Sashe 34
Furar Danƙo Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
.......Sai kawai ya miƙe zuwa jikin window ya ƙurama waje idanu yana kallon shuke-shuken fruits da ganyayyakinsu ke sake ƙawata ƙamshin wajen. Da ƙyar ya iya samu ya dai-daita kansa a wajen har Ummita ta shigo ɗauke da zam-zam mai haɗe da zuma a ɗan wani kofi da ƙaramin spoon. Tana ajiyewa bata zauna ba ta fice. Nannauyar ajiyar zuciya ya sake sauke a karo na babu adadi da takowa ya dawo gaban gadon, komawa yay ya zauna a inda ya tashi tare da amsar yaron data janye a jikinta tana gyara riga. Amsarshi yayi yana goge masa baki, ita kuma sai ta miƙe masa ɗan cup ɗin. Cikin ɗan tura baki a ranta tana faɗin (Kaima ka ɗan ɗana wahalar da nake ci a kansa)
A mamakinta babu musu ya amsa. Kamar kuma dama can wanda ya saba da rainon cikin nutsuwarsa ya ɗibo ruwan zam-zam ɗin mai haɗe da zuma ya zubama yaron a baki kaɗan sai gashi yana ɗan motsa bakin da yamutsa fuska. Hakkanne ya saka Smart sakin murmushi har ya ɗago ya kalli Lulu da itama dai kallon nasu take yi. Kauda idanun nata tai ta maida kan bowl ɗin namanta ta fara ci. Cikin ɗage gira ya ce, “Wannan dai ƙwaɗayinki ne ya gado Madam”.
Da sauri ta ce, “Wa ɗin? ALLAH ya sawwaka mi muka haɗa da shi da zai gado ni, haɗuwa a duniya rabuwa a cikinta”. Sosai maganar tata ta bashi dariya, amma sai baiyi ba yay murmushi kaɗan yana girgiza kansa. Ganin yasha sosai ya goge masa baki ya gyara masa kwanciya a ɗan gadonsa. Lulu ya kama tana kallonsu, amma yana juyowa ta kauda kanta gefe. Kusa da ita ya koma ya zauna gaf, batare da yayi magana ba ya amshi tsinken da take cin naman ya tsira shima ya kai bakinsa, sake tsiro wani ya kai mata baki, idanunta ta zuba masa batare data buɗe bakin ba, shima kallon nata yake a yanayin kasala, dan haka ya ɗan lumshe nasa idanun da kaɗa mata kansa alamar ta amsa. Kamar mai jin ciwo akan lips ɗin ta motsa su da ƙyar shi kuma ya saka mata naman. A kusan tare suka sauke nannauyar ajiyar zuciya su duka. Da ga haka ya cigaba da bata yana ci, sun ci kamar lauma uku a bazata ya jeho mata tambayar da ta sakata ɗan daburcewa, amma jarumar taku sai ta dake abinta.
“Mi yasa kika zaɓi yin rainon cikin nan ke kaɗai batare da ni ba?”.
Cikin basarwar nan tata da son dakewa batare data kallesa ba ta ce, “Miye haɗina da kai da zamuyi rainon ciki tare?”.
“Mai ciki da abunsa har ace miye haɗinsa da cikin. Serious banji daɗin haka ba Mawaddat. Naso ace Ni ne da kaina na kula da ke tamkar ƙwai a cokali a wannan gaɓar. Ban taɓa fuskantar minene ainahin ƙunci ba sai da na waiga babu ke a duniyata, nasan har yanzu zuciyarki na baki na aikata miki abinda ya faru a wancan ranar bisa son zuciya. Ko kaɗan ba haka bane, dan ina son kasancewa da ke basai na baki komai ba ai, domin ke ɗin halalina ce, mizai sa saina wahalar da kaina ta hanyar gusar miki da hankali kamar wani matsoraci. Kin taɓa ganin Aliyu Hydar a matsayin KURE ba ZAKI ba?”. Harararsa tai, sai dai ta kasa cewa komai, shima sai ya ɗan murmusa kaɗan da cigaba da bata naman yana faɗin, “Duk abinda ya faru a wannan ranar Ahmad ne ya ƙullasa bada sani na ba, sai dai karki damu zan rama miki ai kinji ƴar ƙanwata”.
Cikin suɓutar baki da harararsa akan ƙanwarsa daya kirata tana waro idanu ta ce, “Ahmad fa? Taya zan yarda hakane?. Sannan akan Maryam ɗin? Zaka rama?”
“To mata tafi mata ne? Shi ya jawo mata ai. Duk da dai ni ya biyani tunda ban wahala a banza ba ga AA Mawashi na a kusa da ni”. Karan farko tai kamar zata saki murmushi sai kuma ta hararesa ta ɗan taɓe baki da faɗin, “Sai ka shirya amsa hakan a gaban alƙali ai. Dan sai an bimin kadin hakkina na fyaɗe”.
