← Book details Hamdah Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 27 OF 34

Sashe 27

Hamdah Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Da sauri yamike zaune tare da janyo ta jikin sa yana faÉ—in
"Ke meya kawo wannan maganar?, banace kada nasake jin wannan maganar a bakin ki ba?,meye na yin ta meya kawo ta yanzu kuma?,
Okay so kike ki kawar da farin cikin da ke nan ko?,
hauhuwa dama ashe mutum shi yake bawa kansa haihuwa?, okay kin mance cewa Allah shi yake bai wa bayin sa haihuwa?, so kike kiyi tsaɓo to kiyi gaggawan tuba, maza yanzu."
yayi maganar yana share mata hawaye.
kana yaci gaba da faɗin "Dai na kunan kada na sake jin wannan maganar a bakin ki, kada na sake ji idan kuma so kike ki koyi yan da zaki rika ɓata min rai to ki kara yin ta,
na ce miki ina son haihuwa Allah bai nufa na samu bane, idan yaso sai ya bamu bare ma muna da su Æ´aÆ´an da muke yi musu hidima kama daga gidan marayu makarantu da dai sauran su suÉ—in ba namu bane, suma Æ´aÆ´an mu ne, mai da hawayen kinji Fara Æ´ar duma-duma ta." "
kai ta shiga girgiza wa tana faÉ—in
"Nayi shiru bazan sake ba ka yafe min."
kai ya jinjina kana ya koma yajin gina bayan sa da jikin gado, ita ko zaman ta tagyara suna fuskantar juna ya ce
"Ko ke fa fara Æ´ar duma-duma ta to na yafe."
dariya tayi kana taɗan langwaɓar da kanta cikin muryar shagwaɓa a hankali ta ce
"Na yar da ba abun da na faɗa yanzu ke damin ka ba amma na tabbata akwai wani abun, zuciya ta baza ta sami sukuni ba har idan ban za mo silar kawar da damuwar ka ba, amma babu damuwa tun da ka nuna baka so na sani, yau rana ta farko daka taɓa ɓoye min damuwar ka, ban taɓa tunanin akwai ranar da zata zo ka ɓoye min damuwar ka ba, damuwar ka tawa ce kamar yan da yake tawa takace,
ai ban san cewa haka yanzu ka É—auke ni ba shike nan babu damuwa."
tayi maganar tana kokarin sauka a gadon.
dakatar da ita yayi ta hanyar rike hannun ta kana yaÉ—an ja numfashi sannan ya ce
"Abar shi kawai faÉ—ar shi ma bashi da wani amfani."
ido ta kura masa sannan tace
"Haka kace abar shi yaci gaba da damun ka da cin ka a rai ko?, kada ka mance nafi kowa sanin ko kai waye tun sati biyu da suka wuce na fara fahimtar akwai wani abun da ke damun ka, ban daÉ—a gaskata hakan ba sai yau da ka shigo gida, rungumar ka da nayi jikin ka da zuciyar ka suka tabbatar min da haka, dakuma tabbacin damuwar naka yakaru a yau,
tanbayar ka danayi É—azu da zaka tafi masallaci yakuma bani amsar abun da nake zargi, babu halin da zaka shiga koda dai-dai na second 1 ne ban gane shiba."

