← Book details A Dalilin Matar Uba Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 17 OF 28

Sashe 17

A Dalilin Matar Uba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ismail yace naji din, jirani na watsa ruwa mu fita tare Dan zama mutun daya ba dadi, Fahad yace alright my frnd, nan Ismail ya shiga wanka, be dadeba ya fito, yasa wani riga me dogon hannu se wando blue jeans yamai kyau sosai, kafin su fita ne ya dakko *MEMO​* ya duba yai smiling sannan yai kissing din memo din

Fahad kam kallon shi ya tsaya yi yace lol...love wan kill person, Ismail yace eh din naji, let's go, suka kama hanya dan fita shan iska

*​A KADUNA KUMA​*
Mummyn Ismail itama kullun addua take ma d'anta, in Alherine Allah yasa su hadu da xeey inba alheri bane Allah ya ciremai sonta, Dan tsoro takeji kar d'anta ya kamo da heart problem...!

Bangaren Su xeey kuma, Alhamdulillah sauk'i na samuwa, Dan kullun se hajiya tai mata adduoi

Safiyar ran jumma'a, bayan hajiya tai ma xeey addu'a kamar yanda akace mata, yayan Afrah na shirin fita office, daddyn su afrah kuma yana daki Dan yazo Hutu,

Ihu sukaji me karfi a dakin xeey, gaba dayansu suka fito, yayan Afrah kuma daga shi sai towel ya fito daga wanka lolz.. daddy ne yace kallekafa, nan kunya ta kamashi ya koma daki ya sa jallabiya hahaha
Bayan yasa jallabiya se kunya yakeji kamar bazai fitoba, hakadai yayi ta maza ya fuske ya fito, koda ya shiga room din su xeey, yanda yabar su mommy haka yazo ya taddasu

"Xeey CE tarik'e kanta se kuka takeyi,

Mummy ce taje kusa sa ita ta kamata tace menene y'ata?

Daddy ne yace" yace in banda abunki hajiya, yarinyar da bata magana taya zata amsaki?

Kawai jin maganar da basui tsammani ba sukaji *XEEY* tace "inajinku inane nan?

Duka dakin suka hada Baki sukace *Alhamdulillah* *Alhamdulillah* Sannu xeey, kuka ta k'ara tsakewa tana cewa wayyo kaina, wayyo kaina, kowa na dakin tausaya mata yayi, mummy kam har da Yar kwallanta,

Daddy ne tace " haba hajiya meye na kuka, ai godewa Allah zamuyi tunda Gashi ta fara magana, shikam yayan Afrah tsayawa yayi yana ganin ikon Allah... _tabbas duk Wanda ya r'ike Allah zaiga haske_

Xeey kam in banda kuka ba abun da da takeyi, mummy CE tace hana y'ata kidena kuka mana

Daddy ne ya kalla xeey cikin tausayawa yace" Hajiya ki barta ta koka, Allah kadai yasan wahalan da ta tsince kanta, Mummy CE "tace Hakane amma Dan Allah ki dena damuwa muna tare dake,

Xeey binsu da kallo kawai tayi ta daga kai alamun To, sannan suka bar dakin, pallow dukkansu sukaje suka zauna,

yayan afrah kuma se jinjina abun yake, Dan kar ayi bashi, ya dauka wayarshi, ya kira frnd dinshi, yake sanar dashi bazai Iya zuwa office ba, abokinshi yace OK Allah yasa dai lafiya, yace" eh lafiya lau sai dai Monday idan mun hadu, nan sukai Sallama
Daddy ne yace ha'a my son meyasa bazakaje office dinba

Yayan afrah ya shafa keya yace uhm dad banso ayi banine, nasan zamu bukaci jin labarinta

Daddy yai murmushi yace kai my son, mummy ma itama maganar ya bata dariya

Suna zaune a pallow din xeey kam na daki, se kallon dakin takeyi, tashi tayi ta zaga ko ina na dakin, wani babban hoto ta gani a Dakin enlargement, wata kyakkyawar yarinya tagani, a zuciyarta tace to WACECE WANNAN?

ganin bame bata amsane yasa ta k'ura wa pic din ido, can kuma ta tino da Dan uwanta Abba da mahaifirta, dasu Ismail da auntyn ta Mariam Tijjani, nan ta saka wani kuka me taba zuciya

