Sashe 21
Furar Danƙo Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kwanakin Lulu kusan uku tana fama da zazzaɓi kafin ALLAH ya bata lafiya ta dawo dai-dai, duk ta rame sai wani uban haske data ƙara. Kamar ance su dawo nan ciki ya fara girma, ga shi bata samun kunun gyaɗar da take so sai ɗan tea da take sha kaɗan-kaɗan, abincin ma Ummita kan zauna taita lallaɓata har sai taci ko yaya ne, duk da data gama take yin amansa. Wani bai taɓa zuwa musu ba, sai a randa suke cika sati guda ne suka wayi gari suka ga an ajiye musu kayayyakin abinci dana buƙata a falo, ciki harda gyaɗa abin mamaki. Kallon-kallo kawai sukeyi, a ransu sunajin tabbacin duk abinda sukeyi kenan ana sane da su. Murmushi Lulu ta saki a karo na farko, dan dama kawo su nan ya tabbatar mata da hasashenta akan kawun nata kenan. Basu da hurumin cewa bazasuci abinda aka kawo musun ba, sai dai Ummita kan zauna ta tofeshi da addu'oi sannan. Wannan abin da take ɗin ne ya sake sakama Lulu nutsuwa da ita. A hankali shaƙuwa ta cigaba da shiga tsakanin Ummita da Lulu, har takai yanzu Ummita na ɗorama Lulu karatun Alkur'ani da na wasu littattafan addini da take da su kamar yanda Lulun ta buƙata. Sannan cikin dare Ummita kan tashi tai nafilfilinta, tun Lulu najin damuwa da takurar hanata barci da Ummita keyi kasancewar bata saba da zama mutum biyu a ɗaki ɗaya ba har itama ta fara tashi tana sallar. Hakan ya saka Ummita a farin ciki sosai, haka itama Lulun wannan yanayin na sata jin farin ciki da jinta kamar wata sabuwar hallita, dan wata sabuwar nutduwa ce ta sake zo mata. Kullum sai Ummita ta mata addu'a ta bata a ruwa ta sha, sannan takan gaya mata wasu akan ta dingayi tana shafe cikinta da shi. A haka suka cika wata ɗaya a wannan juyayyen waje da basu san inane ba, sai dai hakan bai hana Lulu cigaba da tattara bayanai akan kawun nata ba, ranar da suka cika wata guda sai ga baƙonsu na farko daya fara ziyararsu. Wato Nurse Usman, babu wanda ya ganesa a cikin su Lulu, shi kuma bai nuna musu sani ba ya ce kawai yazo duba lafiyarta. Da taƙi sai yay kiran Alh. Sulaiman. Wannan ce ranar ta farko da su Lulu suka fahimci wanda ya kawo su nan ɗin duk da ita dama Lulu ta gama bama zuciyarta shi ɗinne. Al'amarin ya sake dilmiya Lulu a kogin mamaki game da abinda kawun nata ke yi akanta, sai dai batace komai ba ba kuma ta hana Nurse Usman ɗin yin aikinsa ba duk da tana ɗar-ɗar tana son a na duba mata lafiyar jaririnta kuma, shot note da Usman ya ajiye mata ya sakata sakin ajiyar zuciya. Shima sai yay mata ɗan guntun murmushi. Ya dubata tare da bata magunguna bayan ya tabbatar mata da lafiyar cikin nata. Tai masa godiya ya tafi. Sunyi mamakin ganin bayan ya kammala sai da ya kira akazo aka buɗe masa ƙofar sannan ya fita, hakan na nufin akwai wani a waje da ke gadinsu kenan ma kamar acan inda suka baro. Ganin Ummita zata saka damuwa a ranta Lulu tai mata murmushin kwantar da hankali. Note ɗin Usman ta miƙa mata, sai ga Ummita na murmushi da sauke ajiyar zuwa. Lulu ta lumshe idanunta a hankali ta furta “Yanzu kin fahimci wasan namu ne ko? Karma ki tadama kanki hankali yanzu lokacin tattara bayanai ne, dan haka babu buƙatar cigaba da shiga damuwa kuma farin ciki kawai domin kama tsuntsu mai wayo”.
Ƙaramar dariya Ummita tayi, yayinda a ƙasan zuciyarta tamaji ta fara tsoron Lulu, dan fa ta fahimci atsabibiyar kanta ce ashe.....
