← Book details Hamdah Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 28 OF 34

Sashe 28

Hamdah Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sai kuma yayi shiru batare da yaci gaba da Maganar ba.
ita ko zaman ta tagyara sosai wannan karon ita ta mai da tafin hannun sa cikin nata tasar kafe yatsun su guri guda, kana ta sanya idanun ta cikin nashi, cikin daÉ—a karfafa shi da bashi kwarin guiwar gama fidda damuwar da take ganin tamkar ta yaye masa, tagyaÉ—a masa kai cike da bashi kwarin guiwar yaci gaba da da fidda damuwar da take yi masa kallon cuta ce barin sa a ransa.
A hankali kuwa yaci gaba da maganar yayin da ya daÉ—a sarkafe hannun nasu sosai,
ya ce "Kawa kin san me naji?, wani abun mamaki naji wan da ban san mene ne shi ba,
bayan da yarin yar ta É—auke su ta tafi da su,
sai na tsinci kai na cikin wani irin yanayi mai ka ma da da muwa,
mai kama da son in sake ganin su, amma nafi alakanta son in sake ganin yaran ne,
bayan kwana biyu sai naji tunanin nawa yanata rikiÉ—a, madadin tunanin yaran su biyu sai ya dawo uku, zuwa lokacin na gama fihimtar har da ita yarin yar nake son sake gani.
nayi mamakin kai na matuka,
wata rana dana fita muka kuma haÉ—uwa da su a kan hanya ta ta zuwa mittin,
a tunani na ganin da nayi musu wannan rana shike nan zuciya ta zata huta da tunanin abun da bai shafe ta ba, amma ina bayan rabuwar mu da su sai naji tamkar kara min ake.
Bayan wasu kwana biyun sai nasa ayi min bincike a kan su wato ita da yaran dana ke yi musu kallon kannen ta ne,
nayi mamaki matuka lokacin da labarin su ya iso min, dajin waÉ—an nan yara nata ne ma ana ita ta haife su.
mamaki na shi ne ganin ta kara ma sosai, nasamu cikakken labarin su, da duk kanin bayanan tarihin rayuwar su..."
shiru yayi tare da jan numfashi ya sauke, sannan ya ce
"Labarin su mai cike da ban tausayi na girgiza da jin lamarin, sai dai a yanzu su ba abin tausayi bane, dan Ubangiji ya zartar da ikon sa gare su..."

