← Book details Furar Danƙo Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 52 OF 90

Sashe 52

Furar Danƙo Part 2 Complete Hausa Novel · about 6 min read

       Washe gari kamar yanda ta saba da wuri tai shirin fita. Dan ma tana ta fama da AA da ya maƙale mata yau shagwaɓa yake ji, sai da Ummita ta shigo ne ta ansar mata shi ta samu ta ƙarasa gyarawa tana faɗin, “Yaro zaka gane kuranka yayeka zanyi ai a cikin watannan”.
           Cikin waro idanu waje Ummita ta ce, “Kai aunty wasa kike amma dan ALLAH?”.
     “Oh wasa ko zakuga wasa”.
“Kai aunty wata tara fa, baima cika cif-cif ba. Banda ma yanada kirinki da zafin nama ai bai kai a fita a barsa ba”.
        “Uhm Ummita kanku fa akeji, wlhy jira kawai nake ya taka na yayesa. Tunda yana cin abincinsa ba wani ya damu da nonon bane sosai ai gara na hutar da kaina ko.”
    “Mudai aunty kiyi haƙuri to ko shekara ɗaya mu cika dan ALLAH mun tuba”.
             “Ummita kenan, wai baki tausayina ne ma dai ko. Da wanne zan ji?”.
      “Aunty damu mana, ai mune farko kafin komai. Dan kulawar mu da ta Abbienmu itace farko”.
     Shiru Lulu tai bata sake cewa komai ba. Dan a duk sanda Ummita zata ambaci Abbien AA ɗin takanji zuciyarta na mata nauyi, shiyyasa bata sakewa hirar tai nisa a kansa take basarwa. Ficewa tai a ɗakin tana faɗin, “Bari na duba Daddy zanyi breakfast a wajensa ki yi maza ki shirya kin san munada aiki yau”.
        Cikin girmawa Ummitan ta amsa mata da to tare da Binta da kallo tausayi. Sosai ma'aurata ke matuƙar bata tausayi, bata taɓa ji ko labarin irin aurensun nan ba. Auren kusan shekara ɗaya da fin rabi kaɗan babu a biyu amma zaman wata ɗaya cikakken ba'a samu ba, dan ma UBANGIJI mai hikima da ya saƙa zare mai girma na azurtasu da ɗa. Tana ma kanta addu'a, amma gaskiya Lulu na ɗaya daga cikin manyan addu'ointa a kowacce rana. Fatanta ALLAH ya kawo iyakar komai ta koma wajen mijinta da ayanzu duniya ke faɗa da saurara a fanin ƙwallon ƙafa. Ita tasan duk da Lulun bata nunawa tanada damuwa sosai. Dan tasha kamata tana kallon AA kallo mai harshen damo kasancewar sa tamkar photo copy na mahaifinsa. Sannan shi kansa yaron soyayyar da take nuna masa mai kallo yasan ba tashi bace shi kaɗai harda ta Abbien nasa........✍️

