen kayan Little Mommy na ba, uwata ce ta jini ba lake lake ba, please patronize her tana siyar kaya masu kyau da imganci, zaku iya tuntubarta ko ma ku tuntube ni kai tsaye 💃 sai ku zo 🥰*HURIYYA*
*BOOK 2 PAGE 2*
𝐁𝐨𝐨𝐤 𝐓𝐰𝐨
𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲
Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660
𝐏𝐚𝐠𝐞 2️⃣
Sai da Gwaggo da Mama Rukayya suka yi da gaske sannan suka iya rarashin Amma ta yi shiru, suka dagata suka shigar da ita falon har lokacin Appa ya tsaye ya rasa abun cewa, Hurriya ma kuka take sosai tana tausayin kanenta tana tausayin mahaifiyarta.
“Dan Allah Gwaggo a kwantar mata da hankali, ba yau aka saba daukar mutane kuma ana dawowa da su lafiya, na san dai ba zai wuce su ce suna bukatar kudi ba, kuma ba mu biya mu karbo shi”
“Toh Allah ya bayyana shi cikin aminci”
Yasir yayi shiru sai a lokacin shi ma yake ganin abun da yayi na kai Hurriya a irin wannan lokacin be dace ba. Hajiya Kaltume ta fashe da kuka.
“Haba Alhaji wake da Iyami yanzu an dauke min yar shawalwalar yarinyar, mace ce fa, al kara ma Hamad namiji ne”
Appa ya tashi ya fice, Yasir ya bi bayansa, daga gidan station suka nufa daman kamin su isa Appa ya kira CP ya fada masa abun da ya faru, suna isa ya saka aka shigar da report kamin yan sanda da suke sashen kidnapping su tafi gidan aka kwaso duka yaran, ana tambayarsu yadda abun ya faru suna fada. Babban cikin su dake tambayar ya kalli Namra da ta kare nata bayanin ya ce.
“Wacece Hurriya? Ina ita Huriyyar take?”
“Tana gidansu”
“Okay ita ba yar'uwarku ba ce?”
Appa yayi gyaran murya dan ya san Namra zata iya wata kwabar.
“Yata ce, ni na haifeta amma yanzu tana gurin mahaifiyarta da ta koma gida haihuwa”
“To zamu iya ganin ita Huriyyar? Domin ga dukan alama ita aka zo dauka, ita da Ruma din a yadda na fahimta Hamad din tsautsayi ne ya rutsa da shi, rashin samun Hurriyya sai suka dauke Hamad din, dole akwai tambayoyin da nake son yi mata”
“Ni ma na yi wannan tunanin duba da irin labarin da suka ba ni, zan je na zo da ita”
Appa ya fada sannan ya kalli Yasir.
“Idan an gama ka maida su gida, ni zan je na taho da Huriyya”
“To Appa”
Yasir ya amsa cikin ladabi da biyayya, Appa ya ma Officer sallama ya fice. Tare da direbansa suka isa gidan Gwaggo, a waje suka faka motar direban ya fito ya bude masa mota ya fito. A ransa yana son shiga amman jin hake kamar ana tsikara masa allura a zuciya saboda ya doso gurin da Amma take.
“Bala, ka sallamo Hurriyya”
“Toh ranka ya dade”
Malam Bala ya wuce cikin gidan, Appa kuma ya jingina da mota, Malam Bala be dade ba ya dawo yana sanar masa Gwaggo tace ya shigo tana son magana da shi. Rasa yayi me zai ce, shi dai be isa ya juya yayi tafiyarsa ba, kuma yana jin kunyar hada ido da iyayenta ita kanta Amma a yanzu kunyarta yake ji. Haka dai ya daure ya danne duk wani abun azabar da yake ji ya shiga cikin gidan, sai da ya hada da addu'a sannan ya samu courage din shiga har cikin falon Gwaggo. Be zauna ba sai da ya risina ya gaishe da ita kamar yadda ya saba, ba dan ta girme shi ba, sai dai ma shi ya girme ta, yana bata girmata ne tun a lokacin da ta zama sukurukarsa a yanzu ma be yada girmanawarba, domin har a yanzu sun din suna da kima da daraja a idonsa.
