← Book details A Dalilin Matar Uba Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 9 OF 28

Sashe 9

A Dalilin Matar Uba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Hajiya sa'adatu Tace to amma anya Zan iya kuwa, Yalwa tace meye wani bazaki iyaba kika kashe uwarsu balle su kananan alhaki, So nakefa kema ki shiga gari a dinga ce miki Hajiyan Alhaji... Makkah duk karshen wata,

"sa'adatu tace hahah sai yasa nake sonki fa akwai bani karfin gwiwa, Yalwa tadan harareta tace kima tsaya nan ina fada miki xeey dinnan tana shiga Universty Idon ta budewa zaiyi da kawaye karshe ma may be ba anan Zatai school ba kinga kuwa Da wuya ki iya juyata ko kuma karshe ma Yace ze aurar da ita kinga ba daman aiwatar da abun da nakeso muyi,

Sa'adatu tace eh kuma hakane yar uwa... Yalwa tace kiramun Ita kiga yanda zaki fara.......

``` Kuci gaba da kasancewa Dani```

Xeexee
[11/7, 6:55 AM] Ummiey Xeey Abakson💋: *_ ∆°°••~❣_💞••💙💓❤💛
*A DALILIN MATAR*
*UBA*
*_ ∆°°••~~❣_💞••💙💓❤💛

```STORY & WRITTEN BY```
*Ummiey_Xeey Abakson*💋

*♻EXCLUSIVE WRITER'S FORUM​*
[ɦօʍɛ օʄ քɛaċɛ, ɦօռօʊʀ aռɖ sʊքɛʀ աʀɨtɛʀ's]

*LIKES AND DROP YOUR COMMENTS*
F B.. #https://www.facebook.com/Exclusive-Writers-Forum-E-W-F-1922297541423276/

