← Book details Hamdah Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 14 OF 34

Sashe 14

Hamdah Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Yau Monday da misalin karfe 7 narako su Nasmah har sai da naga tashin su kafin na koma ciki, ina gama abun da zanyi nawuce side É—in su Bappa, ina shiga bayan mun gaisa Bappa yake cemin
"Dama yanzu nake da shirin niman ki, kan ai kin masallacin nan ne harfa an rigada an gama shi, wan da aka bashi kwangilar jiya yake sanar min da cewa an gama."
da murmushi sosai kan fuskata nace
"Kai masha Allah kai amma dai ai kin yamin sauri wlh."
Bappa yayi murmushi tare da faÉ—in
"In dai da kuɗi a kasa komai cikin sauki yake zuwa, in dai da kuɗi ai komai mai sauki ne Allah dai yaba da ikon cin jarabawar da yayi dan shi kanshi arziki babban jarabawa ne, yakan kai mutum wuta yakan kaishi aljanna, kuɗi kamar takwabi yake idan kayi jahadi da shi shigar aljanna mai sauki ne idan ka ai kata ɓarna da shi shiga wuta mai sauki ne, Allah yasa mudace."
Amin Amin. duk muka amsa da shi
cikin washe baki nace
"Bappa masallacin nan fa nagina ne saboda Inna duk ladar arika kai mata kabarin ta, shima asibitin da yanzu ake gina shi idan a ka gama komai kyauta za'a rika yi duk ladar arika kai mata cikin kabarin ta".
"Masha Allah masha Allah".
abun da Bappa da Inna wuro suka rika faÉ—a kena.
Bappa yace "Ubangiji Allah ya tabbatar mana da hakan Allah yajikanta da rahama ya kai mata dukkanin ladan kabarin ta ya kyautata namu bayan nasu, kai sannu HAMDAH kinyi tunani kwarai da gaske Allah ya saka miki da mafificin rahama."
Amin. nace ina mai jin sanyi da daÉ—in addu'ar da yake min.

Muna nan zaune a parlour ban ankara ba sai gani nayi karfe 12 har da É—ori,
wayata na É—aga da sauri ina faÉ—in
"Ikon Allah lallai guri babu wuya dubi 12 har ta gota an yama Yakubu yadawo kuwa bari dai na kirashi naji."
nayi maganar ina laluɓo lambar sa, wayar tayi ta ring bai ɗaga ba, nakira yakai sau biyar bai ɗaga ba, na sauke wayar ina faɗin
"Oh to ya ajiye wayar a ina ne shi ga lokacin É—auko su Nasmah daga School yayi, gashi nayi ta kiransa bai É—aga wayar ba."
Bappa yace "Ko ina ya aje wayar to shi, ina yaje haka ayi ta kirashin baya É—aga wa".
nace "Wlh É—azu ne na ai keshi gidan Hajiya Firdausi matar ministar Bukar, akwai wasu kayan da tayi min tallar su wan da tayi odar su daga jamani, to sun yi min na tura da kuÉ—in to É—azu take faÉ—a min direban ta baya nan ko zan turo nawa direban ya amso min, shine na tura shi to gashi har yanzu bai dawo ba nayi ta kiran shi ma bai É—auka ba".
nayi maganar ina kuma É—aga wayar nakuma niman lambar sa.
Hajiya Firdausi matar ministan Abuja ne,
na yar da idan Allah yayi maka rufin asiri babu irin mutanen da bazaka gani ba ka kuma yi tarayya da suba,
ire-iren irin waÉ—an nan matan manya muna hulÉ—a da su sosai wasu sun girme min nesa ba kusa ba, wasu ma sun haife ni sun juya amma haka muke cuÉ—an ya da su.

Mikewa nayi da sauri ganin na kuma kiran sa har sau biyu nan ma bai É—aga ba, nace "Bappa bari naje kawai na É—auko su har yanzu bai É—aga wayar ba, kar suyi ta jira kasan mutumin ka yanzu haka yana kan musu rigimar zai dawo gida".
Bappa yace "Maza hanzarta kam ga guri nata kan tafiya".
da sauri nafita ina shiga side É—ina mayafi kawai na yafa dan dama a kimtse nake na É—au É—aya daga cikin makullen mota da suke cikin drower, da sauri na sauka na nufi parking space.
kana nashiga motar nayi wa motar key, tun kafin na karaso bakin get maigadi ya wangale min get yana fadin "Adawo lafiya".

