Sashe 12
Uwar Agola Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yana fara buga ƙofar da ƙarfi Kuluwa ta shiga zabga ihu tana neman ɗauki. Haule tana fita ta ga mutane a tsaitsaye da yara a can ma ta ga yaran ta su Alawiyya suna tsaye suna kallon kiɗa. Kalle-kalle ta fara Hudu da ya hango fitowar ta ya taho da sassarfa ganin babu alamar nutsuwa a tare da shi, cike da damuwa da tashin hankali ta ce
"Hudu akwai matsala fa a gidan" Ta faÉ—a tana nuna gidan da hannu. Hudu hankali tashe ya ce
"Mene ne?"
Haule ta ce
"Kuluwa"
Cike da fargaba ya ce
"Allah sa ba wankan manja ta masa ba, hana shi fitowa ta yi?"
Haule cike da ƙosawa da maganganub nashi duk da ya matso kusa da ita kuma ba kowa ne ya lura ba don kowa sabgar gabansa yake. Tana kallonsa ta ce
"Idan manja ne ra watsa masa da sauƙi, wallahi wandon ɗaurin auren ta ƙone" Idanu ya zaro tamkar za su faɗo ya dafe ƙirji ya ce
"Amma wannan mata an yi masifaffiya, ta san shaddar nawa ce wannan...Haule ta katse masa magana da faÉ—in
"Wallahi yana can ya ɗakko adda zai sare mata ƙafafu" Da sauri Hudu ya shige gaba ta mara masa baua, don ya san a yadda abokib nasa yake da son samu son kuɗi kamar tsohon da ya shekara casa,in, ga uban buri da ya ɗora a kan shaddar har cigiyar dillalai ya bashi bayan auren ya samo masa masu saye amma ta aikata wannan ƙanƙancin.
Da gudu gudu suka nufo cikin gidan gudun kar a yi aika-aika.
A can cikin gidan kuwa Malam Nura ganin aikain ɓalle ƙofar babba ne sai ya cire rigar ya rataye, kasancewar lokacin da ya saka rigar yana sauri daman ko singlet bai saka ba, don kiran da Hadiza ta masa ta ce za a ɗaura auren da wani in bai zo a kan lokaci ba shi ya dagula masa gabaɗaya lissafin da bai shirya a tsanake ba, ko mai bai shafa ba haka ya fito jiki fari tas, taimakon da Allah ya masa guda ɗaya wannan man da ya lakuta a saman hanci ba tare da sanin ya lakuta ba, shi ne Haule da ta saka ya murje fuskar ta yi dama dama duk da man ya yi yawan da ban da sheƙi da gumi babu abin da yake kamar ba sabon ango mai shirin angwancewa ba.
Ko da ya cire rigar ya rataye a kan igiya, ya ɗauki taɓarya ya shiga bugawa a jikin ƙofar tana ƙara duk ya loɓa ta, kasancewar akwai langa-langa a jikin ƙofar daga waje..
Hudu yana shigowa da ɗan gudu a kan hular Malam ta ɗaurin auren ya yi wa ƙafarsa masauƙi ba tare da ya sani ba, hular ta lotse, bai ƙaramin kai zuciya nesa ya yi ba da ya hangi Malam Nura ba sanye da wando gajere na shadda iya cinya duk ƙafar a ƙone baƙiƙƙirin tamkar wanda aka fito da wandon daga gidan da gobara ta kama. Ya daddage sai bugun ƙofar yake.
Yana zuwa ya kama shi yana riƙe shi yana bashi baki, Malam Nura rai a ɓace ya ce
"Hudu, Hudu, Hudu, sau nawa na kira ka?" Ya faɗa yana fisge riƙon da ya masa, Hudu ya ce
"Sau uku"
Malam Nura ya ce
"To babu ruwanka a cikin wannan magana, abu ɗaya za ka mini shi ne, ka tafi wajen Hadiza kake ta bata haƙuri ta yi wa iyayenta ta jira in zo a ɗaura auren nan da ni, wallahi aka ɗaura da wani na shiga uku na kaɗe har ganyena" Dariyarsa ya danne ganin duk abokin nasa ya susuce a kan mace, duk ya karaya ya rasa wane irin tafiya da zuciyarsa Hadiza ta yi.
Hudu ya ce
"Ka kwantar da hankalin ka abokina, ai Hadiza bata da wani miji sai kai"
Malam yana riƙe da taɓarya ya ce
"Kai dai ka je ka yi abin da na ce maka Hudu, baka san wace ce Hadiza ba, ita ta kirani a waya ta ce in zo kafin wasu daƙiƙu duk da bata faɗi daƙiƙa nawa ba ne, amma ta ce idan na haura daƙiƙu ban je ba da wani za a ɗaura mata aure" Kuluwa wacce take cikin ɗaki kunnuwanta a buɗe tamkar kunnuwan maciji jin wannan batu ranta fari ƙal, tana fatan Allah kai damo ga harawa, don za ta fi kowa farinciki wataƙila har ruwa sai ta zuba a ƙasa ta sha idan aka fasa ɗaura auren nan da Malam Nura ta ga ƙarshen tsiya da kuma tijara.
Hudu bai amsa masa waccan maganar ba ya ce
"Yanzu dai garin neman gira za ka rasa idanu gabaɗaya, domin kana nan kana ɓata lokacin ka za ta samu wani bazawarin a yi wufff da lokacin ɗaurin auren ka a ɗaura, yanzu abu ɗaya ya dace ka yi mu tafi a ɗaura auren idan ya so muna dawowa ka yi wa Kuluwa huluncin ƙona wandon nan" Kamar zai yi kuka ya ɗaga ido ya sake kallon windon ɗakin inda yake iya hango Kuluwa tare sa tsantsar ƙarfin hali a tare da ita domin babu da na sani a fuskarta, don ta ji an zo ceton ta gabaɗaya sai ma ya ga rawar kanta ya dawo.
