Sashe 30
Furar Danƙo Part 2 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Washe gari da yamma suka wuce Canada har da Smart dake jin wani irin faɗuwar gaba lokaci-lokaci, yakanyi sauri ya ambaci sunan ALLAH. Wannan ziyara tazo ma Lulu a bazatar bazata. Dan bata san wainar da ake toyawa ba sai kawai ganin Usman tai da baƙi. Lokacin da suka shigo tana toilet ne ita da Mamy dake gasa mata jikinta da towel kamar dai yanda ake cikakken wankan jego a Nigeria duk da Lulu tasha maganin da ya dace Mamy bata barta ba kullum sai ta mata safe da yamma ita da ɗan jinjiri.
A hankali take tafiya Mamy biye da ita, tayi fayau da ita sai haske data ƙara da wani cikar ido irin na jego dan tana samun kulawa sosai irin ta malam bahaushe a wajen Mammy duk da cs akai mata. Alhamdullah kumburin ciki da tai duk ya saɓe amma baza'a kirata ramammiya ba kai tsaye. Sanye take cikin doguwar riga mara nauyi dake a buɗe sosai saboda yanayin inda aka yanka ta. Baya tai zata faɗi saboda firgicin ganin abinda idanunta suka gane mata, sai da Mamy ta riƙota tana faɗin, “Mawaddat yi a hankali kinji”. Daga lips ɗin Lulu har zuwa jikinta rawa yake yi, ɗaya bayan ɗaya take binsu da kallo tun daga kan Daddynta har zuwa mutum na ƙarshe da ke tsaye ya ɗan jingina abango da harɗe ƙafafunsa waje guda. Sanye yake cikin Suit milk da sukai masifar masa ƙyau da fitar da cikar haiba da kamalar da ya ƙara, ga wani irin ƙamshi mai sanyi da daɗin shaƙa, gaba ɗaya ya canja da ga Smart na Nigeria zuwa wani baƙin bature mai aji a yanzu. Yanda yay tsaiwar ƙasaita da harɗe ƙafafunsa waje guda idanunsa a waya yana daƙila kamar baya a wajen saika rantse ba shine ke zumuɗin azo ba fiye da kowa. Sai da Mamy ta ambaci sunan Lulu ne ya ɗan ɗago idanun nasa a hankali da take kira na macizai kamar zai lumshesu sai kuma ya zuba mata su cikin shammata da bazata.
Wani irin girgiza zuciyarta tayi ƙirjinta na bugawa da sauri-sauri. Rashin mafita ya sata juyawa cikin tsumar jiki ta basu baya tana mai rumtse idanunta da masifar ƙarfi. Ammah ce ta taka a hankali zuwa gareta, cikin tausayawa da ƙauna ta kira sunanta. Kasa juyowa Lulu tayi sai jikinta da ke ƙara ƙarfin rawa. Riƙo hannunta Ammah tayi ta juyo da ita a hankali, sai kaiwa ta faɗa jikin Ammahn ta rungumeta tsam-tsam tare da sakin kuka mai tsuma zuciya.
A hankali Smart ya sauke idanun nasa ƙasa yana wani irin haɗiyar zuciya da sauri-sauri. Dai-dai nan Ummita ta shigo ɗakin da sallama bayanta goye da baƙon duniya dake barci. Turus tai tana kallonsu itama cikin tsoro da mamaki, yayinda su kuma suka zubama jinjirin bayanta ido. Uncle Yousuf ne yay ƙarfin halin mata nunin ta kunto yaron. Sai ta kalli Mamy. Kai Mamy ta jinjina mata alamar ta kuntosa babu matsala, dan haka ta ɗan saki ajiyar zuciya tare da kunto yaron ta miƙama Uncle Yousuf ɗin. Kamar ko ya sani sai ga idanu ya ɗan buɗe yana motsa baki alamar neman abinci. Dariya Uncle Yousuf ya saki da faɗin, “Oh oh Aliyu dai kawai ne anan babu wani banbanci wlhy sai na shekaru”. Yay maganar yana ƙarasawa gaban Abba da Daddy cikin sassarfa. A hankali Smart da idanunsa ke kan yaron ko ƙyaftawa babu tun shigowar Ummita ya wani lumshe idanun da suka kaɗa a hankali yana sauke ajiyar zuciya a jajjere. Jin al'amarin yake kamar a mafarki, shi Aliyu Hydar ne da ɗa na mutum matsayin mallakinsa a wannan duniyar. Ya arrahaman ALLAH mai alkairi. Furucin Lulu da ke faɗin, Ammah nayi kewarku cikin kuka ya sashi buɗe idanun nasa ya zuba musu su. Murmushi Ammah da ke sharema Lulu hawaye takeyi, kafin ta kama hannunta ta ƙarasa da ita a saman gadon da take jiyyar. Dai-dai nan Abbah ya ƙarasa da Jinjirin ga Smart, nannauyar ajiyar zuciya Smart ya ja tare da fesarwa, sai yaji ma duk ya sake daburcewa. Fahimtar hakan da Abbah yay ne ya sashi sakin ƙaramar dariya da sake miƙa masa yaron. A hankali ya miƙa hannayensa duk biyu Abba ya saka masa yaron a ciki, sai da yay masa kallon kusan sakanni goma kafin ya matsar dashi saman ƙirjinsa ya rungume tsam-tsam dai ga hawaye sharrrr. Uncle Yousuf dake murmushi ne ya ƙaraso gareshi, cikin tsokana ya ce, “A'a ƙanina kaga zauna karka zube mana a ƙasa majiyatan su sake ƙaruwa kuma”.
