← Book details Furar Danƙo Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 63 OF 90

Sashe 63

Furar Danƙo Part 2 Complete Hausa Novel · about 6 min read

_Kiyi son ranki Dan lokacinki ne ta wajen mu🥱😂😂🚴🚴_

_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_

*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*

FURAR DANKO
Billyn Abdul

-ZAFIN KAI
Mamuhgee

-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma

-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo

Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400

Pay at👇

1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇

09032345899

Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070

*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*

*THANKS FOR CHOOSING US*🥰

Zafafa🫶🔥

*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲

  🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗

           𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻

𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 4️⃣4️⃣

.......Smart ya samu zama da Daddy da ya shigo London a ranar da Lulu ke cika kwanaki biyar. A ranar sun buga wasa a cikin London ɗin ne, bayan sun tashi ne sukai zaman tattaunawa su uku harda Uncle Yousuf da ya shigo domin kallon wasan shima. Daddy ya damƙa masa camara, tare da tabbatar masa Sulaiman yana shiri na musamman a kansu. Dan a yanzu haka akwai wata yarinyar baturiya da ya gano an turota ta shiga jikin Smart ɗin. Shiyyasa ma yay azamar kawo masa matarsa kusa da shi saboda gudun kar'a samu akasi. Murmushi Smart yayi da firzar da iska. Kansa a ƙasa ya ce, “Karka damu Daddy in sha ALLAH babu abinda zai faru. Kafin na mallaki iyali nafi ƙarfin kaina ma balle yanzu da na tabbatar da har zuri'a na fara tarawa. In dai al'amarin Sulaiman ne yabar damunka, dan a yanzu haka a tafin hannunmu yake. Abinda nake buƙata a wajenka kawai yanzu bayan wannan camara ɗin shine list ɗin abokan huɗɗarsa. Sannan ka sa su Hassan subar Abuja su koma Kano gabanku. Dan Sulaiman ya fara kai musu hari ta hanyar aboki, a yanzu haka ana gab da jan ra'ayinsu da wani kasuwancin da nake ƙyautata zaton irin shigo-shigon da akai maka ne”.
      Sosai hankalin Uncle Yousuf da Daddy ya tashi, dan sam Daddy hankalinsa bai kai wajenba saboda wani babban business da ya dauki hankalinsa kwana biyun nan. Smart kuma bai sanarma Uncle Yousuf ba dan yakan ɓoye wasu abubuwan gudun tada musu hankali. Muryar Daddy har rawa take wajen faɗin, “Aliyu yaya akai kasan wannan kai da kake anan?”.
    Murmushi Smart yay masa, cikin shafa kai ya ce, “Daddy koyarwarka ce ai. A yanzu idanuna a buɗe suke akan duk wani motsin su Sulaiman da tawagarsa. Sannan Usman ya sake zame min cctv camara. Dan yanzu haka yana Nigeria yin wani aiki da ya shafi hakan ma. Sannan Uncle Yousuf shine jagoran tafiyar,..”
     Da sauri Daddy ya dubi Uncle Yousuf. Murmushi yay masa ya kauda kansa shima. Smart yay dariya shima da cigaba da cewa, “Mu yanzu fatanmu Daddy kaje ka kwanta abinka ka huta. Karka damu da duk wani ƙulle-ƙullensu dan biye muke da su. Yanzu haka a daren jiya sunyi zama kanka harma da Abba. Sannan akwai kayansu dake hanyar shiga Nigeria. Kayane masu nauyin gaske da suka haɗa kusan kaso bibbiyu na dukiyarsu domin kawosu, dan mugayen kayan shaye-shayen ne kawai a cikinsu da in har suka samu shigar da su zasu samu maƙudan kuɗaɗe. Target ɗin mu yanzu muna zargin Sulaiman nada Company na sarrafa magunguna a ɓoye, sai dai bamu san a ina Companyn yake ba, shine muke bibiya domin mu tabbatar...”