“Shima alƙalin koroki zaiyi da ga gabansa ai. Nidai yanzu nace magana ta wuce kawai, Aima Abbien AA afuwa bazai sake yin fyaɗe ba”.
“Humm” ta faɗa tana mai lumshe idanunta. Shima sai ya zuba mata nasa kawai yana kallonta cike da shauƙi. Cikin motsa lips ɗinsa a hankali ya furta, “Ke ƙyaƙyƙyawa ce Mawaddatan'warahmah”.
Da sauri ta buɗe idanun nata a daburce, dan yanda ya furta kalmar sai taji kamar ya haɗa da jinin jikinta ne ya zuƙe har ma da numfashi, kafin ta samu damar cewa komai Usman yay sallama. Amsa masa yay yana mai dafe goshinsa da faɗin, “Gaskiya baka iya zuwa ba”.
Ƙaramar dariya Lulu tai tana kauda kai, shi kuma ya harareta da bashi izinin shigowa bayan ya miƙa mata mayafin da ke ajiye gefenta da faɗin, “ALLAH yasa ma ba haka kike zama min a gabansa ba yana kallemin kayana”. Yanda yay maganar cikin ɓata fuska ya sakata sake sakin murmushi, cike da neman tunzurashi ta ce, “Mi kuma ya rage bayan shine mai karɓar haih....”
“Mtsoww! Shut up!”.
Ya faɗa a hasale yana balla mata harara fuska a gimtse. Dai-dai nan Usman ɗin ya ƙarasa shigowa, sama-sama ya bashi hannu suka gaisa, kafin ya ɗan juya yama Lulu tambayoyi game da yanayin jikinta. Ta tabbatar masa da Alhmdllh bata jin komai. Shima hamdalar yay yana ɗan duban Smart da murmushi, “Oga zamu iya wucewa masauki ko anan zaka kwana ka taya Madam jego? Dan itama lokacin barcinta yayi”.
“Kaga dana ɓarke ɗinkin sai ku tara min jama'arku na likitoci kenan”. Smart ya bashi amsa da ɗan barkwanci duk da da gaske maganar Lulu ta sosa masa zuciya amma ya danne.
Ƙaramar dariya Usman yay da faɗin, “Ai kai oga ne zamu ɗaga maka ƙafa kodan Son ɗina AA”.
Murmushi Smart ya sake yi kawai bai ce komai ba. Usman kuma ya matsa ga Lulu ya mata allura da duk sauran abinda ya dace sukai mata sallama, gaba Usman yay ya barsa. Ganin yanda Smart ɗin ya raka bayansa da kallo mai kama da harara yasa Lulu saurin faɗin, “Nifa wasa nake maka kada ka ƙullacin bawan ALLAH bayan ƙoƙarin sa a kammu. Kana dai ganin a yanda yay min allura ma cike da taka tsantsan”.
Ajiyar zuciya ya sauke a hankali tare da ɗan lumshe idanunsa da launinsu har ya canja. Batare da yace mata komai ba a karo na biyu ya ƙarasa gareta ya rungumeta tsam-tsam a jikinsa ta yanda dai bai taɓa mata ciwo ba. Su dukansu babu wanda bai sauke ajiyar zuciya ba, yayinda Smart ya shiga laluben lips nata. Da sauri ta janye jikinta saboda jiyo takun tahowa, shima sai ya miƙe dan dai-dai nan Ammah tai sallama. Gaban gadon Babyn ya koma tare da kama hannayensa ya fara tofa masa addu'oi. Har saida ya kammala sannan ya ɗago yana kallon Ammah da ke taimakawa Lulu ta kwanta yanda zataji daɗi. Sun ƙara haɗa ido da Lulun ta kauda kai shima ya kauda da ɗan salon taɓe baki yana wani lumshe idanunsa.....
*_NIGERIA_*
Sosai jikin Dada ya ruɗe a safiyar yau dan haka hankalin ƴaƴanta a tashe yake matuƙa. Cikin ƙanƙanin lokaci aka shirya mata barin ƙasar. Baba Garko na Abuja a lokacin Uncle Khamil ya kira shi a ruɗe yana sanar masa zai tafi Kano jikin Dada ya tashi sosai. Duk da ya ji damuwa a ransa sai ya danne cikin nuna halin ko'in kula ya ce, “ALLAH ya bata lafiya” ya kashe wayar abinsa. Abinda Baban yay ya sake tada hankalin yaran. Dan sun sake tabbatar da har yanzu ransa a ɓace yake akan mahaifiyar tasu. Haka suka shirya wasu a cikinsu suka wuce da ita gwiwa a sage. Wanda aka bari a gida kuma suka bita da addu'a kafin suma subi bayansu da ga baya. Matansu kam addu'a suke ALLAH yasa da ga can ta wuce ko zasu huta da samun sukunin zama da mazajensu cikin ƴanci kamar kowacce mace a gidan aurenta. Dan gaskiya surukar tasu ta musu kane-kane a cikin rayuwar aurarrakin nasu....