Furucin Uncle Yousuf ɗin ya sata sake ɗago idanu a karo na biyu ta kallesa, sai akai sa'a shima ita ɗin yake kallo har yanzu yaron na'a rungume jikinsa sai dai ya share hawayen. Harara ta balla masa da ɗauke kanta tana tura baki. Sai ya samu kansa da sakin murmushi yana wani ƙasa-ƙasa da idanu shima. Ammah da ke ankare da su su duka ta ce, “Babana zo mana naga sabon uba dana sake yi, danni kam kai da Mawaddat kun zama Kakannina yanzu kam tunda kun haifa mini Babana”.
A hankali ya tako gaban Ammah cikin yanayin nan nasa na nutsuwa da kasancewa jarumin namiji tsayayye. Maimakon ya miƙama Ammah babyn sai ya kai zaune a kujerar gaban gadon kusan da Mawaddat da hankalinta ke kan Uncle Yousuf da ke mata magana ƙasa-ƙasa.....
Bayan an gaggasa Lulu ta gama ma Daddy da Uncle Yousuf shagwaɓa da koke-kokenta suma sukai mata faɗa akan barin ɗakin mijinta tabi Dada. Ta basu haƙuri da amsar kuskurenta. Sunji daɗin nuna nadamar tata kuwa a gaban kowa. Duk alkairin Ummita da Mamy da Usman gareta bata ɓoye ba. Su Abba sukai musu godiya sosai da wannan karamci duk da akwai sannaya tsakanin mahaifin Usman ɗin da Daddy. Bayan komai ya natsa an fahimci juna Usman yay ma su Abba jagora zuwa masauki, har lokacin kuma bakin Lulu da Smart bai saɓa ba, sai dai ƴar satar kallon juna, koda yake ma shike satar kallon nata, itako tayi biris kamar ta ma manta da shi a ɗakin take nunawa. Baiji komai a ransa ba game da hakan dan halinta kuma ai sai dai ya bama wani labari yanzu. Lulu akwai jan aji, koda wasa bata yarda ta zama a ƙasa ba akan al'amarinta. Lokacin da zasu wuce Usman ya ce ai shi Smart a barshi anan tare zasu wuce gida, suje su ya fara kaisu masauki sai ya dawo ya samesa. Mamy da Ammah kam dama tuni sun fice zuwa ɗayan ɗakin gidan. Itama Ummita sai ta zare jikinta cikin dabara wai bari ta wanke kayan baby data jiƙa ɗazun. Harara Lulu data fara tsarguwa da wannan ƴar zare jikin da ake ɗai-ɗai tabi Ummita da shi, sai dai batace komai ba dan Ummitan ta fita tana mata dariya...........✍️
*_😂Kar naji wani yace komai kuma ehe. Musamman ma dangi dangi Smart ɗinnan. 🙈Koda yake akwai su aunty fa🚴🚴_*
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 2️⃣1️⃣
A hankali take tafiya Mamy biye da ita, tayi fayau da ita sai haske data ƙara da wani cikar ido irin na jego dan tana samun kulawa sosai irin ta malam bahaushe a wajen Mammy duk da cs akai mata. Alhamdullah kumburin ciki da tai duk ya saɓe amma baza'a kirata ramammiya ba kai tsaye. Sanye take cikin doguwar riga mara nauyi dake a buɗe sosai saboda yanayin inda aka yanka ta. Baya tai zata faɗi saboda firgicin ganin abinda idanunta suka gane mata, sai da Mamy ta riƙota tana faɗin, “Mawaddat yi a hankali kinji”. Daga lips ɗin Lulu har zuwa jikinta rawa yake yi, ɗaya bayan ɗaya take binsu da kallo tun daga kan Daddynta har zuwa mutum na ƙarshe da ke tsaye ya ɗan jingina abango da harɗe ƙafafunsa waje guda. Sanye yake cikin Suit milk da sukai masifar masa ƙyau da fitar da cikar haiba da kamalar da ya ƙara, ga wani irin ƙamshi mai sanyi da daɗin shaƙa, gaba ɗaya ya canja da ga Smart na Nigeria zuwa wani baƙin bature mai aji a yanzu. Yanda yay tsaiwar ƙasaita da harɗe ƙafafunsa waje guda idanunsa a waya yana daƙila kamar baya a wajen saika rantse ba shine ke zumuɗin azo ba fiye da kowa. Sai da Mamy ta ambaci sunan Lulu ne ya ɗan ɗago idanun nasa a hankali da take kira na macizai kamar zai lumshesu sai kuma ya zuba mata su cikin shammata da bazata.
