← Book details A Dalilin Matar Uba Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 25 OF 28

Sashe 25

A Dalilin Matar Uba Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Da fitarshi Afrah taje kusa dq Xeey tana ta bata hakuri akan ta dena kuka koma menene duk da ita Afrah batasan meke faruwa ba! Zeey tace ok nan tai shuru, misalin karfe 11ne kowa ya sama inda zai kwanta se bacci, Isma'il ne Yana kwance se hamdala yakeyi Dan wani natsuwa yaji a jikinshi kamar ba abun da yake damunshi, ranshi fess yayi bacci

Cikin dare ne Xeey ta farka tanajin yunwa, mikewa tayi ta kunna filatar dakin taga kowa na bacci, kuma motsinta besa kowa ya tashi ba dan sun gaji gaskiya! Takawa tayi ahankali taje daidai gadon da aka kwantar da Isma'il, K'ura mai ido tayi taji inama ya farka yanzu suyi magana koda sau daya ne, Hakanan ta dinga kallonsa seda ta kusan 20mins akanshi sannan ta wuce ta eba abinci tashi ta sha ruwa sannan ta koma kan gadon itama se hamdala takeyi dan Taga Sahibinta....

*WASHE GARI*
tun Wuri Dr musaddiq ya tashi yaje tai dressing na doctor, suma suka tashi nan nurses suka shugo suka basu medication dinsu na 8am...Alhamdulillah jikinsu da sauk'i dama ba wani ciwo bane suma ne kowa yaji sauk'i sai son barka!
Musaddiq ne zaune suna hira da Isma'il a office din su Dan yanzu Isma'il kunyar su Maman Afrah yakeji Dan be iya zama a ward din da aka kwantar dashi! Suna zaune ne Fatima Zahra ta kira musaddiq tana tambayarshi me yasa kwana biyu baya picking ko reply din text idan ya gani, Musaddiq yace afuwan babban Aminina ne ba Lafiya, Tace" Allah sarki, Allah ya kara Lafiya may be inshugo dubashi, yace" Ameen Ok...Isma'il yace" Angon Fatima, musaddiq yai dariya yace kai kumafa??? Nan dai suketa hiransu

Kwanan Su Isma'il biyu aka sallamesu dukansu aka tsayar da magana Iyayan Isma'il zasuzo Gobe Dan fayyace duk abubuwan da ke tsakanin Xeey da Isma'il, Da kuma yanda akai Xeey tazo gidansu musaddiq!

Su Xeey suna zuwa gida abba (baban Afrah) ya kirata yake jirgin dare zaibi insha Allah meeting din da za ai gobe zai halarta, yaji komai so ta kwantar da hankalinta tace" ok Abba
Bangaren Isma'il shima suna dawowa gida mummy se congrats suke mai, Yace" Adduan ku shi ya Bini, dama mum kullun adduan Allah yasa muga na kike, mum tai murmushi tace hakane my Son! Nan take ya Ciro wayarshi y kira Anty *MARIAM TIJJANI* Tana zaune da mijinta suna hiran soyayya Sega call dinshi, tana dubawa taga *Isma'il din Xeey* Sunan datai saving kenan da number dinshi, Alhaji mijinta yace" pick up, nan ta dannan answer ya gaiaheta cikin natsuwa, Yace" Anty Albishirinki tace" Goro Yace" Wallahi naga Xeey! Alhamdulillah tace" sannan tace ganinan Zuwa! Isma'il yace" Anty ki zamanki gobe Insha Allah ma zamu hadu a malali Ghana road gidan dq Xeey din take kenan! Tace" alhamdulillah Allah ya kaimu yace" Ameen, Nan itama ta fara hamdala kowa dai ranar ya kwana da Farin ciki banda masoya biyu Isma'il da Xeey Wanda ko gyangyadi yaqi daukarsu, Haka suka kwana cikin tinani da kaunar junansu har gari ya waye!
Washe gari kowa ya tashi su Afrah da Xeey da Maman su suka gyra ko ina Dan tarban baki! Anyi abinci kala kala misalin karfe 10am Sega Anty Mariam ta sauka a gidan su Afrah, Xeey na ganinta da gudu taje ta rungumeta tanata kuka Xeey, mman Afrah tace waye wannan Xeey? Xeey tace kanwar mahaifiyatane nan sai suketa Yana kuke kuke har sunfara labari sega yan gidan su Isma'il, nan duka falon yadau Hamdala Dan duk Wanda akeso su hadu Alhamdulillah sun hadu, kamar su Baban Afrah, Maman su, Afrah musaddiq se ita Xeey, se mman Isma'il da babanshi dashi kanshi Isma'il se Kanwar Maman Xeey wato Mariam Tijjani da mijinta, Maza manya 3 mata ma haka!
Nan aka budeu wajen da addua