Saboda yanayin gosulo na bata lokaci sosai a hanya dan har karfe É—aya ta cika har ta É—an gota, kafin nan na isa makarantar su.
tun kafin nakaraso get É—in makarantar, na zubawa kofar makarantar ido sosai dan ganin wasu yara rike a hannun wani mutum "Kamar su".
nafaÉ—a a file, nayi saurin isowa gurin, da mamaki nazuba musu ido ganin suÉ—en ne, yana rike da su suko sai washe baki suke,
shikuma mutumin yana ta tafiya da su yana nufar wata mota dake fake taÉ—an can gefe da get É—in makarantar, yayin da yake ta girgiza kai alamun yana jin surutun da suke ta zuba masa.
cikin hanzari na isa gefe nafaka cike da mamakin ganin nufar motar yake gadan-gadan na ɓalle marfin mota na fita da sauri, cikin hanzari nasoma bin bayansu ina faɗin
"Kai Naseem Nasmah!, malam ina zaka kaisu kuzo nan ku wuce mutafi".
mutumin bai juya ba sai su yaran ne suka juyo sai kuma suka kawar da kansu suka juya suka cigaba da tafiya suna cigaba da zuba masa surutu.
da sauri nasha gaban su gani yan da suka batsar kamar basu sanni ba nace
"Kai ina muku magana kuna jina ina zakuje kuwuce mutafi malam ina zaka kaisu?".
sai sannan mutumin yaÉ—an dukar da kansa dai-dai tsawon su kana yasoma magana
"Kunsan ta ne?." batare da yaÉ—ago ko ya dube ni ba ya ce "Ke a ina kika sannu bamu hanya mu wuce."
ido na waro cike da mamaki jin abun da yafaÉ—a tare da mamaita kalmar nasa
"Nasan su? nasan su fa kace, da alla malam ka sake su ina magana kana cigaba da tafiya da su."
gefe na ya gota batare da yace komai ba ya karasa jikin motar nima da sauri na rufa musu baya ina cigaba da faÉ—in
"Kai malam ina tambayar ka ina zaka kai su wai kana tambaya ta nasan su ne, ni zaka tambaye ni nasan sune, tambaya ta kake nasan su? dalla kasake min yara muwuce,ina ne zaka dasu kake nufar cikin mota da su?,
idan baka sake suba yanzu-yanzu zan kira maka hukuma anan."
baiyi magana ba sai mika hannun sa yayi yabuÉ—e marfin motar, yaÉ—au ko kwalin chocolate yaciro chocolate guda huÉ—u yabawa Nasmah biyu ya baiwa Naseem biyu kana yace
"To ga tsarabar ku kuci wannan yanzu, wannan kuma sai kusa a aljuhu."
yafaÉ—a yana cusa musu wani chocolate É—in cikin aljuhun wandon su.
da mamaki nake kallon su ganin yan da sukayi tamkar basu sanni ba, sai murna da tsalle suke suna faÉ—in
"Ye am bamu da yawa ye am bamu da yawa."
cikin takaici nakai hannu zan fisge chocolate É—in, da sauri mutumin ya janye su gefe kana yaÉ—ago kansa tare da zuba idanun sa cikin nawa,
wani irin dirrr naji a cikin jikina tamkar jan wutan lantar ki.......!

Mommyn Twins ce

6

Yan da idanun sa yasarkafu cikin nawa haka babu zato ko sammani shi yasani shiga yanayin,
sai kuma na gyara tsayuwa ta da kyau, wani kallo yake bina da shi daga sama har kasa kana yace
"Na ɗauka kafin kiran hukuma ihu zaki yi ta yi kitara jama'a kice ga ɓarawo yazo satar yara, ke ba'a yi miki ihu ba har ke zaki wa wani ihu? karfe nawa ne yanzu wai wannan lokacin ne lokacin zuwa ɗaukar yara a makaranta,abar yara can kowa ya watse sai su kaɗai a cikin makaranta, sabo da baki san abun da kike yi ba an turaki ɗaukar su kin tsaya kin ɓata lokaci a hanya kina damuwar ki wata kila ma kinbi gidan kawayen ki kin gama sharholiyar ki,
kafin nan kika zo wai ke a hakan kinzo É—aukar su a makaranta, karfe nawa yanzu?. karfe nawa ne yanzu?!".
yakuma nanata tambayar, yana maganar ne ida nunsa a kaina da kuma alamun jaddada tambayon da yake jefa min,
gashi dai maganar cikin faɗa yake yin sa amma lamɓansa a hankali suke motsawa.
dogone yana da faffaÉ—ar kirji da zubin kakkarfan maza, fuskarsa na É—auke da É—an siririn saje wan da ya zagaye fuskar nasa har zuwa É—an gemun sa da bai wuce rabin kamu ba, irin gemun da gayu suke bare.
baza a kirasa da fari soll ba sanna kuma ba baki bane, hasken sa dai-dai.
kwantaccen gashin kansa baki sitif yasha gyara mai tsamtsi da tsulɓi sai wani yal-yal yake, sabo da iskar dake kaɗawa.

Kaina nakawar gefe tare da murguÉ—a baki nashi a wanne zai zauna yana wani masifa to ina ruwan shi ne ma.
É—an rutsunawa yayi yarage tsawon sa dai-dai tsawon yaran kana ya dubi ko wannen su yace
"Idan kunje gida kuce wa Mommyn ku kada a sake turo Aunty ku ta É—auko a School a rika ai ko me wayo yarika É—auko ku, wan da bazai barku kuyi ta shan wahala a nan ba, kunji ko?."
kai suka gyaÉ—a suna ta faman shan chocolate "Yauwa to kuje gida sai gobe zan kawo muku wani chocolate É—in, kada ku man ta in kunje gida kufaÉ—a wa Mommy kada a kuma turo wannan Aunty'n naku É—aukar ku a School a aiko mai wayo."
yayi maganar yana yi musu alama da suje in da nake yana binsu da murmushi,
ido na waro cikin masifa nabuÉ—i baki zanyi magana, dai-dai lokacin mota ta faka gefen mu, da mugun gudu, Yakubu direba yafito da sauri ya iso in da muka yana faÉ—in
"Ranki shi daÉ—e Hajiya wlh gosulo ne yatsare ni tun É—azu babu ta yan da zanbi na koma da baya na canza wata hanyar, gaba da baya motoci suka sani a tsakiya,jibi kumatu na har mari nasha dana nimi in juya dan na canza hanya, Hajiya a gafarce ni, wlh gosulo ne, ita kuma wayar sam na mance jiya da zankwanta bacci nacire ta a kara yau har gari yawaye kuma ban mai da kararta ba, Hajiya ayi hakuri da Allah."
maganar yake tamkar zai zuba guiwowin sa a kasa yana tafa bayan hannun sa a cikin É—aya tafin hannunsa alamun roko,
banyi magana sai juya wa nayi nanufi gun motar dana zo da ita, dan wannan mutumin yakure ɓata min rai.
Chapter 14 · 0% Book details