Su mummy kuma suna pallow, ta dauka waya tai dialing number Afrah, take CE mata wani babban farin ciki ya samemu, bata ida magana ba sukaji kukan xeey tuni, suka rude suka nufa dakin da Xeey take, shiga sukayi suka sameta a gefen gado, mummy CE ta dafata tace Y'ata ba kuka bane solution kinji, kiyi shuru

Ku ci gaba da kasan cewa dani

*Ummiey xeey CE* kema kowa fatan Alheri
[1/3, 8:30 AM] UⓂmiey Xeey👄: *_ ∆°°••~❣_💞••💙💓❤💛
*A DALILIN MATAR​​​​*
*UBA​​​​*
*_ ∆°°••~~❣_💞••💙💓❤💛

```​​​​​​​​​​​​STORY & WRITTEN BY​​​​​​​​​​​​```
*​​​​Ummiey_Xeey Abakson​💋​​​*

*​​​​♻EXCLUSIVE WRITER'S FORUM​​​​*
_[ɦօʍɛ օʄ քɛaċɛ, ɦօռօʊʀ aռɖ sʊքɛʀ աʀɨtɛʀ's]_

*​​LIKES AND DROP YOUR COMMENTs​​*
FB..#https://www.facebook.com/Exclusive-Writers-Fans-E-W-F-1922297541423276/

```​​​​​​​​​SADAUKARWA GA____​​​​​​​​​```
*​​​​MARIAM TIJJANI ADAM​😍​​​*

```Dedicated to my dear bilkisu BK😍 nagode da soyayya Allah ya bamu tare```
*Allah ya Baki lafiya me amfani, Allah yasa kaffrane*

*PAGE 63__64*

Kuka Xeey take yi mai ratsa zuciya, mummy ce ta rungume ta tana shafa bayanta ta sigar lallashi har aka samu tayi shiru tana ta sauke nannauyar ajiyar zuciya sannan daddy yace" ki daure ki sanar damu wacece ke?

kokarin tattara nutsuwar ta waje daya tayi sannan ta kwashe labarinta tun daga farko har karshe mummy ce ke zubda kwalla sannan ta sanar da Xeey a halin da suka tsince ta da kuma bata labarin Afrah ta fada mata itace silar zamanta a gidan nan sannan tace ki kwantar da hankalin ki Xeey kici gaba da addu,a komi yayi zafi maganin sa Allah kuma nayi miki alqawari insha Allah Indai Kina tare dani ba zaki yi kukan Maraici ba, kuka Xeey taci gaba dayi tare da kuma rungume mummy.

*********************
Mariam ce zaune a pallow ta rasa meke mata dadi firgigit ta mike tace wai meke faruwa ne yaushe rabon dana je na naga lafiyar niece dita *Xeey*anya banci amanar zumunci ba nayi wa kaina adalci kuwa hawaye masu zafi ne ke bin kuncinta tashi tayi ta dauki wayarta ta latsa number mijinta ringing daya aka dauka ta bayyana masa zata ganin *Xeey* amsa mata yayi da ta gaida mata su, da isar ta gidan horn daya tayi gate man ya bude mata ta shiga parking tayi tare da knocking kofar pallow hajiya Sa,adatu ce ta bude mata tare da watsa mata kallon wulaqanci meya kawo ki gida na ina ce babu komai naki a gidan nan *Xeey* ce kike takama da ita ko kuma ta dade da tafiya yawon duniyar ta don haka bani da lokacin ki juyowar da Sa,adatu zata yi

*Mariam* ta wanke mata fuskanta da Mari ta hagu ta dama wanda saida taga wuta, kuma ta kara da cewa" shegiya kin kashe min yar uwa sannan kice bakisan inda yata take ba wallahi ba zaiyu ba duk inda take ki fito min da ita kafin 24hours fuuuuuuuu taja motar ta tabar gidan

Hajiya Sa,adatu kam tsaye tayi r'ike da kunci tana ajiyar zuciya zabura tayi ta dauki waya ta kira yalwa cikin minti 10 sai ga yalwa ta iso labarin duk abinda ya wakana da tsakanin ta da Mariam tayi jinjina kai yalwa tayi tare da kyabe baki tace babban magana...!

Sa'datu tace" dan Allah ki temakeni, Yalwa tace" kinsan bakya gayawa Alhaji wannan magana ba Kinsan sharadin boka ne wannan don dakin fadi abinda ya shafi waccan matacciyar zance zaisha bambam ayi babu ke hakuri zaki yi, tunda yanzu da zance Ki kawo wata dubu Dari saiki ce baki da Ita da kinga aiki da cikawa.

Da fitar *Mariam*bata tsaya a ko ina ba sai gidansu daddyn Xeey (mahaifitar babban xeey) Sallama tayi da fara,a hajiyar ta tarbe ta tare da bata juice da ruwa mai sanyi gaisawa suka yi sannan Mariam ta sanar mata da abinda ya faru tsakanin ta da hajiya Sa,adatu shiyasa tazo neman Xeey ko tana nan kuka hajiyar ta saki tana fadin *innalillahi wa,inna ilaihirraji,un*wallahi na manta da wata Xeey *A DALILIN MATAR UBA*yanzu an rusa mata rayuwa ni rabon dana sa daddyn nata a idona harna manta saboda yafi shekara daya dana sashi a ido kuma duk wata hidima da kika san yana yimin Sa,adatu ta hana shi kannansa ma da suka je gaida shi cewa yayi bai sansu ba yanzu muje muyi ta addu,a duk inda *Xeey*take Allah ya bayyana mana ita yau na sake shiga wani tashin hankalin ni khadija.
*************************
Daddy ne zaune a Office sai juya biro yake ya rasa meke yi masa dadi ya tafi tunani amma ya rasa wai meye ke faruwa dashi??? Wunin ranar bai iya tabuka wani abun kirki ba gida ya dawo Sa,adatu ta tarbe shi cikin kissa daga mata hannu yayi alamar ta dakata saroro tayi dakinsa ya shige tare da murza key zaga dakin ya rinka yi ba tare da ya sami solution ba
***********************
*xeey*ce kwance a pallow tana kallon TV amma zuciyarta ba nan take Kallo ba tana can wajen tunanin daddyn ta Aunty mariam da isma,il dinta Wanda hawaye ke biyo kuncinta wanda bata san yana zubowa ba Maganar da kisa sunan yayan Afrah haba my beloved sister meke faruwa ba zaki karbi nasihar da Mum ta miki ba hadiye kukanta tayi tare da cewa yaya bawai ban amsa nisihar bane wallahi wani Abu nake tinawa sai yasa

Yayan Afrah yaj itausayinta sosai yace........

Ummiey XEEY
[1/3, 8:30 AM] UⓂmiey Xeey👄: *_ ∆°°••~❣_💞••💙💓❤💛
*A DALILIN MATAR​​​​*
*UBA​​​​*
*_ ∆°°••~~❣_💞••💙💓❤💛