(To mudai munce ALLAH ya baki lafiya Dadansy).
__________★
A mamakinta babu musu ya amsa. Kamar kuma dama can wanda ya saba da rainon cikin nutsuwarsa ya ɗibo ruwan zam-zam ɗin mai haɗe da zuma ya zubama yaron a baki kaɗan sai gashi yana ɗan motsa bakin da yamutsa fuska. Hakkanne ya saka Smart sakin murmushi har ya ɗago ya kalli Lulu da itama dai kallon nasu take yi. Kauda idanun nata tai ta maida kan bowl ɗin namanta ta fara ci. Cikin ɗage gira ya ce, “Wannan dai ƙwaɗayinki ne ya gado Madam”.
Da sauri ta ce, “Wa ɗin? ALLAH ya sawwaka mi muka haɗa da shi da zai gado ni, haɗuwa a duniya rabuwa a cikinta”. Sosai maganar tata ta bashi dariya, amma sai baiyi ba yay murmushi kaɗan yana girgiza kansa. Ganin yasha sosai ya goge masa baki ya gyara masa kwanciya a ɗan gadonsa. Lulu ya kama tana kallonsu, amma yana juyowa ta kauda kanta gefe. Kusa da ita ya koma ya zauna gaf, batare da yayi magana ba ya amshi tsinken da take cin naman ya tsira shima ya kai bakinsa, sake tsiro wani ya kai mata baki, idanunta ta zuba masa batare data buɗe bakin ba, shima kallon nata yake a yanayin kasala, dan haka ya ɗan lumshe nasa idanun da kaɗa mata kansa alamar ta amsa. Kamar mai jin ciwo akan lips ɗin ta motsa su da ƙyar shi kuma ya saka mata naman. A kusan tare suka sauke nannauyar ajiyar zuciya su duka. Da ga haka ya cigaba da bata yana ci, sun ci kamar lauma uku a bazata ya jeho mata tambayar da ta sakata ɗan daburcewa, amma jarumar taku sai ta dake abinta.
“Mi yasa kika zaɓi yin rainon cikin nan ke kaɗai batare da ni ba?”.
Cikin basarwar nan tata da son dakewa batare data kallesa ba ta ce, “Miye haɗina da kai da zamuyi rainon ciki tare?”.
“Mai ciki da abunsa har ace miye haɗinsa da cikin. Serious banji daɗin haka ba Mawaddat. Naso ace Ni ne da kaina na kula da ke tamkar ƙwai a cokali a wannan gaɓar. Ban taɓa fuskantar minene ainahin ƙunci ba sai da na waiga babu ke a duniyata, nasan har yanzu zuciyarki na baki na aikata miki abinda ya faru a wancan ranar bisa son zuciya. Ko kaɗan ba haka bane, dan ina son kasancewa da ke basai na baki komai ba ai, domin ke ɗin halalina ce, mizai sa saina wahalar da kaina ta hanyar gusar miki da hankali kamar wani matsoraci. Kin taɓa ganin Aliyu Hydar a matsayin KURE ba ZAKI ba?”. Harararsa tai, sai dai ta kasa cewa komai, shima sai ya ɗan murmusa kaɗan da cigaba da bata naman yana faɗin, “Duk abinda ya faru a wannan ranar Ahmad ne ya ƙullasa bada sani na ba, sai dai karki damu zan rama miki ai kinji ƴar ƙanwata”.
Cikin suɓutar baki da harararsa akan ƙanwarsa daya kirata tana waro idanu ta ce, “Ahmad fa? Taya zan yarda hakane?. Sannan akan Maryam ɗin? Zaka rama?”
“To mata tafi mata ne? Shi ya jawo mata ai. Duk da dai ni ya biyani tunda ban wahala a banza ba ga AA Mawashi na a kusa da ni”. Karan farko tai kamar zata saki murmushi sai kuma ta hararesa ta ɗan taɓe baki da faɗin, “Sai ka shirya amsa hakan a gaban alƙali ai. Dan sai an bimin kadin hakkina na fyaɗe”.
“Shima alƙalin koroki zaiyi da ga gabansa ai. Nidai yanzu nace magana ta wuce kawai, Aima Abbien AA afuwa bazai sake yin fyaɗe ba”.