Ganin yan da ta hakikan ce tanuna damuwar ta matuka a kanshi takuma nuna ɓacin ranta nakin faɗa mata da yayi wan da ada ba haka asakanin su.
sai ya janyo ta jikin sa ya rungume,
tabbas ita wata sashi ce a rayuwar sa da bazai iya ɓoye mata komai na rayuwar sa ba, kamar yan da tun fari suka gina rayuwar su ta hanyar faɗawa junan su sirrukan su,
bata ɓoye masa komai kamar yan da shima baya ɓoye mata, ko a yanzu dayake ta kokarin barin abun cikin zuciyarsa shi kaɗai yana ta shan fama da ɗawai niya da zuciyar sa dan bai saba ba sam.
numfashi ya ja kana a hankali yasoma magana
"Akwai wani abun da ke damu na amma sam banso na fitar ba naso nayi jarumtar iya barin sa a raina dan faÉ—ar sa sam bashi da amfani."
wani numfashi yakuma saukewa kana a hankali ya cigaba da magana
"Kiyi hakuri da abun da naketa ɓoye shi a zuciya ta ni kaɗai, wan da nagaza iya dan neshi sabo da ban saba da irin saba, yabani wuya sosai a zuciya ta, kiyi hakuri yanzu da zakiji shi a kan laɓɓana, tabbas da gaske bazan iya ɓoye miki sirri na ba kokarin yin haka dana yi kuwa dan cigaba da ganin kwanciyar hankalin ki yabani wuya sosai a zuciya,
nayi ta kokarin danni shi cikin zuciya ta hakan ya garara gashi bugun farko kin gano da akwai abun da yake dami na."
hannun ta ya damke cikin nasa kana yaja numfashi ya sauke sannan yaci gaba da faÉ—in
"Wata ranar da Company na ya tura kayan bukata izuwa wata makarantar yara, kamar da yan da kika sani a ka saba,
lokacin da motar Company ya isa aka shai da min da isar sa, sai na tashi da kai na naje makarantar domin ganewa ido na kalar farin cikin da yara zasuyi kan kayan da aka kai musu wan da yawan ci kayakin wasa ne irin na yara,sai sabbin kujeru, dan nima naji daÉ—i, duk da kuwa makarantar bana Gwamnati bane, makaranta ne ma irin na Æ´aÆ´an masu kuÉ—i,
lokacin da na shiga makarantar nayi arba da wasu yara guda biyu, sunata wasanni da kayakin wasan da aka kai musu, duk da yara dayawa agurin amma nafi ganin farin cikin waÉ—an nan yara guda biyun sosai cikin matukar farin ciki da kuma jin daÉ—i suke ta wasa da kayan da motar Company na ta sauke,
naji daÉ—i matuka ganin farin ciki a fuska da zukatan É—aliban, amma sai dai hankali na yafi karkata kan farin cikin da ke baiyana ga waÉ—an nan yara guda biyu,
kasan cewar lokacin tashi yayi nan É—alibai suka fara watsewa, wasu diraibobin su suka zo suka kwashe su wasu kuma motar makaranta ta kaisu, haka yara sukayi ta watsewa.
ina nan a cikin makarantar muna magana da shugaban makarantar bayan mun gama maganar na fito, lokacin tuni students sun watse, a bakin get na tadda waÉ—an nan yara guda biyun, da lokacin da na shigo makarantar su na fara ganin su da É—in bin farin ciki kan fuskokinsu, tare da mai gadin makarantar suna zaune a bakin get.
ko da na iso gurin su kan su na shafa tare da duban mai ganin na ce,
yaya su ba'a zo É—aukar su bane kokuma motar makaranta zasu bi kuma naga É—alibai duk sun watse.
mai gadin ya ce
Ba motar makaranta zasubi ba direban su ne zai zo ya É—auke su ko mai akayi dai yanzu yana hanya, yau an É—an makara ne wajen zuwa É—au kar su.
kan su na daÉ—a shafawa sai nayi waje cike da jin sha'awar yaran, ina fita kuwa sai suka biyo ni a baya, sai na tsaya naruko hannun su ina tanbayar su yaya sunan su,
kai yaya sunan ka nafara tambayar na mijin sai yace min sunan sa Naseem, ita kuma macen tace min sunan ta Nasmah,
nafahimci wayo sosai tattare da yaran duk da kuwa ƙarancin shekarun su, dan bazasu wuce shekaru uku zuwa uku da rabi ba,
bayan nayi musu tambayar sai suma suka mai da min tambayar.
to kai ma yaya sunan ka, wayon yaran ya burge ni sosai jin yan da suma suka iya mai da min tambayar,
Sai nace musu sunana Daddy, kin san wani irin yanayi nagani a tare da su lokacin da nace musu suna na Daddy?."

Dan sakai ta maganar yayi tare da daÉ—a matse hannun ta cikin nasa kana yaci gaba da faÉ—in
"Ihun murna suka sake haÉ—e da tsalle suka rungume ni suna faÉ—in laa kai Daddy ne irin Daddy'n su Aeeman,É—in class É—in mu, to kai Daddy'n su waye ne?, maganar yaran yasa Ni shiga wani yanayi, sai dai farin cikin danake hango wa tare da su da kuma fahimtar da nayi kalmar sunan Daddy dana furta musu yazo mu su a sabon abu ko makamancin haka,
Sai na ce musu Daddy'n ku.
kin san me yaran sukayi?."
nan ma hannun ta yakuma damke wa cikin nashi kana yaci gaba da faÉ—in.
"Da É—a rungume ni sukayi suna ta tsallen murna da nanata kalmar sunan Daddy,
wani irin abu naji acikin jiki na da zuciya ta, a duk san da suka furta kalmar Daddy a gare ni, sai naji wani irin farin ciki da jin daÉ—i mara misaltuwa a gare ni, cikin kan kanin lokaci naji yaran sun shige cikin zuciya ta,
har nake ji tamkar Æ´aÆ´an da na haifa ne a gaba na suke kira na da wannan suna,
abun da na daÉ—a lura da yaran a lokacin sosai na ke hango jin daÉ—i irin na samun sabon abu a tare da mutum, sai suka ce min
Daddy kai ma zaka bamu chocolate irin wan da Daddy'n Aeeman yake bashi. na ce musu kwarai kuwa, to lokacin akwai ragowar Chocolate a mota wan da nake baiwa yara a gidan marayu idan naje,
sai na ruko hannun su nace muje na basu chocolate yana mota ma kuwa.
lokacin da muka nufi gun mota, a dai-dai lokacin wata yarin ya ta iso gurin a cikin mota."
Chapter 27 · 0% Book details