Sashe 29
Furar Danƙo Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Yau ma kamar kullum gidan yana ruɗe da hayaniyar yara da jikoki kasancewar juma'a ce ta ƙarshen wata. Dan an sakko massalacin kenan sai ga Abdull ya shigo yana sanarma Ammah Abbah yace a bada ruwa anyi baƙi. Kasancewar itace da girki babu wanda ya damu. Ta haɗa ruwa harda zoɓon da Maryam tayi domin zuwan Ahmad ɗinta kasancewar duk juma'a yake zuwa hira bayan sallar la'asar (Kun san fa Ahmad da Maryam an jone🥱). Har Abdull zai wuce Ammah ta sake dakatar da shi, dan tunda taga Abbah ya aiko a amshi ruwa da alama baƙin masu muhimmanci ne. Masar da tayi matsayin abincin rana ta zuba ta ce Asma'u ta ɗauka ta bisa da shi.
Sosai Uncle Yousuf ya tsirama Asma'u da ta kai har ƙasa tana gaishesu idanu, dan sosai tana kama da Smart, sai dai kawai dan shi namiji ne ita mace, ta kuma fishi haske sosai. Murmushi yayi domin tuna wani abu. Daddy na lure da shi sai dai baice komai ba har Asma'un ta fita. Mikewa Abba yay da nufin barinsu suci abinci, amma sai Daddy ya ce yayi zamansa ai ruwama kawai ya wadar. Ɓata rai Abba yay da faɗin, “Saboda abincin namu ba irin naku bane Alhaji Isma'il?”.
Cikin ɗan daburcewa Daddy yace, “Wlhy ba haka bane Malam Mika'il. Amma aimana afuwa bara muci.” dariya suka ɗanyi cikin barkwanci, da ga haka suka shiga buɗe abincin, ganin masa tasha manshanu ga lafiyayyen zoɓo bama su san sanda suka shiga cin ba har sai da suka tada abincin tas. Daddy na tsokanar Uncle Yousuf ne ya cinye, shima yana tsokanarsa shine ya cinye. Shi dai Abba dariya yake musu cike da sha'awar wannan zuminci tamkar wasu abokai. Bayan sun kammala Uncle Yousuf yace ya kamata Ammah tazo dan suji miya kawosu a tare. Abbah ya jinjina kansa cikin gamsuwa, sannan ya ɗaga waya yay kiran Ammah. Cikin ƙanƙanin lokaci kuwa sai gata, tayi mamakin ganin ashe baƙin su Uncle Yousuf ne, amma sai batace komai ba ta zauna suka gaisa cikin girmama juna. Uncle Yousuf ya zaro hotuna a aljihunsa ya miƙama Abbah. Amsa yay yana murmushi, sai dai yana kallon jinjirin dake a hoto sai da zuciyarsa ta harba. Dan haka ya ɗago da sauri ya na duban Ammah data tsira masa ido, sai kuma ya dubi su Daddyn da ke kallonsa da murmushi. Itama dai Ammah gabanta ne ya faɗi lokacin da taga abinda ke jikin hoton, muryarta na rawa ta ɗago tana kallon Abbah. Abban Salim wannan ai Hydar ne yana jinjiri, sai dai ban san sanda aka ɗauki hoton ba gaskiya, dan kayama na manta da su.”
Daddy da ya kasa riƙe dariyarsa ne yay gyaran murya, dan haka suka dubeshi su duka har Uncle Yousuf dake danne tasa dariyar shima. Daddy ya ce, “Anya Aliyu ne? Kudai sake kallon hoton Malam Mika'il”.
Kallon juna Ammah da Abba suka sake yi, sai kuma suka sake maida hankalinsu a hotunan. Abba ne ya sake cewa, “Gaskiya Aliy ne a hotunan nan Alhaji Isma'il. Ba mu da muka haifesa ba ma, duk wanda zaka tambaya in har yasan Aliy yana jariri wannan amsar zai baka”. Ammah dake jinjina kai tace, “Wannan gaskiya ne Abban Salim. Dan Hydar ne yana jariri”.
“Wannan jinin Aliyu Hydar ne a yau ba Aliyu yana jinjiri ba”. Cewar Uncle Yousuf cikin murmushi. Cikin haɗa baki Abbah da Ammah sukace, “Jinin Aliyu! Tayaya?”.
“Ta hanyar matarsa Baba. ALLAH ya albarkaci matar Aliyu da haihuwa jiya, wannan shine albarkar da ALLAH ya azurtamu da ita mu da ku da shi”.