Wani irin girgiza zuciyarta tayi ƙirjinta na bugawa da sauri-sauri. Rashin mafita ya sata juyawa cikin tsumar jiki ta basu baya tana mai rumtse idanunta da masifar ƙarfi. Ammah ce ta taka a hankali zuwa gareta, cikin tausayawa da ƙauna ta kira sunanta. Kasa juyowa Lulu tayi sai jikinta da ke ƙara ƙarfin rawa. Riƙo hannunta Ammah tayi ta juyo da ita a hankali, sai kaiwa ta faɗa jikin Ammahn ta rungumeta tsam-tsam tare da sakin kuka mai tsuma zuciya.
A hankali Smart ya sauke idanun nasa ƙasa yana wani irin haɗiyar zuciya da sauri-sauri. Dai-dai nan Ummita ta shigo ɗakin da sallama bayanta goye da baƙon duniya dake barci. Turus tai tana kallonsu itama cikin tsoro da mamaki, yayinda su kuma suka zubama jinjirin bayanta ido. Uncle Yousuf ne yay ƙarfin halin mata nunin ta kunto yaron. Sai ta kalli Mamy. Kai Mamy ta jinjina mata alamar ta kuntosa babu matsala, dan haka ta ɗan saki ajiyar zuciya tare da kunto yaron ta miƙama Uncle Yousuf ɗin. Kamar ko ya sani sai ga idanu ya ɗan buɗe yana motsa baki alamar neman abinci. Dariya Uncle Yousuf ya saki da faɗin, “Oh oh Aliyu dai kawai ne anan babu wani banbanci wlhy sai na shekaru”. Yay maganar yana ƙarasawa gaban Abba da Daddy cikin sassarfa. A hankali Smart da idanunsa ke kan yaron ko ƙyaftawa babu tun shigowar Ummita ya wani lumshe idanun da suka kaɗa a hankali yana sauke ajiyar zuciya a jajjere. Jin al'amarin yake kamar a mafarki, shi Aliyu Hydar ne da ɗa na mutum matsayin mallakinsa a wannan duniyar. Ya arrahaman ALLAH mai alkairi. Furucin Lulu da ke faɗin, Ammah nayi kewarku cikin kuka ya sashi buɗe idanun nasa ya zuba musu su. Murmushi Ammah da ke sharema Lulu hawaye takeyi, kafin ta kama hannunta ta ƙarasa da ita a saman gadon da take jiyyar. Dai-dai nan Abbah ya ƙarasa da Jinjirin ga Smart, nannauyar ajiyar zuciya Smart ya ja tare da fesarwa, sai yaji ma duk ya sake daburcewa. Fahimtar hakan da Abbah yay ne ya sashi sakin ƙaramar dariya da sake miƙa masa yaron. A hankali ya miƙa hannayensa duk biyu Abba ya saka masa yaron a ciki, sai da yay masa kallon kusan sakanni goma kafin ya matsar dashi saman ƙirjinsa ya rungume tsam-tsam dai ga hawaye sharrrr. Uncle Yousuf dake murmushi ne ya ƙaraso gareshi, cikin tsokana ya ce, “A'a ƙanina kaga zauna karka zube mana a ƙasa majiyatan su sake ƙaruwa kuma”.