        Ji Daddy yay kamar ya saki kuka, hannayen Smart da Uncle Yousuf ya kamo a cikin nashi, sai ma ya rasa mizaice da su. Sai ga hawaye kawai na gudu a fuskarsa. Da ga Uncle Yousuf har Smart rikicewa sukayi. A take suka shiga jera masa tambayoyi. Sai ya sakar musu murmushi yana goge ƙwallar tasa da faɗin, “Kunga bafa wani abu bane. ALLAH yay muku albarka. Ban taɓa tunanin zanga irin wannan ranar ba a gareni. Domin na ɓata tsahon shekarun girmana a tunanin yanda zan ɓulloma wannan al'amarin ne. A duk sanda nayi hangen sako su Hussain a ciki sai zuciyata ta ƙi aminta da hakan, saboda su sunada rauni. Sannan har yanzu suna a kan dokin ƙuruciya ne ba komai suke kallo a mai muhimmanci ba. Aliyu kai ɗan halak ne, nagodama ALLAH da yasa ka zamo mijin Mawaddat, na kuma godema ɗan uwana da yay wannan haɗin alkairi. ALLAH yay muku albarka. Ya kare rayuwarku da ta ahalinmu gaba ɗaya. ALLAH ya ƙara ɗaukaka ku, ku zama abin alfahari da babu irinsu a wannan zamanin. ALLAH ya albarkaci rayuwar Aliyu ƙarami da takwarana Isma'il (Ra'is) da Kamaluddeen, yasa suji ƙanku fiye da yanda kuka jiƙanmu”.
        Cikin rauni Smart da Uncle Yousuf ke amsawa da Amin. Smart na ƙara jin ƙaunar surukin nasa na ratsashi. Ga Uncle Yousuf Daddy ya juya. A hankali ya furta, “Nasha gaya maka Yousuf kaine babana a wannan matakin, narasa baba ne kawai a suna, amma ga babana a kusa dani.....”
     Cikin katseshi Uncle Yousuf ya ƙyalƙyale da dariya. Sai kuma ya rungumesa da faɗin, “Oh oh Yaya ni Wlhy kunya kake sakani, ni dai ba sai kace komai ba. Karka manta fa kaine na tashi nakema kallo a matsayin mahaifi kai da aunty Khareema. Kun raineni tun bansan kaina ba. Kun gatantani tun baku san minene daɗin ƴaƴa ba. Wlhy raina fansa ne a wajen kare ku daga duk wani maƙiyi da zaice kune abin harinsa. Ni dai fatana ka cigaba da kwantar min da hankalinka kawai da mana addu'a. Sannan ka janye mana ra'ayin su ƴan biyun kamar yanda Aliyu yace shine kawai aikinka.”
     Kasa cewa komai Daddy yayi, Smart dake saurarensu yana murmushi ya ɗan fesar da numfashi yana ɗan jujjuya camara ɗin. “Inaga a wannan gaɓar ya kamata Mawaddat ta fara aikinta. Dan haka zan duba abubuwan cikin camara ɗin nan tare da ita. Sai dai ina jin tsoron al'amarin ta dan bata da haƙurin kawaici ma abu, zata iya buɗe mana aiki da wuri wlhy”.
       Yanda ya ƙare maganar cikin marairaicewa ya saka Daddy da Uncle Yousuf kwashewa da dariya. Dan kuwa suko suka san wacece Mawaddat. Daddy yace, “Aliyu kamar kasan abinda nake tunani kenan ALLAH. Dan Mawaddat yanda kasan zawayi haka take. Ballema ta ƙullaci Sulaiman ɗin a yanzu, dan bakaga yanda taima Dada bane ba ma fa. Abinda kawai zamuyi shine da zarar kun gama gani sai mu samu lokaci mu zauna da ita mu duka kafin na wuce. Sauƙin ma ga babanta da ya san matakan bida ita yanda ya kamata sai kaga tayi abinda ake so”
      Murmushi kawai Uncle Yousuf ya keyi shi dai. Yace “Ku gama gulmarta duk sai na faɗa mata ai, dama kun mata wayo kun kawota nan. kai kaine za'a hana tuwo”... Yau maganar yana nuna Smart.
      Dariya Smart da Daddy keyi, Daddy yace, “Sauƙin abinma kaine gaba-gaba wajen ƙullawar dan nayi recording.”
    Smart ya kasa daina dariyar waɗan nan mutane. Komai nasu a sauƙaƙe cike da ƙauna da soyayyar juna. Suna ƙara masa ƙaimi akan ƙaunar ƴan uwansa shima.....

      _______★
Chapter 63 · 0% Book details