A hankali hawaye suka ziraroma Ammah da jikinta har yake tsuma. Muryarta na rawa ta ce,.......✍️
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 2️⃣3️⃣
.........*_CANADA_*
Kwanaki Uku kenan da mata cs ɗin, amma Alhamdullah da alamun fara samun lafiya tattare da ita kasancewar bata da ƙan jiki, sai dai kuma Lulu akwai raki. Mahaifiyar Usman da yake kira da Mamy tazo tana tare da su tun shekaran jiya. Hakan yasa take sake ƙara samun kulawa ita da jinjirinta. Ga Ummita na iya ƙoƙarinta itama tako wane fanni. Hakama Usman da Dr Lameer. Tayi mamaki matuƙa da ganin ɗunbin kayan baby da Mamy ta kawoma Aliyu ƙarami. Sai dai yanda matar ke kulawa da su cikin haba-haba ya sa Lulu kasa cewa komai akan hakan. Duk da wannan gata da kulawar da take samu wajen abokan arziƙi zuciyarta a cinkushe take da rashin ahalinta ko guda ɗaya a kusa da ita. Hatta shi kansa uban tafiyar yakan zo mata a rai, duk da a duk sanda yazo ɗin takan yamutse fuskar cikin nuna halin ko'in kula. Sai dai hakan babu alamar zai turesa a ran nata, dan data dubi ɗan jaririn nata zuciyarta kan harba mata, balle kuma idan tana shayar da shi takan zuba masa idanu da tafiya cikin tunani mai zurfin gaske akan al'amarin mahaifinsa. Kasancewar Mamy babbar mace ta jima da hango halin da Lulun ke a ciki, amma bata cewa komai saboda lokacin cewar bai isa ba...
A ranar da su Lulu ke cika kwanaki biyar da zuwan baƙon duniya su Abba da Daddy suka iso ƙasar Canada, tafiyar da tai masifar tada hankalin su Ummah dan Abba yace musu zasuje duba Smart ne zuwa ƙasar England. Jidali iya jidali rasar su Aunty Amarya sun gani wajen Ummah, dan su Asma'u ma basa gidan Ammah catai su tafi gidan yayunsu har sai sun dawo su dawo. Dan haka suka tafi gidan Aunty Bilkisu da shirin idan suka mata kwana biyu sai su koma gidan Hawwah itama su mata kwana biyu. Babu irin zagin da Ammah bata sha ba ranar har maƙwafta sai da suka shigo, inda mutane da yawa suka fara fassara al'amarin Umman da hassada. Dan sukam basu ga wani abin tada jijiyar wuya a nan ɗin ba...
Oho su Ammah ma basu san tana yi ba, dan suna can a hanya hankalinsu kwance. Ƙasar England su Abba suka fara yada zango wajen Smart. Wanda zuwan nasu yazo masa a bazata sosai, dan sam Uncle Yousuf bai sanar masa ba. Tsabar farin ciki baima san lokacin da ya rungume Ammah ba. Turesa tai cikin jin nauyi da faɗin, “Kajimin ja'irin yaro abinda ka koya a ƙasar turawan kenan kuma?”. Cikin dariya da shagwaɓa Smart ya ce, “Ammah nafayi missing ɗinki ne, ALLAH sai nake ganin kamar mafarki nakeyi”. Tsinguli ta kai masa da faɗin, “Bari na tabbatar maka idonka biyu”.
“Ouch!” ya faɗa cikin turɓune fuska yana kallon Abba a marairaice. Abba ya riƙo masa hannu yana hararar Ammah. Daddy da Uncle Yousuf dai dariya sukeyi, dan basu taɓa zaton Aliyun taɓararre bane a wajen iyayen nasa sai yau. Smart ya gaishe da Daddy cikin girmamawa, Uncle Yousuf kam ai baida maraba da aboki duk da yanzu ana ƴar kunyar surukuta kaɗan-kaɗan. Sosai mazaunin Smart ɗin ya ƙayatar da su Ammah, suka shiga godiya ga UBANGIJI a zukatansu da mamakin wannan rahama ta UBANGIJI. Sunci sun sha daga abincin da Smart ya tanada musu a cikin ƙanƙanin lokaci, dan abinci ne na ƴan Nigeria. Bayan kowa yaci ya ƙoshi suka ɗan tattauna, sosai zaman ya sanyaya ran Smart, inda ya fahimci surukinsa sosai a yanzu ya kuma sakko daga fushin daya tafi. Sun tafi zuwa masauki aka bar masa Ammah da Abbah nan. Hakan ya musu daɗi su duka, dan sun sami damar tattauna abinda ya shafesu sosai shi da iyayen nasa. Inda ya ƙara warware musu cigaban da ya samu da wanda yake fatan samu anan gaba. Ƴan uwansa kaf bai manta da kowa ba sai da ya tambaya, har maƙwafta da abokan arziƙi. Ranar dai ansha hira, dan duk rashin yawan maganar Ammah da Smart yau dai sun sha hira abinsu kamar suyita kasancewa a haka suke ji...