Furucin Uncle Yousuf ɗin ya sata sake ɗago idanu a karo na biyu ta kallesa, sai akai sa'a shima ita ɗin yake kallo har yanzu yaron na'a rungume jikinsa sai dai ya share hawayen. Harara ta balla masa da ɗauke kanta tana tura baki. Sai ya samu kansa da sakin murmushi yana wani ƙasa-ƙasa da idanu shima. Ammah da ke ankare da su su duka ta ce, “Babana zo mana naga sabon uba dana sake yi, danni kam kai da Mawaddat kun zama Kakannina yanzu kam tunda kun haifa mini Babana”.
A hankali ya tako gaban Ammah cikin yanayin nan nasa na nutsuwa da kasancewa jarumin namiji tsayayye. Maimakon ya miƙama Ammah babyn sai ya kai zaune a kujerar gaban gadon kusan da Mawaddat da hankalinta ke kan Uncle Yousuf da ke mata magana ƙasa-ƙasa.....
Bayan an gaggasa Lulu ta gama ma Daddy da Uncle Yousuf shagwaɓa da koke-kokenta suma sukai mata faɗa akan barin ɗakin mijinta tabi Dada. Ta basu haƙuri da amsar kuskurenta. Sunji daɗin nuna nadamar tata kuwa a gaban kowa. Duk alkairin Ummita da Mamy da Usman gareta bata ɓoye ba. Su Abba sukai musu godiya sosai da wannan karamci duk da akwai sannaya tsakanin mahaifin Usman ɗin da Daddy. Bayan komai ya natsa an fahimci juna Usman yay ma su Abba jagora zuwa masauki, har lokacin kuma bakin Lulu da Smart bai saɓa ba, sai dai ƴar satar kallon juna, koda yake ma shike satar kallon nata, itako tayi biris kamar ta ma manta da shi a ɗakin take nunawa. Baiji komai a ransa ba game da hakan dan halinta kuma ai sai dai ya bama wani labari yanzu. Lulu akwai jan aji, koda wasa bata yarda ta zama a ƙasa ba akan al'amarinta. Lokacin da zasu wuce Usman ya ce ai shi Smart a barshi anan tare zasu wuce gida, suje su ya fara kaisu masauki sai ya dawo ya samesa. Mamy da Ammah kam dama tuni sun fice zuwa ɗayan ɗakin gidan. Itama Ummita sai ta zare jikinta cikin dabara wai bari ta wanke kayan baby data jiƙa ɗazun. Harara Lulu data fara tsarguwa da wannan ƴar zare jikin da ake ɗai-ɗai tabi Ummita da shi, sai dai batace komai ba dan Ummitan ta fita tana mata dariya...........✍️
*_😂Kar naji wani yace komai kuma ehe. Musamman ma dangi dangi Smart ɗinnan. 🙈Koda yake akwai su aunty fa🚴🚴_*
_LABARAI MASU JAN HANKALI BAN TAUSAYI ZALLAR SOYAYYA MARA MANTUWA_
*KINSAN SUNAN LABARAN?,.....GASU KAMAR HAKA*
FURAR DANKO
Billyn Abdul
-ZAFIN KAI
Mamuhgee
-TABARMAR ‘KASHI
Safiyya Huguma
-BAKON MUNAFIKI
Miss xoxo
Duka hudu 1k
Uku 800
Biyu 600
Daya 400
Pay at👇
1487616276
Access Bank
Bilkisa Ibrahim Musa
Sai katura shedar biyanka anan👇
09032345899
Idan katin waya ne kuma saika tura anan👇
09033181070
*_karki bari ayi tafiyar ZAFAFA BIYAR BABU KE!!!_*
*THANKS FOR CHOOSING US*🥰
Zafafa🫶🔥
*_ALLAH ya gafartama iyayenmu😭🙏_*
𝐓𝐲𝐩𝐢𝐧𝐠📲
🫗 𝙁𝙐𝙍𝘼𝙍 𝘿𝘼𝙉𝙆'𝙊.....!!🫗
𝑩𝒊𝒍𝒚𝒏 𝑨𝒃𝒅𝒖𝒍𝒍 𝒄𝒆🤙🏻
𝕭𝖔𝖔𝖐 𝖙𝖜𝖔
𝑪𝒉𝒂𝒑𝒕𝒆𝒓 2️⃣1️⃣