← Book details Furar Danƙo Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 38 OF 90

Sashe 38

Furar Danƙo Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read

         Ajiyar zuciya Lulu ta sauke da maida kallonta kan AA bayan ficewarsu da ganin Hararar da Smart yay mata sanda yake ficewa. A dai-dai nan Ummita ta shigo ɗakin da sallama. Harara Lulu ta sakar mata cikin wasa da faɗin, “Sai yanzu ake ganinki? Ɗan naki ma yayi fushi ai shima”.
     “Oh oh karki haɗamu faɗa Aunty, my sweetheart, I'm sorry sorry naga kana tare da Daddy ai yau ko shiyyasa ban zo ba” Ummita tai maganar tana ɗaukar AA da manna masa kiss a goshi. Har zuciyarta take jin ƙaunar yaron, dan ya shigar mata rai sosai. Murmushi Lulu keyi, sai kuma takai kwance da faɗin, “Su Ammah barci sukeyi ne?”..
“A'a suna hira abinsu tun ɗazun. Amma gasu can tare da su Daddyn AA yanzu suna magana. Ashe gobe idan ALLAH ya kaimu shagalin sunan Yarona zamu sha?”.
      “Ku kuma ƴan son bidi'a dama haka kuke so ko?”
   Dariya Ummita tayi ranta fes......✍️

_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_

*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*

FURAR DANKO
Billyn Abdul

-ZAFIN KAI
Mamuhgee

-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at👇

1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇

09032345899

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

Zafafa🫶🔥

*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

  🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗

           𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 2️⃣8️⃣

___________________

*3 DAYS CLASS*

Ko kunsan cewa duk shekara ana samun rarar kudade a turai wanda ake cewa *unclaimed scholarship funds?* Kunsan irin ayyuka Jobs da zaku nema ku samu daga Nigeria zuwa kowace kasa? Ana samun rarar kudinne sakamakon rashin neman scholarship da bama yi, mun bude 3 days class don koya muku yadda zaku samu scholarship a kasashen waje, da yadda zaku nemi karatu da yadda zaku nemi Aiki Skills or unskills Job daga gida Nigeria zuwa kowace kasa da takardun secondary diploma ko degree da yadda zaka canza kasa Relocating daga Nigeria zuwa kowace kasa, Canada, Us, etc a tuntubeni

Class ze fara ranar jumaa insha Allah

WhatsApp group 👇👇👇

https://chat.whatsapp.com/E8Lzqogsm1nAFy1feTwbmA

WhatsApp 08144147273

👉 Masu bukatar tafiya da kudinsu ba scholarship ba, Muna yin study & work ko working visa, a takaitaccen lokaci, working visa Qatar munayi a sati daya, Canada study & working visa a 4 to 5 months, Oman working visa a 7 days insha Allah, Maxico Tour visa 1 month

_________________

.......Har dare Lulu bata sake saka Smart a idonta ba. Suna can sunyi busy shi da su Usman. Sai ma zuwa yamma ne da kewarta ya ishesa ya sa Usman yay masa kiranta a wayar Mamy duk da tsiyar da yeke masa bai kulashi ba. Gaisuwa kwai sukai a wayar ya tambayi AA tana amsa masa cikin basarwar nan tata. Gajeren Murmushi kawai yayi da jinjina jan aji da son tsare girma irin na Lulu. Ya jima baiga mace mai ɗankaren basar da abu ba irinta. Shi kaɗai yake iya gane wacece matar tasa, shiyyasa yake sarrafata a salon da takan zurma ta saki masa jiki batare da ita kanta tana sanin ta zurma ɗin ba. Dan ita Lulu zuma ce, idan kace ma zaka bita da wutar maimakon cin nasara kai wutar zata dawo ta baibaiye ne. Shiyyasa yake amsar zaƙin nata da harbin duka gaba ɗaya sannan ya bita da feshin furanni masu ƙamshi...
        Lulu tayi mamakin ganin irin ƙwarya-ƙwaryar liyafar da aka shirya cikin ƙanƙanin lokaci nan. Ba ita ba hatta su Ammah sunyi mamakin hakan. Sai dai Ammah taji daɗi sosai. Har dare suna abu guda. Bayan sun nitsa ɗin domin su huta ɗin ma gajiya ta hanasu zama a gidan. Lokacin da ya shigo ɗakin musu sai da safe Lulu ma tayi barci saboda alluran da ake mata. Yaronsa kawai yay ma addu'oi da kiss, idon Ammah kuma ya katangesa ga zuwa inda Lulun take sai dai kallo da ga nesa.