“Hurriya ta shigo tana ta kuka, amman bata yi magana ba har yanzu ta kasa fadar abun da ya faru, a baki Rukayya muka ji cewar Yasir ne ya kawo ta ma, kuma da kayan makaranta ta shigo, babu gilashi a idonta, yanzu kuma sai ga Malam Bala ya shigo wai kana kiran Hurriya shiyasa na ce ya shigo da kai ciki mu ji abun da ya faru domin mu ma hankalinmu duk a tashe yake”
“Gwaggo, ni ma kaina ban san abun da ya faru ba. Shiyasa na kira Hurriyar na ji ta bakinta”
“Can gida ba su fada maka komai ba.?”
Appa ya ki yarda su hada ido.
“Ba su fada min ba, Hurriya tana kusa?”
“Eh tana dakin mahaifiyarta, bari a kirata”
Gwaggo ta tashi ta fita. Bata jima ba Iyami ta shigo falo tana sanye da digon Hijab har kasa Hurriya na rike da hannunta. Appa na kallonsa sai gashi ya mike tsaye yana kallon cikin dake jikinta cikin wani yanayi na rashin jindadi.
“Na fada maka babu uwar da zata so yayan wasu kamar nata, yanzu wannan tashin hankali duk na minene? Ba komawa gidanka nake bukata ba kwanciyar hankalin yayana kawai nake bukata a yanzu...”
“Iyami zauna”
Amma har ta yi kamar ta ce masa ba zata zauna ba, domin niyarta ta kawo Hurriya kuma ta jadda masa amanar yayanta ta koma, sai kuma ta zauna domin bata saba musa masa a komai ba. Sai da ta zauna sannan shi ma ya zauna.
“Ba wani abu aka yi mata ba, ki daina saka kishi da son cusa kiyayyar Kaltume ko Nafisa a zuciyar yayanki, ba dukan Hurriya aka yi ba, ba wata bakar magana aka fada mata ba, babu wanda ya mata komai, ba mutuwa aka yi ba”
“To miyasa ta zo tana min kuka? Kuma Yasir da ya kawo ta be shigo gidan ba ya fita?”
“Ni ma shi na zo tambayarta”
Amma ta kalli Hurriya har lokacin hawaye take sai dai ba kamar dazun ba. Ta kalli Appa
“Ina Hamad...!”
Appa ya ji tambayar kamar saukar aradu. Appa ya kalleta ya kasa cewa komai.
“Ina Hamad Appan Hurriya?”
“Dan Allah kin kwantar da hankalinki”
“Kamar ya na kwantar da hankalina? Miye abun tashin hankali a tambayar Hamad? Ko kuma shi ya aikata wani laifin?”
“be aikata laifin komai ba Wallahi, ki ba mu guri zamu yi magana da Hurriya”
Amma ta kalli Hurriya kamin ta mike tsaye ya fice daga falon. Appa ya tashi daga inda yake zaune ya koma kusa da Hurriya ya zauna ya rika yarsa.
“Hurriya”
“Na'am Appa”
“Ki kwantar da hankalinki kin ji, Hamad zai dawo soon da yardar Allah, babu abun da zai same shi, kuma na ji dadin da baki fadawa Iyami abun da ya faru ba, kin ga tana da ciki zata iya daga hankalinta,”
Ta daga kai ta kama hannun Appa ta jimke da karfi.
“Appa bana ganin komai yanzu, bana ganin komai sai abun da ya faru, me yasa suka dauke Hamad? Me yayi musu?”
“Wallahi dukanmu ba su sani ba, amman dai an san ba zai wuce su ce a ba su kudi ba, kamar yadda suka yi ma Kaltume kuma shi ma za su sako shi”
“Hadda Ruma aka kama”
“Na sani duka zamu biya kudi mu karbo su Da yardar Allah, amman yanzu zamu tafi dake gurin police za su miki tambayoyi akan abun da ya faru, saboda kun sanar da ya sanda, kamin nan kuma ina son ki min alkawarin ba zaki fadawa Iyami ba, kuma ki daina kukan nan har sai mun karbo shi”
Kamin Hurriyya ta dauki alkawarin suka jiyo Amma daga jikin curtains din kofar dakin tana furta.