Sosai Uncle Yousuf ya tsirama Asma'u da ta kai har ƙasa tana gaishesu idanu, dan sosai tana kama da Smart, sai dai kawai dan shi namiji ne ita mace, ta kuma fishi haske sosai. Murmushi yayi domin tuna wani abu. Daddy na lure da shi sai dai baice komai ba har Asma'un ta fita. Mikewa Abba yay da nufin barinsu suci abinci, amma sai Daddy ya ce yayi zamansa ai ruwama kawai ya wadar. Ɓata rai Abba yay da faɗin, “Saboda abincin namu ba irin naku bane Alhaji Isma'il?”.
Cikin ɗan daburcewa Daddy yace, “Wlhy ba haka bane Malam Mika'il. Amma aimana afuwa bara muci.” dariya suka ɗanyi cikin barkwanci, da ga haka suka shiga buɗe abincin, ganin masa tasha manshanu ga lafiyayyen zoɓo bama su san sanda suka shiga cin ba har sai da suka tada abincin tas. Daddy na tsokanar Uncle Yousuf ne ya cinye, shima yana tsokanarsa shine ya cinye. Shi dai Abba dariya yake musu cike da sha'awar wannan zuminci tamkar wasu abokai. Bayan sun kammala Uncle Yousuf yace ya kamata Ammah tazo dan suji miya kawosu a tare. Abbah ya jinjina kansa cikin gamsuwa, sannan ya ɗaga waya yay kiran Ammah. Cikin ƙanƙanin lokaci kuwa sai gata, tayi mamakin ganin ashe baƙin su Uncle Yousuf ne, amma sai batace komai ba ta zauna suka gaisa cikin girmama juna. Uncle Yousuf ya zaro hotuna a aljihunsa ya miƙama Abbah. Amsa yay yana murmushi, sai dai yana kallon jinjirin dake a hoto sai da zuciyarsa ta harba. Dan haka ya ɗago da sauri ya na duban Ammah data tsira masa ido, sai kuma ya dubi su Daddyn da ke kallonsa da murmushi. Itama dai Ammah gabanta ne ya faɗi lokacin da taga abinda ke jikin hoton, muryarta na rawa ta ɗago tana kallon Abbah. Abban Salim wannan ai Hydar ne yana jinjiri, sai dai ban san sanda aka ɗauki hoton ba gaskiya, dan kayama na manta da su.”
Daddy da ya kasa riƙe dariyarsa ne yay gyaran murya, dan haka suka dubeshi su duka har Uncle Yousuf dake danne tasa dariyar shima. Daddy ya ce, “Anya Aliyu ne? Kudai sake kallon hoton Malam Mika'il”.
Kallon juna Ammah da Abba suka sake yi, sai kuma suka sake maida hankalinsu a hotunan. Abba ne ya sake cewa, “Gaskiya Aliy ne a hotunan nan Alhaji Isma'il. Ba mu da muka haifesa ba ma, duk wanda zaka tambaya in har yasan Aliy yana jariri wannan amsar zai baka”. Ammah dake jinjina kai tace, “Wannan gaskiya ne Abban Salim. Dan Hydar ne yana jariri”.
“Wannan jinin Aliyu Hydar ne a yau ba Aliyu yana jinjiri ba”. Cewar Uncle Yousuf cikin murmushi. Cikin haɗa baki Abbah da Ammah sukace, “Jinin Aliyu! Tayaya?”.
“Ta hanyar matarsa Baba. ALLAH ya albarkaci matar Aliyu da haihuwa jiya, wannan shine albarkar da ALLAH ya azurtamu da ita mu da ku da shi”.