_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_

*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*

FURAR DANKO
Billyn Abdul

-ZAFIN KAI
Mamuhgee

-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at👇

1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇

09032345899

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

Zafafa🫶🔥

*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

  🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗

           𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 4️⃣0️⃣

.......Ƙaramar dariya yayi da ɗage gira sama ya ce, “Nima naga alama ƴar ƙanwata babu abinda ta sani sai cin abinci da barci”. Ya ƙare maganar da lakace mata hanci.
Hannunsa ta buge da sake yunƙurin tashi tana faɗin, “ALLAH dai ya shiryaka kai kam”.
Sakin nata yay yana dariya da tashi zaune shima cike da shaƙiyanci.
            “Miye na dariyar to”.
       “A'a babu komai ƴar ƙararrama, ai ko cikin AA ma a ruwan madara kika sha ni shaida ne.”
   “Kaji da shi dai. Fitinanne”.
“Kema zaki zama fitinanniyar”.
“ALLAH ya tasreni wlhy”.
   “Sai dai na gaba wannan dai ya faru tunda ga AA a duniya”.
          Da sauri ta miƙe cikin ɗage kai tana faɗin, “Oh kama tunamin, yaron nan zai iya tashi ya ce zai sakko wlhy”.
     Miƙewar yay shima da cewa, “Yi zamanki ina zuwa, bari na duba shi.” bata Musa masa ba ta koma ta zauna. Sai dai har ya gama haye ɗan steps ɗin hanyar bedroom ɗin nasa tana binsa da kallo, sai da ya shige ta sauke nannauyar ajiyar zuciya da lumshe idanu tana sakin wani ɗan murmushi mai sanyi. Babu jimawa sai gashi ya dawo ɗauke da AA kuwa a hannu, sai zillewa yaron yake da ɓata fuska irin na ƙiwa, shi adole bai sanshi ba. Yana ganin Lulu ya wani zabura wajenta yana ɓare baki. Dole ta amshesa dan ya cika mata kunne, yana ganinsa a hannuta sai yay shiru yana kallon Smart da sauke ajiyar zuciya. Zaune Smart ya kai kusa da Lulu cikin damuwa da ɗan murmushi, ya zubama yaron idanu da faɗin, “Kayi fushi da Papa ko Sweet heart? Kayi haƙuri Papa yayi laifi da baizo ya ganka ba tsahon lokaci. Please ka daina min ƙiwa kaji my sweet friend ɗina”. Ya ƙare maganar yana ɗan lakacema yaron hanci. Da sauri AA ya sake lafewa jikin Mamansa ya zata ɗaukar yasa zai sake yi.
Murmushi ya sake saki da girgiza kansa kaɗan. Sai kuma ya dubi Lulu dake saurarensu da kallo kawai. “Yana cin abinci ne?”.
        Cikin ɗan ɗage kafaɗa da taɓe baki tana kallon yaron ta ce, “Da ga Kunu sai tea kawai yake sha, sai biscuits haka da ɗan sweets suma wani lokacin ko an bashi bai sha”.
     “In dai ya biyo Babansa kam bazai sha ba, dan bana shan zaƙi nikam. Bari na haɗa masa tea ɗin maybe yunwa ce ta tashesa”. Kai kawai ta iya gyaɗa masa. Har ga ALLAH wannan halayyar tashi na saka mata ganin girmansa da kimarsa. A haka idan ka dubesa sai ka ɗaukesa a wani mutum mai jin kai da girman kai, amma sai ka zauna da shi kaga baida damuwa akwai sauƙin kai. Babu jimawa ya dawo da cup ɗin tea, zama yay a gabansu yana fuskantarsu, ya ɗan ɗebi tea ɗin a spoon ya kai bakin AA. A mamakinsu sai sukaga yaron ya ɗan kallesa kamar zai yi kuka sai kuma ya amsa. Dariya suka sanya su duka. Smart ɗin ya ɗan dungure masa kai da faɗin, “Ana son kayana amma ana guduna”. Ita dai Lulu dariya take musu. Tun yana amsa daga cinyarta harya zamo ya rarrafo jikinsa.
       “Oh ashe ƙiwar bamai nisa bace Sweetheart”. Smart ɗin ya faɗa yana ɗaukarsa zuwa jikinsa. A haka ya cigaba da bashi tea ɗin suna hira da Lulu duk dai akan yaron ne da yanda yake samun soyayyar ƴan uwanta da nashi. Sosai Smart kejin ɗari a ransa, dan kuwa maganar nan ce dai ta malam bahaushe da kan ce mai ɗa wawa shima ke ɗawainiya da shi....

*_NIGERIA_*

     A karo na farko tun bayan sakinsa da dawowarsa ƙasar yau sukai zaman meeting na farko da abokan cin mushen nasa. Wato Alh. Baita, Hon. Nakowa. Da Hon. Misau. Sai yaronsa Malami da aka dakatar daga waje kafin lokacin tasa shigowar yayi, dan akwai abinda ya ke son su fara tattaunawa da ba dole bane sai malamin yaji duk da kuwa a cikin sirrikansa babu abinda bai sani ba. Wani abu ma daya sani su su Alh. Baitan basu sani ba. Sun ƙara jajanta masa abinda ya faru cikin nuna ɓacin rai da tattara laifin gaba ɗaya akan Daddy da ɗan ka-ce-na-ce akan yanda akai suka san inda Lulu take. Shi dai shiru yay kawai yana saurarensu har suka gama bai ce uffan ba. Sai ma ya ɗakko musu batun kayan da yayo order da lokacin da yake ganin zasu iya shigowa Nigeria. Sun ɗan tattauna sosai akan hakan sannan suka dai sake komawa batun Daddy. Duk wani tsare-tsare a kansa sun yisa ne a wannan ranar harda ita Lulu da Smart suna a cikin plans nasu. Hatta da Abba wannan karon shima ya shigo lissafinsu.....

*_UK_*
Chapter 52 · 0% Book details