A hankali yashiga bata labarin su kamar yan da aka kawo mishi cikakken tarihin su, bai ɓoye ko rage mata komai ba kamar yadda baiyi da farko ba, bayan gama shaida masa abin da aka sanar masa a kan su sai ya cigaba da faɗin
"Kin san wace ce wannan yarin yar?."
kai ta girgiza jiki a sanyaye yayin da idanun ta suka cika da ƙwalla tap suna shirin zubowa.
taji bala in tausayin su da jin labarin su jikin ta yayi matukar sanyi.
ya ce "I ta ce mai Company *HAM'NAS*."
ido ta waro ta ce "Mai Company *HAM'NAS* mai *HAM'NAS* Nigeria Limited?."
"Kwarai kuwa ita ce."
kai ta jinjina tare da faÉ—in
"Allah mai iko wan nan shine sakayyar da mafificin rahama yayi mata sakamakon cin jarabawar da ya É—aura mata tabbas labarin rayuwar ta abun a tausaya ne, a da yanzu kam Allah yayi mata sauyi da mafificin rahamar sa."
sai gata tana hawaye cikin matsanancin tausayin labarin rayuwar HAMDAH da taji, har da jan sheshshe ka.
ta kai hannun ta share hawayen ta tare da faÉ—in
"Allah kayi mana mai kyau kasa mu dace duniya da kiyama."
ya ce "Amin." sai ya saki hannun ta yakoma ya kwamta tare da lumshe idanun sa.
a sannu ta gyara ita ma sai ta kwanta gefen sa tare da yin pillow da damtsen hannun sa, a hankali takai hannun ta kan fuskar sa, a sannu tashiga shafa gefen fuskar sa, in da kayataccen saje ke kwance a gurin lub-lub gwanin ban sha'awa.
duban sa tayi da kyau cikin kulawa a hankali ta ce
"Aboki." idanun sa da suke lumshe yaÉ—an buÉ—e su a kanta sannan ya amsa da
"Na'am." in da ya am sa can cikin kasan mako shin sa, laɓɓan sa ne suka motsa tanan ta fahinci ya amsa kiran nata.
idanun ta cikin nashi, sannan tace
"Aboki bayan sanin labarin ta kuma sai me baka karasa bani labarin ba."
idanun sa ya lumshi cikin son kawar da zancen ya ce
"Wani labarin kuma ai na gama baki labarin."
murmushi tayi tare da faÉ—in
"Baka kara sa ba da saura dan acikin duk kanin labarin da ka bani baka bani asalin gundarin labarin ba, kawai dai ka ce min kana
jin wani abu a kanta mene ne shi?."
"Ba ko mai fa." yafaÉ—a a takaice yana gyara kwanciyar sa, tare da juya wa ya fuskanci jikin garu, yana faÉ—in
"Zanyi bacci ki tai maka min kisa yayi daÉ—i."
hannun ta ta cusa karkashin gashin kansa ta bayan keyar sa, yana jin haka da sauri ya juyo dan yasan jan masa sumar zatayi da karfi bawai tayi masa yan da zaiyi baccin ba.
dariya tayi tana faÉ—in
"Ai da baka juyo ba Aboki yau aski zan maka."
ido yaÉ—an waro ya ce "Aski da hannu."
farr tayi da ido ta ce "Zan nimo abin yin askin ai taɓawa nake naji ta in da zan fara."
ya ce "FaÉ—i gaskiya dai Æ´ar guntun muguntar ce ta motsa."
dariya takuma in da shi kuma ya murmusa yana kokarin mai da idanun sa ya lumshi tayi saurin dakatar da shi ta hanyar faÉ—in
"Me zaka ɓoye min ne iye sai fa ka karasa bani labarin nan dan baka gama bani ba."
shiru yayi bai ce komai ba,
Murmushi tayi tare da faÉ—in
"To ni bazan karasa baka labarin, tun da yau ka aro hijabi ka sakata sakanin mu, zan yaye ta yanzu dan babu ita sakanin mu har gaba da abadan."
É—an numfashi ta ja tare da cigaba da faÉ—in
"Tun da ka sanya ido kanta Ubangiji yayi ikon sa,ya datsa maka sonta, a lokacin da baka taɓa sammanin a kwai ranar da hakan zata kasan ce da kai ba, dan kai a tunanin ka ni kaɗai ce Ubangiji ya dasa maka sona cikin zuciyar ka, babu wata macen da zata kuma samin gurbi cikin zuciyar ka,
ka mance da cewa Allah shi ne sarkin mulki mai yin yadda yaso da bayin sa, nasan ka da son yara amma son da kake yiwa waÉ—an nan yaran na daban ne, kana yi musu irin son da uba yake yi wa Æ´aÆ´an sa, haka ne ko?."
tayi magaran tana duban sa da murmushi sosai kan fuskar ta.
numfashi ya sauke kana ya janyo ta jikin sa sannan ya ce
"Haka ne." ya faɗa dan babu ɓoye-ɓoye ko karya sakanin su, ko yan zu ma dayayi kokarin yin hakan sabo da wani dalilin yasha wuya sosai da fama da abun cikin zuciyar sa.
wani yelwataccen murmushi ne ya baiyana kan fuskar ta, kana ta ce
"Kana son ta?." kai ya gyaÉ—a alamar Eh sannan ya ce
"Amma abar maganar domin bana jin zan iya haÉ—a ki da wata."
gyemun sa taja, sai kuma ta ɓata fuska sannan tace "Haka Allah ya ce, bana son ka canza daga halin dana sanka baya yi maka kyau,
dama kan haka kake masaltawa zuciyar ka aje damuwar da bata saba ba, shine har kake son ka koyi karya ko?,
kana son ta, tun daga farkon labarin ta naji nima ina son ta ina son ƴaƴan ta, ita ta musamman ce yarin ya karama mai halin man ya ba kasafai ake samun irin su a duniya ba, ni ma ina son ta, zan ku ci gaba da son duk wani abun da kake so har idan bai saɓawa Shari'a ba har karshen rayuwa ta zan cigaba da son sa."
mike wa zaune yayi ya lankwashe kafafun sa kana ya dubi ta da É—in bin farin ciki da jin daÉ—in kasan cewar ta cikin rayuwar sa ya ce
"Haki ka babu wan da yakai ni dace da samun mace ta gari, da ace kowani na miji irin ki ya samo a matsayin mata shi da damuwa ko tashin hankali bazai gansa ba har karshen rayuwa, Allah yayi miki albarka matar aljanna, faran tamin da kike Allah kema ya faran ta miki fara Æ´ar duma-duma ta."
"Ameen Ameen ameeeeeen."
tafaÉ—a tana jan É—an gyemun sa irin na gayun nan.
sai kuma da sauri ta saki gyemun ta ce
"Ka faÉ—a mata kana son ta kuwa?."
kai ya girgiza ya ce "Ban faÉ—a mata ba."
ta ce "To me ya sa?." ya ce "Sabo da baza ta amince ba."
"Kamar ya, zakace bazata amin ce ba, baka tin kare ta da batun ba ka bata laifi." tayi maganar tana rike haɓa.
kuma tun ta yaja kana ya ce
"Um to tana da masifa tsiwar tsiya ce da ita."
dariya tayi sosai tare da tafa hannu ta ce
"Masifa haÉ—e da tsiwa kuma, a'a kada kayi wa kanwa ta fin tsayi." shiko murmushi yayi yana faÉ—in
"Allah idan ta fara tsiwa sai kin sha mamaki."
dariyar ta kuma ta ce
"Zata amin ce kai dai je ka latsa ta kuma ka gani in sha Allahu zata amin ce, wata mace ce zataki tayin ka duk haÉ—uwar ta da dukiyar ta kuwa,
ai mijin nawa da farin jinin sa aka halitto sa, shiyasa ma har gida ake kawo masa hari, wannan bazawarar taka ma jiya ta zo."
dariya duk kanin su suka fashe da shi, zillo tayi gefe ganin yami ko hannu yana kokarin ruko ta, tasan sarai baya so tari yi masa maganar ire-iren waÉ—an nan matan da suke kawo masa hari.
janyo ta yayi jikin sa ya rungume yana faÉ—in
"Zakiyi baya ni." dariyar take tana daÉ—a shige wa cikin jikin sa.
Kissing yashiga ai ka mata yana faÉ—in.
"Hakika nayi dace da mace ta gari Æ´ar uwa ta jini kawa kuma abokiyar shawara,
tabbas duk wan da yasa mi mata kamar ki yagama more yaruwar sa har gaba da abadan,
ke matar aljanna ce insha Allahu da yar dar Allah zamu shiga aljanna ni da ke da kafafun mu."
Baki ta turo gaba ta ce
"To HAMDAH fa?."
ya ce "To har da ita." mumushi tayi tare da daÉ—a rungume shi ta ce
"In sha Allahu kuwa Allah ya tabbatar mana."
ya am sa da amee. nan suka shiga nuna wa junan su tsantsar kauna da soyayya in da zancen ya sauya suka lula duniyar ma'aurata...
Chapter 28 · 0% Book details