```​​​​​​​​​​​​STORY & WRITTEN BY​​​​​​​​​​​​```
*​​​​Ummiey_Xeey Abakson​💋​​​*

*​​​​♻EXCLUSIVE WRITER'S FORUM​​​​*
_[ɦօʍɛ օʄ քɛaċɛ, ɦօռօʊʀ aռɖ sʊքɛʀ աʀɨtɛʀ's]_

*​​LIKES AND DROP YOUR COMMENTs​​*
FB..#https://www.facebook.com/Exclusive-Writers-Fans-E-W-F-1922297541423276/

```​​​​​​​​​SADAUKARWA GA____​​​​​​​​​```
*​​​​MARIAM TIJJANI ADAM​😍​​​*

_Dedicated to my dear sweet heart, Khady fresh💞..thanks for your love and support_

*PAGE 65_66*
Yayan Afrah ne yaji tausayinta sosai yace" duk da bansan meke damunkiba amma ki kwantar da hankalinki, muna tare dake, komai yayi farko zaiyi k'arshe, Xeey CE tace" uhm Hakane tnx for your advice, yace" Never mind dear, ciro hankacif yayi ya bata yace" ta share hawayenta, ta amso ta share, sannan shima ya zauna sukai kallon tare amma yana lura da ita ba wani sakewa tayiba, kallo daya zakai mata kasan tana cikin tinani matuka

Suna cikin zaune ne mummy ta shugo ta samesu tace" haa meya farune naga kamar Xeey tayi kuka, bro yace" lol wlhi kuwa, mummy CE ta rungumeta tana dai ta bata hakuri, nan sukai hira sosai, mummy har tana kiran Afrah suka gaisa, itama Afrah ta k'ara ba xeey hakuri Dan gane da halin da take ciki....!
Chapter 17 · 0% Book details