← Book details Furar Danƙo Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 80 OF 90

Sashe 80

Furar Danƙo Part 2 Complete Hausa Novel · about 4 min read

        An ɗauki Dada babu alamar rai a tattare da ita ga jini na zuwa ta inda gilashin kofi ya jimata ciwo. Shi kansa Baba Garko a kiɗime yake dan bata taɓa kasancewa a irin hakan ba duk wannan rikicin da akeyi. Iyaka dai ta suma da'an zuba mata ruwa ta farfaɗo. Amma yau babu abinda basu gwada mata ba ko motsi. Da tab.. ɗin ya fita a hannunsa, dan yasan koma mi ya sakata a wannan halin bazai kasance ƙaramin ba.
      Cikin ƙanƙanin lokaci labari ya isa kunnen ƴaƴanta da jikoki. Kafin wani lokaci asibitin da aka kaita ya cika da Garko family, zuri'ar Uncle Khamil dake Abuja ne kawai babu suma suna tafe sai na auta dake a Saudiyya. Har zuwa washe gari ba'a samu kan Dada ba, dan haka hankalin kowa ke'a tashe. Hatta shi uban gayyar a wannan karon hankalin nasa a tashe yake. Dan koba komai fa yana son matarsa, sannan itace uwar ƴaƴansa. Tun shekarun ƙuruciya suke tare har zuwa tsufa da daɗi babu daɗi tana zaune da shi. Washe gari zuwa sha ɗaya na safe auta ya iso tare da nasa iyalinsa, tamkar shi Dada ke jira ya iso ta farfaɗo, sai dai fa numfashin farko da taja ta fesar da jini ta fesoshi. Wani sabon tashin hankalin kenan, dan likitocin ma sun kasa musu bayani, sai kai-kawo da shigi da fici sukeyi. Duk wanda suka tunkara sai dai ya zame da faɗin yana zuwa. Duk wannan abun da akeyi babu Alh. Sulaiman sai ƴaƴansa da uwar gidan sa. Karan farko da Tajuddeen yaji baƙin cikin halin mahaifin nasa. Shin wai minene na wannan gabar, a ganinsa mahaifiya ai tafi gaban wasa. Dada na a irin wannan yanayin har yace yanada wata hujjar cigaba dayin gaba. Duk wanda yaga Dada a jiya zuwa yau dolene ya tausaya mata. Shi kansa Baba Garko ya ajiye makaman yaƙinsa harda hawaye yake da sambatun ta tashi dan ALLAH kada ta tafi ta barsa. Cikin ɓacin rai Tajuddeen ya dannama ubansa kira. A lokacin yana ɓoyayyen Companyn sa suna tattaunawa da yaransa malami da wasu abokan cinikayyarsa mazauna Legos akan kayansu da suka iso Nigeria a daren jiya. Sai dai sun rasa yanda zasu fidda kayan daga bakin ruwa saboda kamar fa an saka musu ido... Yana ɗaga wayar Tajuddeen ya fashe masa da kuka cikin masifa yake faɗa masa “Yanzu nan Dad har kanada lokacin nishaɗi haka mahaifiyarka kwance ranta a hannun ALLAH tana aman jini likitoci tun daren jiya tsaye a kanta. Anya kuwa kana fatan gamawa da duniya lafiya Dad. Ace iyayenka ne abokan gabarka. In dai dan ni kakeyi toka ajiye dan nikam dai na haƙura da Mawaddat koda ace sonta zai zamar min ajalina. Duk ƴan uwanka gasu nan har wanda basa ƙasar kai kaɗai ne ka fita zakka a cikinsu saboda son zuciya. Idan ta mutu sai kazo zaman gaisuwa ai” ya faɗa yana yanke kiran wani irin kuka mai cin rai na kufce masa...

*_★UK★_*

    .....A dalilin wayar Tajuddeen da mahaifinsa su Lulu suka san halin da ake ciki. Domin suna tsaka da ganin zaman meeting ɗin Alh. Sulaiman da abokansa ta direct camara ɗin su. Hankalin Lulu ya tashi matuƙa, dan koma minene ya faru Dada ba abar yardawarta bace ba. Kuka ta fara cikin tashin hankali ta shiga neman layin ƴan uwa. Da kyar ta samu Uncle Amin ya ɗaga. Cikin kuka take faɗin yanzu nan Dada na'a irin wannan halin amma babu wanda ya faɗa mata. Lallashinta Uncle Amin ɗin ya farayi akan ta kwantar da hankalinta tai mata addu'a daga inda take. Amma ina Lulu taƙi saurarensa. Shima Smart ɗin ta matuƙar tayar masa da hankali, dole ya saya mata ticket dan bazai juri ganinta a haka ba. Sai dai ita kaɗai zata taho banda AA. Ta barsa wajen Iya Tabawa da aunty Bilkisu da har yanzu bata kammala ganin likita ba duk da tana a gida lokaci-lokaci dai take zuwa ana dubata asibitin........✍️

_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_

*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*

FURAR DANKO
Billyn Abdul

-ZAFIN KAI
Mamuhgee

-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at👇

1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇

09032345899

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

Zafafa🫶🔥

*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

  🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗

           𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 5️⃣8️⃣
Chapter 80 · 0% Book details