Tun daga wannan ranar Lulu da Ummita suka sake sakin jikinsu tamkar basu da wata damuwa, ga ciki nata haɓaka da bunƙasa cikin ƙoshin lafiya. Ganin yanda suka sake jiki da walwala ya saka Alh. Sulaiman bada umarnin a ɗan dinga buɗe su, sai dai yana son duk inda suka saka ƙafa a tsibirin nan yana sani. Dan ya zagayesu da mutanensa kusan goma batare da sun sani ba. A cewarsa yanzu plan zai fara. Kamar yanda itama Lulu take ji a ranta yanzu wasan zai fara........✍️
_🤣🤣Hahaha anayi muna cin gyaɗa mai gishiri🥱🥱🚴_
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 1️⃣8️⃣
.........*_CANADA_*
Sosai Lulu ta riga ta sakama ranta tsoron haihuwar ne, duk yanda su Usman suka so ta haihu da kanta hakan na neman gagara. Ga naƙudar tata da gani mai zafi ce, dan tayi wujiga-wujiga a ƙanƙanin lokaci. Tun ma tana hawayen har idanun sun bushe, Ummita dai nata maimaita mata addu'a tana faɗa. Har ALLAH ya isa sai da tama Smart cikin fitar hayyaci😜, akace kuma sai anyi Shari'a da shi yayi jail😂. Abin yaso bama Usman dariya ya dai danne da ƙyar. Dr Lameer yaja Usman gefe cikin damuwa ya ke faɗin, “Ussy inaga fa muyi mata CS ɗin nan kawai, ta riga ta saka tsoro a ranta ga shi kuma jinjirin yayi girma da yawa sosai saboda ciye-ciye data dingayi. Sannan an taɓa taɓa cikin hakan ya raunana mata mahaifa. Amma da ace bata saka tsoro a ranta ba wannan bakomai bane zata iya haihuwa da kanta. Yanzu kam ina tsoron kar wahala tasa mu rasa abinda ke cikinta”.
“No no Doctor bana fatan a rasa babyn nan wlhy, inaga kawai ayi mata cs ɗin”.
“Shike nan babu damuwa, wazai saka hannu a cikinku?”.
“Bara na saka hannun kawai ni”.
Alhamdullah an samu nasarar zaro baby boy a jikin Lulu ƙamshi. Lafiyayyen yaro ƙyaƙyƙyawa da bai baro komai na ubansa ba, ga shi ƙaton gaske masha ALLAH. Dan hatta wani tawadan ALLAH da Smart ke da shi a gefen kunnensa babba shima jinjiri na da shi. Ankai Lulu ɗakin hutu, yayinda Ummita ta rungume yaro tana mai jin ƙaunarsa a ranta kamar jininta. Shi kansa Usman yaron ya shigar masa rai. Bai kira Alh. Sulaiman da ke can yana jiran ace Lulu ta haihuwa ɗa a ruɓe ba, dan yau shine target ɗinsa akan kuɓutar da su Lulun dama. Shi yay duk wani tsare-tsarensa na nemawa Lulu transper da taimakon Dr Lameer zuwa wani ɓoyayyen ƙaramin asibiti a Derby city. A wannan daren aka fita da Lulu cikin ambulance da Ummita, abinka da turai tsaro kaca-kaca hankalinsu kwance suka iso Derby city zuwa gabannin asubahi. Sanin Alh. Sulaiman zai iya bibiyarsu komai ya tafi ne akan tsari da kulawa. Dan wani gida ne a kusa da asibitin aka ajiyesu, acan gefen gari wajen ana noman fruits, sai gidan abinci da ke gaba kaɗan kasancewar babban hanya ce, sannan bature shi babu ruwansa da daji duk inda yay masa alƙarya ce. Komai da Lulu zata iya buƙata na kulawar lafiyarta su Usman ya tanada a gidan, dan bashi da damar barin ƙasar da su a yanzu kasancewar passport nasu na hannun tsule, fita dasu kai tsaye zai zama mai wahala.