Mariam ta fara bada labarin tun daga kan tasowar Xeey har irin wahalan Da Xeey tasha wajen *matar uba* yanda matar uban ta rabata da Isma'il da duk yan uwanta, Baban su Afrah yace" Alhamdulillah to muma dai nan muna zaune wannan yarinyar ya nuna Afrah yace" ta sanadiyyarta tazo gidan nan har Allah yasa suka hadu da Isma'il.....nan akaima Afrah godiya sosai da dabiun ta na gari, nan dai aka yanke shawarar za'aba Isma'il Xeey tunda soyayyar su ta Dade so ba abun da'a jira, kowa ya amince da hakan Mariam tace" wannan shawarar tayi, baban Su musaddiq yace" ubanta ai nanan ko? Akace Eh nan suka mik'e zasu tafi gidan Su baban Xeey

UMMIEY Xeey
[1/21, 10:34 PM] ©REAL UMMIEY XEEY: *_ ∆°°••~❣_💞••💙💓❤💛
*A DALILIN MATAR​​​​*
*UBA​​​​*
*_ ∆°°••~❣_💞••💙💓❤💛

```​​​​​​​​​​​​STORY & WRITTEN BY​​​​​​​​​​​​```
*​​​​Ummiey_Xeey Abakson​💋​​​*

*​​​​♻EXCLUSIVE WRITER'S FORUM​​​​*
_[ɦօʍɛ օʄ քɛaċɛ, ɦօռօʊʀ aռɖ sʊքɛʀ աʀɨtɛʀ's]_

*​​LIKES AND DROP YOUR COMMENTs​​*
FB..#https://www.facebook.com/Exclusive-Writers-Fans-E-W-F-1922297541423276/

```​​​​​​​​​SADAUKARWA GA____​​​​​​​​​```
*​​​​MARIAM TIJJANI ADAM​*

*Dedicated to All lovers of the world....❣❣❣❣*

*PAGE 97....98*

baban Su musaddiq yace" ubanta ai nanan ko? Akace Eh nan suka mik'e zasu tafi gidan Su baban Xeey, dukansu sun fita Se Xeey da Isma'il wani kallo yai mata da ita kanta tasan she's missed him, Yana mata kallon shima ya fita itama tabiyo bayanshi!
Mota suka hau suna tafe Afrah se Jan Xeey da hira take wai she's lucky gaskiya! Musaddiq yace ki tsaya wasa yarinya kema karki fito da miji, Isma'il kam shuru yayi se kallon Xeey yaketayi ta mirror, ita ko Xeey in banda fargaba da tsoron fitinar matar ubanta da zasuje ta tadda ba abun da takeyi...minti kadan suka karasa gidan tofaa!

Saukowa sukayi su mazan suka tsaya a waje Matan suka shiga mezai faru! Hajiya Sa'adatu tana ganin Mariam Tijjani gabanta yai mugun fadi, batama lura dq Xeey ba tace was Maryam" oh yau kinmun gayyane to ku fitar mun a gida maza maza, sudai mu mummyn Afrah kallonta suka tsaya sunayi sukace ba shakka wannan muguwar *matar ubace* Mariam tace" matsalarki, hajiya Sa'adatu tace" matsalar ku dai chan tunda Xeey ba dawowa zatai ba ta mutu!!! Maman Su Afrah ne tai dariya tace lalle kuwa kudirinki yau ya karye ga Xeey nan bata mutuba da ranta! Kallon Xeey tayi tsab tabbas itace wani mugun faduwar gaba taji, Alhaji baban Xeey, Yana daki yanajin an ambato Xeey wuf ya fito, Xeey na ganin babanta da gudu taje ta rungumeshi sai kuka, jin gidan ya kaure ne da maganganu da koke koke mazan suka suka shugo, hajiya Sa'adatu taga yau karyarta ya kare a Fasa kuka ba Wanda ya saurareta, Maman Isma'il binta da kallo tayi tace" makira!!!

