← Book details Hurriya Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 64 OF 133

Sashe 64

Hurriya Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

“Waya siya miki”

“Ni dai ka ba ni zan yi amfani da daya”

“Wallahi ba duba tun a lokacin da aka taba fasa miki gialshin na bincika ko'ina ban ganshi ba, ban san ya aka yi ya bata ba”

“Yaya ka sake dubawa idan ka gani ka ba ni”

“Okay”

“Toh, Yaya yau ka je gurin Mama Rukayya? Ko zaka je?”

Ya watsa mata wata kalar harara.

“Hurriya yaushe na fara wasa da ke?”

Ta fice da sauri tana dariya, a yanzu kam ta tabbatar Yayanta yana son kanwar mahaifiyarta, idan haka kuma ya kasance zata fi kowa farincikin domin dukansu tana sonsu. Bangaren Momy ta dawo ta shiga dakinta ta yi wanka sannan ta saka kayan bachi ta yi addu'a ta yi karatun suratul milk sannan ta kwanta.

Ina masu fama da ciwon dajin? Ciwon hanta? Ulcer? Hawan jini da Ciwo sashe, Ciwo sugar da ciwon mara, Ciwo sanyi kai har da ciwon HIV. Ina masu fama da Ciwon da aka kasa gane kansa, ina masu fama da matsalar Jinnu? Ina matan da sai an yi maganar aure abu yayi shiru? Ina matan dake neman mazajen aure? Ina masu neman tsarin jikinsu? To fa nesa ta zo kusa cibiyar MALAM MAITAWAKKALI ta zo musu da mafita da yardar Allah. Duk wata cuta da aka kasa gane kanta, ko kuma ciwon da yake damun mutum a jiki ko wane iri ne za ku samu warakarsa da yardar Allah. Muna bada maganin ne ta hanyar da addinin musulunci ya yarda da shi babu bokanci ko tsibbo a ciki. Kuma muna bada maganinmu ne cikin sauki da rahusa, mun saukaka kamar kyauta na goro kawai za ku bada, biya kuma sai bukata ta biya, burinmu dai shi ne samun lafiyarku da kuma biyan bukatarku.

Mazauni cibiyar na nan a Kwantagora Local Government, hanyar farin ruwa kusa da dan gandu rice. Za ku iya tuntubar mu ta wannan line 08135421882 ko kuma 08061663326. Zaku iya kira ko chat, wani abun burgewa kuma shi ne za mu iya aika muku da maganinmu a duk garin da kuke ba dole sai kun zo ba. Ku dai ku kira ko kuma ku tuntube mu ta Whatsapp. Sai kun zo... 💃🏻
[11/30, 9:45 PM] AMINA KABIR CAPS: *KHADIJA CANDY*

*3️⃣0️⃣*

HAJIYA KALTUME POV.

Kai ta daga sama tana karewa dakin kallo wanda ya kasance na kasa ne ko'ina sai kulli kullin yawu da aka sarkafa, sai mayan allunan karfe da madubai ga kuma ruwa a kasko da karya ga kwalabe ta ko'ina kana shiga gurin zaka fahimci wane irin mutum ne, balle kuma hancin mutum yayi arba da gawurtaccen kamshi turaren aljannu dake tashi har wani juyin kai yake sakawa. Cikin hikima Hajiya Kaltume ta jinjina kai tana jin dadi, ganin take kamar ciwonta ya warke ma gaba daya. Yana shigowa cikin dakin ta gyara zamanta ta matsa baya tana kallonsa.

“Malam an shigo”

Ya zauna yana fadin.

“Da dai zaki kirani da Dan masani, ko na gangare zai fi Hajiya”

“Toh dan masani, sannu da kokari”

“Yauwa sannu dai Hajiya”

“Ya gidan ya iyali da komai”

“Komai lafiya kalau, Hajiya”

Ta dauko katon madubi ya dora a cinyarsa.

“Daman... ”

Zata fara bayani ya daga mata hannu, ya dangwalo yawun bakinsa yayi rubutu da shi, sannan ya kalleta ya girgiza kai ya maida idonsa a gurin madubin, ya fi karfin minti ashirin a haka sannan ya dago ya kalleta ya ce.

“Kanwar Kulu ta kawo ki nan ko?”

“Eh haka ne, can gidansu na fara zuwa sannan aka kawo ni nan”

“Na gani ai, kuma kin zo nan ne saboda mijinki zai kara aure, gashi kuma ya canja miki, ga danki yana son auren yar kishiyarki da ta fita, kuma kina fargabar kar ciwon da kika aika mata ya karya ta tashi mijinki ya ce zai dawo da ita, sannan kina yawan faduwa har ki ji ciwo a kafa har kika tsoron ko an miki ture ne”

Ta daga masa kai.

“Hakkun babu musu a maganarka take”

Yayi dariya.

“An fada mana komai ai”

“Haka nake so, yanzu so nake a hana ďana auren yar iskar yarinyar, kuma a hana mijina aure, sannan a dauke hankalinsa daga gurin kowa sai ni, idan da hali ma wannan matar da take tare da shi abokiyar zamana ita ma a koreta, sannan bana son mijina ya dawo da Iyami, kuma ciwon kafar nan ba turo min aka yi? Ni har tsoron faduwar nake ji kar naje na fada a inda be kamata ba kafar ta cire ko ta karye na shiga uku”

“Duk za'ayi Hajiya, amman sai kin daure kuma kin shirya domin ni bana aiki da wasa, ciwon kafarki kuma babu wani ture babu aljannu babu komai, daga Allah ne”

“Toh Alhamdulillah yanzu hankali ya dan kwanta, kuma daman ni ai haka nake so, yanzu miye abun yi?”