Kusan ƙarfe takwas Lulu ta dawo hayyacinta, inda cikin amincin ALLAH ta farka bakinta ɗauke da addu'a. Da sauri Ummita da ke zaune a gefenta rungume da jariri dake ta barcinsa tai saurin kallonta da faɗin, “Alhamdullah aunty kin farka?”. Idanu kawai Lulun ta zuba mata ita da jaririn, sai kuma ta sauke numfashi a hankali da motsa lips ɗin ta tana mai bin ɗakin da kallo. “Ina ne nan Ummita? Miya faru da ni?”. Cike da farin ciki Ummita ta ce, “Aunty an miki C'S ne ga baby boy mun samu, nan kuma sabon wajene da Usman ya kuɓuto damu da ga hannun kawunki.” Lulu batace komai ba sai idanu data zubama jaririn hannun Ummitan, da sauri Ummita ta miƙe zuwa gabanta da jaririn, Lulu ta zuba masa ido zuciyarta na wani irin harbawa na masifa. Dan duk da yaron da sauran ɗanyantakarsa ta kasancewa jinjiri kamaninsa da mahaifinsa a bayyane suke. A hankali ta lumshe idanunta tana sakin wasu irin ajiyar zuciya a jajjere, sai kawai ta samu kanta da sakin kuka. Hankalin Ummita ya tashi, ta shiga jera mata tambayoyi akan ko wani waje na mata ciwo ne? Bata iya bata amsa ba har su Usman suka shigo, Dr Lameer ya dubata yayinda Usman ke faman lallashinta da tabbatar mata ta kwantar da hankalinta, insha ALLAH sun kuɓuta kenan, zai kumayi duk yanda zai yi na ganin sun koma gida Nigeria. Ummita ita ta bada shawaran ya kamata ama jaririn huɗuba fa, dan haka suka tambayeta wane suna take so a saka masa. Ita kanta batama san lokacin da ta furta, *_“ALIYU”_* ba. Usman da ya saki wani ɗan murmushi ya ɗauki jinjirin yaymasa huɗuba da suna ALIYU HYDAR ZAKIN FAMA. tare da masa addu'a dan duk lalacewar Usman yanada iliminsa na addini. Kawai zama a waje ne ya sashi zama mara jin magana.
Lulu da idonta ke a lumshe a zuciyarta ta furta (ALLAH ya albarkaci rayuwarka *_Aliyu Aliyu Mika'il Mawashi_*) sai kuma ta ɗan yamitse fuska kamar wadda take jin hakan banbarakwai a zuciyarta...
_(To muma dai munce ALLAH ya raya Aliyu Aliyu Mika'il Mawashi. Dangin Smart kar ace bamuyi Barka ba🥱🚴)_
*_NIGERIA_*
Ƙaramar dariya Ummita tayi, yayinda a ƙasan zuciyarta tamaji ta fara tsoron Lulu, dan fa ta fahimci atsabibiyar kanta ce ashe.....
Tun daga wannan ranar Lulu da Ummita suka sake sakin jikinsu tamkar basu da wata damuwa, ga ciki nata haɓaka da bunƙasa cikin ƙoshin lafiya. Ganin yanda suka sake jiki da walwala ya saka Alh. Sulaiman bada umarnin a ɗan dinga buɗe su, sai dai yana son duk inda suka saka ƙafa a tsibirin nan yana sani. Dan ya zagayesu da mutanensa kusan goma batare da sun sani ba. A cewarsa yanzu plan zai fara. Kamar yanda itama Lulu take ji a ranta yanzu wasan zai fara........✍️
_🤣🤣Hahaha anayi muna cin gyaɗa mai gishiri🥱🥱🚴_
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 1️⃣8️⃣
.........*_CANADA_*
Sosai Lulu ta riga ta sakama ranta tsoron haihuwar ne, duk yanda su Usman suka so ta haihu da kanta hakan na neman gagara. Ga naƙudar tata da gani mai zafi ce, dan tayi wujiga-wujiga a ƙanƙanin lokaci. Tun ma tana hawayen har idanun sun bushe, Ummita dai nata maimaita mata addu'a tana faɗa. Har ALLAH ya isa sai da tama Smart cikin fitar hayyaci😜, akace kuma sai anyi Shari'a da shi yayi jail😂. Abin yaso bama Usman dariya ya dai danne da ƙyar. Dr Lameer yaja Usman gefe cikin damuwa ya ke faɗin, “Ussy inaga fa muyi mata CS ɗin nan kawai, ta riga ta saka tsoro a ranta ga shi kuma jinjirin yayi girma da yawa sosai saboda ciye-ciye data dingayi. Sannan an taɓa taɓa cikin hakan ya raunana mata mahaifa. Amma da ace bata saka tsoro a ranta ba wannan bakomai bane zata iya haihuwa da kanta. Yanzu kam ina tsoron kar wahala tasa mu rasa abinda ke cikinta”.
“No no Doctor bana fatan a rasa babyn nan wlhy, inaga kawai ayi mata cs ɗin”.
“Shike nan babu damuwa, wazai saka hannu a cikinku?”.
“Bara na saka hannun kawai ni”.