      Washe garin cikar sati guda da haihuwar AA suka wayi gari da shagalinsu da kuma isowar Ahmad da Coach, dan Smart yace idan zai iya ɓoyema kowa banda mutanen nan biyu. Yaro yasha addu'a a wajen Coach da Ahmad, Lulu da Smart kuma sun sha sheri wajen Ahmad dan sai da Lulu ta koma ɓoyewa idan taji maganarsa. Duk da bawani yawane da su ba abin dolene ya ƙayatar da mai kallo. Kamar yanda Smart ya faɗa an yankama AA ƙaton ragon turawa, a take kuma aka gashe shi gashi mai ƙyau da tsafta ya shiga jerin abinda za'aci a wajen shagalin. Duk da Lulu na dojewa haka dai dole ta shirya a cikin kayan da Mammy ta kawo mata sabuwar doguwar rigar shadda babba sosai da bazata takura mata ba saboda ciwonta. A kallo ɗaya mai kallo zai san shaddar taja kuɗi, maiƙon da take ma kawai da stones work da aka zuba mata na azaba abin ba'a magana. Bawai an ɗinka kayan bane dan wannan taron, kayan Mamy ne ta ɗinka abinta sai dai bata taɓa sakawa ba. Tunda wannan ta taso sai kawai ta ce Lulu tai amfani da su. Karo na farko Lulu tasa kayan da ba fitet ba a jikinta. Amma sai tai ƙyau sosai musamman da Ummita ta mata ɗauri mai ƙyau sosai, ƙanwar Usman da sai yau suka fara ganinta tai mata kwalliya tana dojewa ta na komai sai da akayi. AA ma an shiryashi cikin wasu tsadaddun kayan yara masu taushi da ƙayatarwa da Abbiensa ya siya masa. Angon jego ma yayi nasa ƙyawun cikin lallausan farin yadi da ya zauna masa ɗas ya fito a cikakken bahaushen sa ɗan Nigeria dan harda hula. Ita kanta Lulu a kallo ɗaya data masa ta sake tabbatar da jiya fa ba yau bace, ƴan maza sun gama cika mazaje sai dai fatan tsahon rai kawai da gamawa da iyaye lafiya. Yanda yake satar kallonta haka take satar kallonsa. Sai dai in sun kama juna ta hararesa ta basar. Yakanyi murmushi ya ɗauke kansa kawai. A haka dai aka fara ɗan taron da iyakar sune sai Dr Lameer da iyalinsa da ƙanwar Usman da boy friend ɗinta data gayyato. Sai abokan Usman biyu da suna ganin Smart suka shaida shi kasancewar su masoya ƙwallo, sun kuma bibiyi wasan link na ƙasar England. Ɗaya ma ɗan can ƙasar ɗinne. Lulu dai tayi mamakin a ina suka kwasosu? Da yanda suke girmama Smart ɗin da wani tattalinsa duk ya ɗaure kanta dan kowa dai yasan waye bature. Sai dai batace komai ba dai ta bar abinta a zuciya tana taɓe baki. Gaba ɗaya taron nasu dai basu fi su ashirin ba. An kuma yisa cike da birgewa da ƙayatarwa, gashi babu wata hayaniya sai ɗan cool music da aka saka na waƙoƙin masoya, duk da dai Ahmad ya saka waƙar data shiga har cikin jini da ɓargon Lulu da Smart ta hausa. Wato (Labarina baya zama nawa ta Salim Smart da KEWA ta Auta Waziri). Amma da farko basu saka ba saboda su Abbah. Sai da sukai addu'oi wa jariri da mai jego dama uban jego sannan. Can cikin lambun Abbah da Daddy da mahaifin Usman suka koma abinsu suka baje suna hirarsu ta dattijai da tarin abinci da aka shirya musu. Yayinda Ahmad da Usman da hali yazo ɗaya a rawar kai suka warware sautin sai dai bamai hayaniya ba. Ansha hotuna kala da iri, sai dai a duk sanda za'ai Smart na naniƙe da Lulu, idan da namiji za'ai tana gefensa ta inda babu kowa bai yarda wani ya raɓar masa mata ba. Tunma su Usman basu farga ba har suka fahimci mutumin nasu fa akwai kishi. Sai suka kama kansu suma yanda bazasu takaloshi ba. Ahmad ne dai kam ya addabesa tako ina da ina, sai dai tunda ya iso AA na hannunsa ya kasa bama kowa. Har cikin rai ƙaunar yaron yake ji tamkar shiya haifa. Yace dai surukinsa ne dan shi da Maryam ɗinsa zasu haifa masa mata. Anyi dariyar zancen nashi, yayin da Smart ya ce, “ALLAH ya shiryeka kai dai. Kadai fara tara ƴaƴa sai ka fara canjawa”.
        “To dama ance maka ban canja bane. Kana ganin har na fara furfura zuwan My Son duniya kuma surukina.” cewar Ahmad yana hararar Smart. Murmushi kawai yay masa da girgiza kai. Taro kam Alhmdllh, sai dai Lulu ana kammala hotuna ta koma ciki wajen Ammah da Mamy da suka basu waje suma saboda yanayin jikinta. Shima dai AA ba'a saki jiki da shi a wajen ba saboda sanyi. Sun ɗan samu gift dai-dai misali, zuwa dare taro ya tashi kowa ya kama gabansa. Gajiya ɗan kai da kawon da suka sha a yinin jiya yasa su Smart wucewa da wuri domin kwanciya.
Chapter 38 · 0% Book details