“Humm” ta faɗa tana mai lumshe idanunta. Shima sai ya zuba mata nasa kawai yana kallonta cike da shauƙi. Cikin motsa lips ɗinsa a hankali ya furta, “Ke ƙyaƙyƙyawa ce Mawaddatan'warahmah”.
Da sauri ta buɗe idanun nata a daburce, dan yanda ya furta kalmar sai taji kamar ya haɗa da jinin jikinta ne ya zuƙe har ma da numfashi, kafin ta samu damar cewa komai Usman yay sallama. Amsa masa yay yana mai dafe goshinsa da faɗin, “Gaskiya baka iya zuwa ba”.
Ƙaramar dariya Lulu tai tana kauda kai, shi kuma ya harareta da bashi izinin shigowa bayan ya miƙa mata mayafin da ke ajiye gefenta da faɗin, “ALLAH yasa ma ba haka kike zama min a gabansa ba yana kallemin kayana”. Yanda yay maganar cikin ɓata fuska ya sakata sake sakin murmushi, cike da neman tunzurashi ta ce, “Mi kuma ya rage bayan shine mai karɓar haih....”
“Mtsoww! Shut up!”.
Ya faɗa a hasale yana balla mata harara fuska a gimtse. Dai-dai nan Usman ɗin ya ƙarasa shigowa, sama-sama ya bashi hannu suka gaisa, kafin ya ɗan juya yama Lulu tambayoyi game da yanayin jikinta. Ta tabbatar masa da Alhmdllh bata jin komai. Shima hamdalar yay yana ɗan duban Smart da murmushi, “Oga zamu iya wucewa masauki ko anan zaka kwana ka taya Madam jego? Dan itama lokacin barcinta yayi”.
“Kaga dana ɓarke ɗinkin sai ku tara min jama'arku na likitoci kenan”. Smart ya bashi amsa da ɗan barkwanci duk da da gaske maganar Lulu ta sosa masa zuciya amma ya danne.
Ƙaramar dariya Usman yay da faɗin, “Ai kai oga ne zamu ɗaga maka ƙafa kodan Son ɗina AA”.
Murmushi Smart ya sake yi kawai bai ce komai ba. Usman kuma ya matsa ga Lulu ya mata allura da duk sauran abinda ya dace sukai mata sallama, gaba Usman yay ya barsa. Ganin yanda Smart ɗin ya raka bayansa da kallo mai kama da harara yasa Lulu saurin faɗin, “Nifa wasa nake maka kada ka ƙullacin bawan ALLAH bayan ƙoƙarin sa a kammu. Kana dai ganin a yanda yay min allura ma cike da taka tsantsan”.
Ajiyar zuciya ya sauke a hankali tare da ɗan lumshe idanunsa da launinsu har ya canja. Batare da yace mata komai ba a karo na biyu ya ƙarasa gareta ya rungumeta tsam-tsam a jikinsa ta yanda dai bai taɓa mata ciwo ba. Su dukansu babu wanda bai sauke ajiyar zuciya ba, yayinda Smart ya shiga laluben lips nata. Da sauri ta janye jikinta saboda jiyo takun tahowa, shima sai ya miƙe dan dai-dai nan Ammah tai sallama. Gaban gadon Babyn ya koma tare da kama hannayensa ya fara tofa masa addu'oi. Har saida ya kammala sannan ya ɗago yana kallon Ammah da ke taimakawa Lulu ta kwanta yanda zataji daɗi. Sun ƙara haɗa ido da Lulun ta kauda kai shima ya kauda da ɗan salon taɓe baki yana wani lumshe idanunsa.....
*_NIGERIA_*
Sosai jikin Dada ya ruɗe a safiyar yau dan haka hankalin ƴaƴanta a tashe yake matuƙa. Cikin ƙanƙanin lokaci aka shirya mata barin ƙasar. Baba Garko na Abuja a lokacin Uncle Khamil ya kira shi a ruɗe yana sanar masa zai tafi Kano jikin Dada ya tashi sosai. Duk da ya ji damuwa a ransa sai ya danne cikin nuna halin ko'in kula ya ce, “ALLAH ya bata lafiya” ya kashe wayar abinsa. Abinda Baban yay ya sake tada hankalin yaran. Dan sun sake tabbatar da har yanzu ransa a ɓace yake akan mahaifiyar tasu. Haka suka shirya wasu a cikinsu suka wuce da ita gwiwa a sage. Wanda aka bari a gida kuma suka bita da addu'a kafin suma subi bayansu da ga baya. Matansu kam addu'a suke ALLAH yasa da ga can ta wuce ko zasu huta da samun sukunin zama da mazajensu cikin ƴanci kamar kowacce mace a gidan aurenta. Dan gaskiya surukar tasu ta musu kane-kane a cikin rayuwar aurarrakin nasu....
(To mudai munce ALLAH ya baki lafiya Dadansy).
__________★