Nan Baban Isma'il yace" Alhaji ba zamu mukazoyi ba, kamar daga sama Alhaji yaji ya dawo dai dai bisa adduo'in da yasha, baban Isma'il yace" tabbas mun DDE da nemanka da inda kake, nan dai suka bashi labarin from A to Z na wahalar da Xeey tayi *a Dalilin matar uba* nan baban Xeey yaci kuka yace ba da saninshi bane, har suna hada baki sukace tabbas munsani sai yasa mukai maka uziri! Yqnzu munzo maganar auran Isma'il ne da Xeey mun yanke komai in kuma kanada magana ne kayi
Nan baban Xeey yace" ai sungama mai komai, hajiya Sa'adatu tanajin labarin Xeey zatai aure nan fa fara wasu kururuwa tana Fasa kayan dakinta, sukai banza da ita Ashe dai Hajiya Sa'adatu ta hau kace ne. Kaikayi ya koma kan mashekiya kenan Alhamdulillah!
Bban Xeey yace gaba da musu godiya sukace bakomai" yace" abarmai Xeey, Sukace a'a zasu tafi da ita Dan bazasu bari wannan matar ta sake ma Xeey lahani ba Dan haka sukace an tsayar da biki nan da Wata uku, yayi murna sosai sunfito shima ya futo wajen neman Yar uwanshi.....suna fitowa sega Sa'adatu ta rugu da gudu waje ta tara bola se tsalle takeyi, kowa sedai ya kyalleta yace" Allah ya kyauta Dan kana ganinta kasan mugun abun da tai ya koma mata

Dan haka suka tafi da XEEY shima yabar mata gidan har abada yaje nemen yan uwanshi da basu labarin nan me dadi!

Tun a wajen kowa yai sallama dan no need su koma gidan su Afrah! Maman Isma'il da babanshi suna tafe suna hiransu, Mariam ma haka, baban su musaddiq shima tare da matarshi, se Musaddiq da yake driving dinsu Afrah, Zeey da Isma'il suna tafe suna hira basu tsya ko inaba se gidan su musaddiq nan kowa ya huta

*BAYAN SATI DAYA* hankalin kowa. Kwance matsalar dake damun kowa Allah y kawo karshenshi, itama yanzu Afrah Ta sama wani lecturer Abdulrasheed Yana sonta dan aure sai yasa duka aka tsayar da bikinsu rana daya! Kowa abun yamai dadi Matuka!

Akwai wata ranane Isma'il yazo gidansu musaddiq suna zaune musaddiq yace" abokina bari inzo mu tafi ko? Isma'il yace" ina kenan fa? Musaddiq yace" wajen Fatima mana! Isma'il yai dariya harda rik'e ciki yace" tab yau soyayya zansha da baby Xeey kullun nazo tare muke hira all yau nida itane! Musaddiq yace" ohhh nikam kaga tafiyata, Yana fitowa yaga Afrah da saurayinta lecturer Abdulrasheedl! Shidai yai gaba Isma'il ya shiga har falon Su Xeey ya kirata!!!!!!!!!

Kuci gaba da biyoni

Ummiey Xeey Ce
[1/21, 10:34 PM] ©REAL UMMIEY XEEY: *_ ∆°°••~❣_💞••💙💓❤💛
*A DALILIN MATAR​​​​*
*UBA​​​​*
*_ ∆°°••~❣_💞••💙💓❤💛

```​​​​​​​​​​​​STORY & WRITTEN BY​​​​​​​​​​​​```
*​​​​Ummiey_Xeey Abakson​💋​​​*

*​​​​♻EXCLUSIVE WRITER'S FORUM​​​​*
_[ɦօʍɛ օʄ քɛaċɛ, ɦօռօʊʀ aռɖ sʊքɛʀ աʀɨtɛʀ's]_

*​​LIKES AND DROP YOUR COMMENTs​​*
FB..#https://www.facebook.com/Exclusive-Writers-Fans-E-W-F-1922297541423276/

```​​​​​​​​​SADAUKARWA GA____​​​​​​​​​```
*​​​​MARIAM TIJJANI ADAM​*

*101...102*
Gabanshine yai mugun fadi, yaji duk bazai ma iya zuwa office din ba nan ya fada gado!!!
Shuru Shuru musaddiq yaga Isma'il bezo office ba Dan haka ya dauka wayarshi ya kira! Har ya gama ringing ba'a daukaba, ya sake kira chan Isma'il ya dauka muryanshi har wani shakewa yakeyi, Musaddiq yace" Isma'il what's wrong? Isma'il saboda bugun kirji ya kasa cewa komai! Musaddiq ya sake tambayarshi, shuru jin shurun da yayine yace" a office dinsu yna zuwa! Ko 20 mins ba ai ba Sega musaddiq gidansu Isma'il, direct dakinshi ya wuce ya sameshi kan gado se nishi yakeyi! Musaddiq ne ya tallabo Isma'il Yana tambayarshi meya faru! Isma'il yace" aboki shine zaka cuce rayuta Ashe Xeey da wqnda takeso zata aura! Musaddiq yace" bangane ba kamar ya akwai Wanda Xeey takeso, to inma akwai ni bansaniba gaskiya! Isma'il ya nunawa musaddiq text din da Xeey tai ma, zare ido shima yayi yace what Wlhi bansaniba!
Chapter 25 · 0% Book details