*OCTOBER 2017*
_SHORT STORY_

```SADAUKARWA GA____```
*MARIAM TIJJANI ADAM*😍

_The More I Meet U The More U Appear New.. The More I Know U The More I Want To Love U.. Each Day My Love For U Is My First Love....Bcoz, Each Day I Feel As If I Have Just Started loving U..!_
MISSING YOU MY *EMNOOR AHMERD DON*👄

*PAGE📄31__32*

Yalwa tace kiramun Ita kiga yanda zaki Fara, Sa'adatune ta tashi zata fita kiranta, "yalwa dariya tayi tace ai seta rainaki wlhi, Daganan zaki kwalla mata kira basai kin wahalar da kankiba....

"sa'adatune ta kwalla wa Xeeeyxeey kira har sau Uku, xeey nachan na bacci Bata jiba a fusace yalwa ta tashi ta shiga dakin ta bubbuga gado tace kee bakiji *MATAR UBANKI* na kiranki Bane?

Firgigit Xeey ta tashi tace hajiya wlhi banji bane tace to maza kije tana kiranki, Xeey da bacci be gama sakenta ba ta nufa Dakin Hajiya sa'adatu Ta sama waje ta tsugunna yalwa ta Bude baki tace ke haka wai aka koya miki Kinbar bayi duk wari maza kije ki wanke kuma kina gamawa Ki share wajen flowers duk Yayi datti ko kina jiran masu aikine bayan kina kwance ba abun da kikeyi,

"xeey Tace Ok bari naje na wanke ta tashi ta nufa bayin ta tsugunna kenan ta tino da furucin matar Nan wai ba'akoya mata bane, dazu kuma tace haka aka koya musu tarbiya? Hawayene masu zafi suka fito daga idonta amma ta daure wata xuciyan tace karki kuka tunda ba *MATAR ubanku* bane tace miki haka, dan haka tai abun da zatai ta gama ta koma daki time din la'asar yayi tayi alwala tai sallah ta dakko uniform dinta tai musu sallama Ta tafi islamiya..

"Yalwa tace to kinga abun da nayi dai nida ba matar gidan ba; haka zaki dinga mata da ita da kaninta dan ke basa'arsu bace "hajiya sa'adatu Tace to indai wannan ne ba damuwa sosai karkiji komai munanan zan baki labari uwar dakina. Sukaci abinci sukai Sallah yalwa Ta tafi gidanta.....

*WASHE GARI*
tun asuba sa'adatu ta tashi amma taki tashin su xeey, dama akwai abun data ayyana a xuciyanta dan haka Ta tashi ta dafa ruwan tea dinta tana da bread da kayan tea a daki taci ta koshi ta koma baccinta hankali kwance....

"Abba ne ya fara tashi yaga gari duk yai haske, Allah yasama ran sunday ne ba school da yau kam bazasuje school ba, Kofa yai ma xeey knocking itama ta window taga gari yayi haske sosai, bude kofa tayi Tace bro yau mun makara ka bugawa anty kofa bari nai alwala nai sallah...

"Abba ya tafi yaje yana mata knocking budan bakinta tace waye ke bugamun kofa kamar yana neman abu a wajena..

"abba yai smiling yace anty mun makara tace toh naji ai tun tuni na farka kasan ku yan gayune bakwa tashi da wuri sai gari yai haske,

"abba yace laa Aunty ko sallah fa bamuyi ba da munyi sallah se mukai 10am indai weekend ne yana magana da raha,

"sa'adatu tace sai kayi kuma karka sake damuna kana jiko,

_Abba yai matukar mamakin maganganunta bece komai ba ya wuce yai sallah yazo yai wanka ya zauna yafara nazarin maganar *MATAN UBANsu* tsaki yayi dan abba yarone bameson damuwa ba, laptop dinshi ya dakko ya fara dube dubenshi, Har 10am beji Ance mai ga breakfast ba dan haka ya tashi ya nufa Dakin Xeey,

"A kwance ya sameta da alama bacci takeyi dan ba karamin gajiya tayi Jiya ba, yace sist nifa yunwa nakeji tace haa Aunty batai breakfast Bane bro? Yace banga alama ba gaskiya Tace ok bari naje na tambayo yace ok Sist

Fitowa xee tayi taga ko ina duk datti, da alama bata gyara Ko inaba, dakin step mum din taje ta tura tai sa'a a bude yake shiga xeey tayi ta gaisheta ta amsa a wulakance tun daganan Jikinta ya fara sanyi, Tace amm uhmm Aunty bamuga Abincin break fast din muba,

wani harara sa'adatu ta jefo mata tace sannu mulkakko da mai dama an ajiyeni ne dan na dinga muku girko or what, To banyiba kuma Bazan yiba infact duk aikin gidan nan ke zaki dingayi, Ba ruwan masu aiki, Munafukan yara kawai,

Me sukai kuma na munafunci kuma, wani kuka xeey ta sake a dakin Dan batasan me sukai mata ba lalle rashin Uwa gaskiyane, Jin kukantane Yasa Abba ya shugo dan ganin me ya faru, Yana shuguwa suka hada ido da Sa'adatu dukda yarone tadan tsorata dan namiji duk kankantarshi na mijini, karfin hali tayi tace fitan mun a daki, kaima kazo munafuncin kenan, Kamar zaiyi magana seyai shuru yace xeey sorry Allah nanan, ya fita a gidan dan abba nada zuciya dukda yarone,

Xeey kam itama tashi tayi ta nufa dakinta kanta ta chusa cikin pillow ta fara Kuka me tsananin taba zuciya, sedataci kukanta ta gama sannan ta tashi ta gyara ko ina dan idan ma batai abincin break fast ba su zasu wahala ita da bro dinta dan haka ta sama xuciyarta Salama akan yanzu dole ta dinga girki, wunin ranar aiki taci sosai dan badama Ta zauna se sa'adatu ta jajubo mata aiki........

Bayan kwana biyu ran da dad zai dawo kuma sukaga Akasin Haka, Ranar Tun asuba Hajiya sa'adatu ta Tashi tai duk wani aiki da tasan mijinta zai yaba, Su xeey da abba sukace Allah sarki mamansu, Tace abba yaje yai wanka xeey ma haka ta dakko musu kaya me kyau suka sa tasa musu abinci sukaci sosai kamar ba ita kwanakin biyu baya ba ta chanza musu kai mata akwai makirci wallahi....

"itama taci kwalliyarta tace suzo su zauna dad yau xe dawo, basuce mata komai ba sukazo suka Zauna suma...amma Se kallon juna abba da xeey sukeyi dan kowa nada abun cewa a xuciyarsa......

*TEAM XEEY*
[11/7, 6:55 AM] Ummiey Xeey Abakson💋: *_ ∆°°••~❣_💞••💙💓❤💛
*A DALILIN MATAR*
*UBA*
*_ ∆°°••~~❣_💞••💙💓❤💛