“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un.
Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un
Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un”
Daga Appa har Hurriya ba su san Amma ta yi labe ba sai a lokacin. Appa ya taso ya fito da sauri yayinda Gwaggo ma ta fito da sauri daga dakin Amma ta nufota.
“Gwaggo sun dauke min Hamad, su biyu Allah ya ba ni sun dauke daya, kashe shi za su yi Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un”
Gwaggo ma ambaton Allah ta shiga yi tare da rike Amma dake shirin faduwa.
“Allah yasa kaddara ba musanya zata min ba, Allah yasa ba Hamad za a dauke a ba ni wani ba, La'ilaha Illallahu, Allah kasa kari zan samu ba musanya ko ragi ba, su wa suka dauke shi? Na san ďana be jin magana amman su yi hakuri dan Allah idan wani laifin yayi, kowa ya min haka be kyauta min ba, me suke so Innalillahi wa'inna Ilaihiraji'un”
Gwaggo ma sai da ta fashe da kuka saboda kukan da Amma take yi. Appa kuma yayi tsaye a gurin hopeless yana kallon tsohuwar matarsa dake dauke da cikinsa ya rasa me zai yi.
Littafin nan kudi ne biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660
________________
https://chat.whatsapp.com/F1ch00M9VNvFxrVVgCEeXo
Ina Yan uwan Yan gayu makotan Masu Kudi?
Daku nake Magana.
Matan da suka san ciyon kansu masu hada goma ta zamo ishirin kuzo ku sari Kaya acikin sauki da rahusa a Ummu Ahmad store muna kawo kayan mu ne daga Lagos masu quality da karancen farashi akwai kayan kitchen akwai shoes and bags, Akwai kayan abinci na awo laces,kayan yara,da sauransu
Sannan akwai kayan gyara irin su tsimi kala kala gumbar mata daban daban maganin sanyi
Akwai kaza me rubutu da wadda akeyi da sanyun magani
Akwai taimako na haihuwa ga wadda taje asibiti akace batada matsalar komai akwai rubutun da muke badawa Wanda idan ta gama Al adarta zatayi amfani dashi za adace da yardar Allah
Akwai kayan kamshin daki da na jiki
Location dinmu zamfara
Muna tura Kaya a koina kk cikin aminci da yardar Allah payment validate ur order Ummu Ahmad 08032350261
Ni Khadeeja Candy nake tabbatar muku ba zaku taba nadamar siyen kayan Little Mommy na ba, uwata ce ta jini ba lake lake ba, please patronize her tana siyar kaya masu kyau da imganci, zaku iya tuntubarta ko ma ku tuntube ni kai tsaye 💃 sai ku zo 🥰*HURIYYA*
*BOOK 2 PAGE 2*
𝐁𝐨𝐨𝐤 𝐓𝐰𝐨
𝐀𝐫𝐞𝐰𝐚𝐛𝐨𝐨𝐤𝐬 @𝐤𝐡𝐚𝐝𝐞𝐞𝐣𝐚𝐜𝐚𝐧𝐝𝐲
Littafin nan na kudi ne biya ki karanta cikin aminci pay 500 to 2451879008 Hadiza Abubakar Zenith Bank, then send the evidence to 08036126660
𝐏𝐚𝐠𝐞 2️⃣
Sai da Gwaggo da Mama Rukayya suka yi da gaske sannan suka iya rarashin Amma ta yi shiru, suka dagata suka shigar da ita falon har lokacin Appa ya tsaye ya rasa abun cewa, Hurriya ma kuka take sosai tana tausayin kanenta tana tausayin mahaifiyarta.
“Dan Allah Gwaggo a kwantar mata da hankali, ba yau aka saba daukar mutane kuma ana dawowa da su lafiya, na san dai ba zai wuce su ce suna bukatar kudi ba, kuma ba mu biya mu karbo shi”
“Toh Allah ya bayyana shi cikin aminci”