Alhamdullah an samu nasarar zaro baby boy a jikin Lulu ƙamshi. Lafiyayyen yaro ƙyaƙyƙyawa da bai baro komai na ubansa ba, ga shi ƙaton gaske masha ALLAH. Dan hatta wani tawadan ALLAH da Smart ke da shi a gefen kunnensa babba shima jinjiri na da shi. Ankai Lulu ɗakin hutu, yayinda Ummita ta rungume yaro tana mai jin ƙaunarsa a ranta kamar jininta. Shi kansa Usman yaron ya shigar masa rai. Bai kira Alh. Sulaiman da ke can yana jiran ace Lulu ta haihuwa ɗa a ruɓe ba, dan yau shine target ɗinsa akan kuɓutar da su Lulun dama. Shi yay duk wani tsare-tsarensa na nemawa Lulu transper da taimakon Dr Lameer zuwa wani ɓoyayyen ƙaramin asibiti a Derby city. A wannan daren aka fita da Lulu cikin ambulance da Ummita, abinka da turai tsaro kaca-kaca hankalinsu kwance suka iso Derby city zuwa gabannin asubahi. Sanin Alh. Sulaiman zai iya bibiyarsu komai ya tafi ne akan tsari da kulawa. Dan wani gida ne a kusa da asibitin aka ajiyesu, acan gefen gari wajen ana noman fruits, sai gidan abinci da ke gaba kaɗan kasancewar babban hanya ce, sannan bature shi babu ruwansa da daji duk inda yay masa alƙarya ce. Komai da Lulu zata iya buƙata na kulawar lafiyarta su Usman ya tanada a gidan, dan bashi da damar barin ƙasar da su a yanzu kasancewar passport nasu na hannun tsule, fita dasu kai tsaye zai zama mai wahala.
Kusan ƙarfe takwas Lulu ta dawo hayyacinta, inda cikin amincin ALLAH ta farka bakinta ɗauke da addu'a. Da sauri Ummita da ke zaune a gefenta rungume da jariri dake ta barcinsa tai saurin kallonta da faɗin, “Alhamdullah aunty kin farka?”. Idanu kawai Lulun ta zuba mata ita da jaririn, sai kuma ta sauke numfashi a hankali da motsa lips ɗin ta tana mai bin ɗakin da kallo. “Ina ne nan Ummita? Miya faru da ni?”. Cike da farin ciki Ummita ta ce, “Aunty an miki C'S ne ga baby boy mun samu, nan kuma sabon wajene da Usman ya kuɓuto damu da ga hannun kawunki.” Lulu batace komai ba sai idanu data zubama jaririn hannun Ummitan, da sauri Ummita ta miƙe zuwa gabanta da jaririn, Lulu ta zuba masa ido zuciyarta na wani irin harbawa na masifa. Dan duk da yaron da sauran ɗanyantakarsa ta kasancewa jinjiri kamaninsa da mahaifinsa a bayyane suke. A hankali ta lumshe idanunta tana sakin wasu irin ajiyar zuciya a jajjere, sai kawai ta samu kanta da sakin kuka. Hankalin Ummita ya tashi, ta shiga jera mata tambayoyi akan ko wani waje na mata ciwo ne? Bata iya bata amsa ba har su Usman suka shigo, Dr Lameer ya dubata yayinda Usman ke faman lallashinta da tabbatar mata ta kwantar da hankalinta, insha ALLAH sun kuɓuta kenan, zai kumayi duk yanda zai yi na ganin sun koma gida Nigeria. Ummita ita ta bada shawaran ya kamata ama jaririn huɗuba fa, dan haka suka tambayeta wane suna take so a saka masa. Ita kanta batama san lokacin da ta furta, *_“ALIYU”_* ba. Usman da ya saki wani ɗan murmushi ya ɗauki jinjirin yaymasa huɗuba da suna ALIYU HYDAR ZAKIN FAMA. tare da masa addu'a dan duk lalacewar Usman yanada iliminsa na addini. Kawai zama a waje ne ya sashi zama mara jin magana.
Lulu da idonta ke a lumshe a zuciyarta ta furta (ALLAH ya albarkaci rayuwarka *_Aliyu Aliyu Mika'il Mawashi_*) sai kuma ta ɗan yamitse fuska kamar wadda take jin hakan banbarakwai a zuciyarta...
_(To muma dai munce ALLAH ya raya Aliyu Aliyu Mika'il Mawashi. Dangin Smart kar ace bamuyi Barka ba🥱🚴)_
*_NIGERIA_*