```STORY & WRITTEN BY```
*Ummiey_Xeey Abakson*💋

*♻EXCLUSIVE WRITER'S FORUM​*
[ɦօʍɛ օʄ քɛaċɛ, ɦօռօʊʀ aռɖ sʊքɛʀ աʀɨtɛʀ's]

*LIKES AND DROP AND YOUR COMMENTS*
FB.. #https://www.facebook.com/Exclusive-Writers-Forum-E-W-F-1922297541423276/

*OCTOBER 2017*
_SHORT STORY_

```SADAUKARWA GA____```
*MARIAM TIJJANI ADAM*😍

*°°°•••YAR GATA NAH•••°°°*
💞💞💞
When I See Your Smile.
And Know That,
It Is For Me,
That Is When I Will,
Miss You The Most..
*I MISS YOU MY REAL KHADY*

*PAGE 📄33___34*

_ Suna Zaune a pallon su ne da yasha gyara ko ina se kamshin turaren Dan maiduguri yakeyi.

"daddy ne ya kira Xeey a waya yace mun sauka fa wani tsalle xeey tayi tace Aunty daddy is back, itama murmushi tayi tace Yeah Dama yace 10AM zasu sauka, malan mukhtar ai sunje dakkowashi, "Abba ma smiling yayi dan atleast Zaiga beloved dad dinshi...

Suna zaune suna kallo sukaji alamun an bude gate, da gudu suka fito dan yiwa dadynso Oyoyoo, ware hannunsu Dad yayi alamun oyoyo suma haka Sukazo se murna sukeyi,

"Hajiya sa'adatu kam bata fitoba tana ta lekensu ta window tace Zakuci ubankune yara.... Lolx..

__tana zaune dad ya shugo wani murmushi ta sakar mai hade da juya ido alamun tayi missing dinshi, Shima dad murmushi ya mayar mata dashi, yazo ya sama waje ya zauna a kujere xeey na hannun dama Abba na hannun hagu, Sake AC akayi dan dad yace ya gaji gashi yunwa yakeyi dan haka ya sakko kasa ya baje yaci abinci sosai, sannan yanata kollon yaranshi Sun dan rame amma yai tinanin ko duk rasuwar mahaifiyarsune dan besan abun dake faruwa ba, Yasa yai shuru:

"bayan yaci abinci suka taba hira sosai sannan ya shiga wanka daganan ya wuce daki dan hutawa, yanajin sanyin Ac bacci ya kwasheshi,

"hajiya sa'adatu bayan mijinta ya shiga daki ta tattara ko ina ta sake Saka wani tilaren tai wanke wanke tadan dora mai Doya dakwai na Anjuma dan best food din alhaji kenan.. Abba da xeey kam se kallon ikon Allah suke suma ba daman magana,

************ bangaren ismail kuwa be zama sosai dan zirga zirga yakeyi sosai yanzu Dan ya kusan barin kasar zai tafi Egypt karatu, Ismail ne yau zaune a daki yau kusan 4days bega xeey ba kuma ko ya kira numbernta Akashe dakko drawing dinnan da yayi ya kalla Yace a Zuciyanshi soon to miss you my baby sister, kawai yaji kwalla na shirin zubomai wata xuciya tace haba Ismail kaida namijine be dace daga tinanin mace ka fara kuka ba dan haka ya dakko wani *memo* guda biyu ya fara rubuta Love words duk abun da ya rubuta a daya seya rubuta a daya duka memon Rubuta iri dayane Sak sedai daya ismail ne daya kuma Xeey

Seda ya gama Tsab ya fesheshi da turare kamar wata mace yace insha Allah se randa zan tafi school zan baki ya bude wani dan karamin kit din da dad dinshi ya siyo mai mekyau, Ya saka dawowa kan gado yayi rub da ciki se tinanin Xee yake xuciyanshi na fadamai indai beganta yau ba akwai matsala.....

___Da daddarene su xeey suna pallow sega wani yaro yace wai ana kiran Xeey inji ismail, Ta tashi ta dakko hijabinta tace yanzu zata dawo,
Chapter 9 · 0% Book details