Ya aje madubin dake jikinsa gefe daya ya dubeta.

“Ina mai tabbatar miki da wani abu, tabbas mijinki zai dawo da abokiyar zamanki da kike tsoron ya dawo da ita, matukar baki tashi tsaye ba”

Hajiya Kaltume ta dora hannu a kai tana jin wani karin tashin hankali na kusantota.

“Shiyasa na zo gurinka ai, dan Allah a hana ya maido da ita”

“Za'a iya hakan ne kadai idan zaki iya daukar nauyin jini, amman muddin matar nan tana raye babu makawa sai ta dawo gidanki”

“Dan masani me kake nufi kenan?”

“Ni matsala ta bana boyo kuma duk abun da na gani ina fadawa mutum gaskiya, amman ina aiki na gaskiya, abun da ya fi kawai mu yi ma matar nan halbin kasko domin matukar tana raye Wallahi ina mai tabbatar miki mijinki sai ya sake zaman aure da ita”

“Dan masani babu wata hanyar sai kisa? Kar abun yayi min yawa?”

Yayi dariya.

“Ashe baki shirya kenan kika zo, baki shirya mallakar mijinki ba, kuma baki shirya hana kishiyarki dawawa ba, gaskiya ban ga wata mafita a nan ba bayan wannan, domin madubin nan baya kara kuma ya nuna min akwai sauran zama a tsakaninsu”

Hajiya Kaltume ta yi shiru na wasu dakiku sannan ta sauke ajiyar zuciya ta ce.

“To maganar mallakar Alhaji fa? Da kuma hana dana aure”

“Za a yi miki na mallaka zaki mallake Alhaji ki koma kamar uwarsa, karki damu da wannan amman fa zaki zuba kudi”

“Kamar nawa Malam?”

“A kalla za a kashe 50k”

Ta yi murmushi 50k abu ne mai sauki idan dai zata samu biyan bukata.

“50k ma matsala ba ne, zan bada fiye da haka ma, amman a duba idan akwai wani aiki mai sauki da ba sai kisa ba sai ayi”

“Bari kiji na fada miki, matar nan ma tana nan ta fara tashi domin wanda kika saka yayi miki aikin nan ya fara karya aikin, tabbas kuwa zata dawo cikin gidanki, kuma dawowarta yana nufin fitarki”

“Innalillahi Wa'inna Ilaihiraji'un, fita ta kuma? Ai ni shi ne tashin hankalina, ta zauna ma ya na kare balle ita tana ciki ni ina waje?”

Gaba daya sai hankalinta ya tashi ta ji wani gumi na keto mata.

“Amman kana ganin idan an aikata aikin zai yiyu?”

“Me zai hana? Saboda hasarin halbin kasko idan be sameta zai iya fadawa akan jininta shakiki kamar danta ko yarta”

Hajiya Kaltume ta taba hannu biyu.

“Shikenan ma daman yarta ta isheni a duniyar nan, a aikata mata kawai ka ga aikata mata zai saka su ji tsoro su hana Yasir Rukayya, kuma zan huta nima hankali ya kwanta, amman ina lafiya idan aka ce zata dawo kuma ni na fita”

“Idan aka yi haka babu ita babu mijinki har abada”

“Toh yanzu yaushe za'ayi aikin”

“A yanzu ma idan kika bada kudi, sai a dauko kayan hadi a kira aljannu, cikin dare za'ayi halbi kin ga ruwan da yake cikin kaskoncan? A cikinsa za a halba idan aka gabatar da aiki aka yi halbi da dare kamin safe sako ya isar mata, amman fa tabbas idan be sameta ba zai fada akan yarta balle ma ita muke fatan ya samu”

“Akan samu irin haka ne, ayi ma mutum aiki kuma ya zama be fada kansa ba?”

“Ban taba samun irin haka ba, gaskiya wani lokacin ma akan fada ma mutum biyu da uwa da jininta, kawai ina tabbatar miki karfin aikin ne”

“Zan biya kudin, zan bada 200k gaba daya, ina son a hana dana aure kuma a janyo hankalin mijina a gareni sannan kuma a hana shi aure wacan yarinyar da yake hasashen aure a yi musu farraqu”

Dan masani na jin 200k ya ji ransa yayi wasai kudin wata gona da wani gidan kauye har da fili ma.

“Hajiya ni ko ina tabbatar miki, kuma na miki alkawari tsakanin yau zuwa gobe zaki tashi da labari mai dadi akan kishiyarki, na mallaka kuma akwai aikin da zan hana sai ki aiko ko kuma ki zo da kanki jibi ki karba, da zarar ya ci an gama da shi, a game da auren da zai kara kuma wannan ni an san aikin da zan yi, mai irin sunan yarinyar ma ba zai sake sha'awa ba”

Hajiya Kaltume ta yi murmushi ya jinjina kai

“Haka nake so, so nake na mallake komai a gidan nan, ya zama be ganin kowa sai ni da Yayana, Hurriya ma ina son a cire masa ita a rai kwatakwata”

Ta saka hannunta a jaka ta dauko 200k ta aje masa.

“Idan bukata ta biya zan baka ninkin wannan, ni dai burina ayi aiki yayi”

“Aiki kam ya gama, tashi ki yi tafiyarki”

“Na Gode dan masani”
Chapter 64 · 0% Book details