A hankali hawaye suka ziraroma Ammah da jikinta har yake tsuma. Muryarta na rawa ta ce,.......✍️
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 2️⃣3️⃣
.........*_CANADA_*
Kwanaki Uku kenan da mata cs ɗin, amma Alhamdullah da alamun fara samun lafiya tattare da ita kasancewar bata da ƙan jiki, sai dai kuma Lulu akwai raki. Mahaifiyar Usman da yake kira da Mamy tazo tana tare da su tun shekaran jiya. Hakan yasa take sake ƙara samun kulawa ita da jinjirinta. Ga Ummita na iya ƙoƙarinta itama tako wane fanni. Hakama Usman da Dr Lameer. Tayi mamaki matuƙa da ganin ɗunbin kayan baby da Mamy ta kawoma Aliyu ƙarami. Sai dai yanda matar ke kulawa da su cikin haba-haba ya sa Lulu kasa cewa komai akan hakan. Duk da wannan gata da kulawar da take samu wajen abokan arziƙi zuciyarta a cinkushe take da rashin ahalinta ko guda ɗaya a kusa da ita. Hatta shi kansa uban tafiyar yakan zo mata a rai, duk da a duk sanda yazo ɗin takan yamutse fuskar cikin nuna halin ko'in kula. Sai dai hakan babu alamar zai turesa a ran nata, dan data dubi ɗan jaririn nata zuciyarta kan harba mata, balle kuma idan tana shayar da shi takan zuba masa idanu da tafiya cikin tunani mai zurfin gaske akan al'amarin mahaifinsa. Kasancewar Mamy babbar mace ta jima da hango halin da Lulun ke a ciki, amma bata cewa komai saboda lokacin cewar bai isa ba...
A ranar da su Lulu ke cika kwanaki biyar da zuwan baƙon duniya su Abba da Daddy suka iso ƙasar Canada, tafiyar da tai masifar tada hankalin su Ummah dan Abba yace musu zasuje duba Smart ne zuwa ƙasar England. Jidali iya jidali rasar su Aunty Amarya sun gani wajen Ummah, dan su Asma'u ma basa gidan Ammah catai su tafi gidan yayunsu har sai sun dawo su dawo. Dan haka suka tafi gidan Aunty Bilkisu da shirin idan suka mata kwana biyu sai su koma gidan Hawwah itama su mata kwana biyu. Babu irin zagin da Ammah bata sha ba ranar har maƙwafta sai da suka shigo, inda mutane da yawa suka fara fassara al'amarin Umman da hassada. Dan sukam basu ga wani abin tada jijiyar wuya a nan ɗin ba...
Oho su Ammah ma basu san tana yi ba, dan suna can a hanya hankalinsu kwance. Ƙasar England su Abba suka fara yada zango wajen Smart. Wanda zuwan nasu yazo masa a bazata sosai, dan sam Uncle Yousuf bai sanar masa ba. Tsabar farin ciki baima san lokacin da ya rungume Ammah ba. Turesa tai cikin jin nauyi da faɗin, “Kajimin ja'irin yaro abinda ka koya a ƙasar turawan kenan kuma?”. Cikin dariya da shagwaɓa Smart ya ce, “Ammah nafayi missing ɗinki ne, ALLAH sai nake ganin kamar mafarki nakeyi”. Tsinguli ta kai masa da faɗin, “Bari na tabbatar maka idonka biyu”.
“Ouch!” ya faɗa cikin turɓune fuska yana kallon Abba a marairaice. Abba ya riƙo masa hannu yana hararar Ammah. Daddy da Uncle Yousuf dai dariya sukeyi, dan basu taɓa zaton Aliyun taɓararre bane a wajen iyayen nasa sai yau. Smart ya gaishe da Daddy cikin girmamawa, Uncle Yousuf kam ai baida maraba da aboki duk da yanzu ana ƴar kunyar surukuta kaɗan-kaɗan. Sosai mazaunin Smart ɗin ya ƙayatar da su Ammah, suka shiga godiya ga UBANGIJI a zukatansu da mamakin wannan rahama ta UBANGIJI. Sunci sun sha daga abincin da Smart ya tanada musu a cikin ƙanƙanin lokaci, dan abinci ne na ƴan Nigeria. Bayan kowa yaci ya ƙoshi suka ɗan tattauna, sosai zaman ya sanyaya ran Smart, inda ya fahimci surukinsa sosai a yanzu ya kuma sakko daga fushin daya tafi. Sun tafi zuwa masauki aka bar masa Ammah da Abbah nan. Hakan ya musu daɗi su duka, dan sun sami damar tattauna abinda ya shafesu sosai shi da iyayen nasa. Inda ya ƙara warware musu cigaban da ya samu da wanda yake fatan samu anan gaba. Ƴan uwansa kaf bai manta da kowa ba sai da ya tambaya, har maƙwafta da abokan arziƙi. Ranar dai ansha hira, dan duk rashin yawan maganar Ammah da Smart yau dai sun sha hira abinsu kamar suyita kasancewa a haka suke ji...