Baki ya damƙe ya ce
"Ka san dai babu wanda zai ɗauki maƙudan kuɗi ya sayi rigar shadda kaɗai ko? Ta cuceni ta taƙaitani ai dai ba zan je wajen ɗaurin aure da gajeran wandon ba, wallahi babu mai cewa ma gajeran wando ne tun da ba a iya hango wandon sai zallar ƙwanrin ƙafata, kalli yadda ta mayar da wandon nan iya cinyata dab da tsantsa ta fa yake, banbancinsa da ɗan kamfai(Pant) Kaɗan ne"Ya faɗa yana saka hannu ya kama wandon yana nunawa Hudu. Hudu ya danne dariyarsa saboda arziƙin da Malam Nuran yake da shi ya wuce ya yi wannan abun a kan shaddar da bata kai dubu talatin ba har kuɗin ɗinkin, amma duk ya saka damuwa a ransa.
Hudu ya ce
"Ka bar batun wanna shaddar tata ta ƙare, don ko a Kano shagon da na siyo ita kaɗai ta rage a bandir ɗin ni na saye gabaɗaya, ka ga kuwa ko da an sake kawowa ba lallai a samu mai zanenta sak ba da sai a yanko a yi wandon ka siyar da ita tun da asarar kake hangowa" Kasa magana ya yi harara kawai yake aikawa Kuluwa ji yake tamkar ya zama ƙuda ya shiga ɗakin ta windown ya aiwatar da nufinsa ko ya samu sauƙi.
Maimakon ya yi wa Hudu magana sai ya juya wajen Kuluwa ya ce
"Kuluwa baki da zanen shadda kalar wannan?" ,Da mamaki take kallonsa har dariya ta so kuɓuce mata amma gudun masifarsa ta danne, saboda ta san tana darawa zai ce bata damu da halin da yake ciki ba, muryarta da alamar dariya domin sai da ta danne, yau ne ta tabbatar da cewar idan mutum yana neman mafita komai ma gani yake zai dace tana karkata kai cike da nuna damuwar da yake ciki ta ce
"Haba Malam ina ni ina shadda irin wannan mai tsada, kai ma ina jin a kaf rayuwarka wannan ne karon farko da ka É—inka kuma kananganin siyar da ita za ka yi ba za ka ci gaba da sakawa ba bare ni... Kamar zai kai mata duka ya ce
"To na ji abun da na tambaye ki da ban amsar da kike bani da ban... Hudu ya ce
"Ba fa ita ta kai zomon ba rataya aka bata, ga wacce ta yi abun can tana É—aki baka da damar hukuntata kawai don ita ce kuka mai daÉ—in hawa... Malam yana masifa ya ce
"Ya isheka matarka ce ko tawa?" ,Hudu ya ce
"Allah ya baka haƙuri, wai kana nufin zanin shaddar za ka ɗaura idan tana da akwai?" Ya faɗa yana haɗiye dariyarsa don har ya hango gogan nasa ɗauri da zani.
Malam Nura ya yi shiru yana tuno da yanzu fa yana can a cikin jama,a ana masa Allah sanya alkairi, ana ta musu hoto shi da Hadiza wataƙila ma har hannunsa dai ta kama, tana masa murmushi, da yanzu ta zama mallakinsa amma Kuluwar nan ta kawo masa tsaiko a lamarin auren nan.
Kamar ya kai wa Hudu duka ya ce
",Kamar wani bayerabe zan ɗaura zani, ka san dai na ɗaura zani na je wajen nan wallahi kwanan ɗaurin aurena da Hadiza ya ƙarw don ba za ta aureni ba, daman nufina a je a samu wani tela mai saurin ɗinki ya ɗinka mini wandon, ko zanin ba zai isa ba sai ya mini ƙafafun in ya so daga saman ko atamfa ce ya saka a mini kwanbileshin (Combination) ka ga idan na saka babu mai cewa zanin atamfa ne daga sama tun da rigar shaddar za ta rufe wajen.
Idanun Hudu gabaɗaya sun kawo kwalla, amma ba ta kuka ba sai ta tsabar dariyar da take cinsa yake dannewa, ba komai yake bashi dariya ba illa idan ya kalli Malam Nura da wannan ƙonannan wandon, abu na biyu idan ya tuna yadda ido ya juye da mujiya, wato Malam Nura ya je wajen Hadiza ne da soyayyar ƙarya saboda an ce mijin ta da suka rabu mai kuɗi ne, kuma ita ma tana da kuɗi shi ne ya je da nufin ya aure ta ya wanki banza, ya tatiƙe kuɗaɗen ya sake ta, ya tsakuri wani abu daga abin da ya mora daga gare ta ya auro wata, amma da yake Allah ya ga mugun ƙudirinsa aai ya jarabce shi da son ta na gaskiya, sannan sai gashi shi take wanka a maimakon ya wanke ta, ita take cin kuɗinsa har yanzu yana ganin idan ya aure ta, zai ci kuɗin ta ne. Abu na uku yana mamakin yadda Kuluwa ta shammace shi ta ƙona wandon shaddar, ya san ba komai ba ne yake faruwa da abokinsa sai irin tijarar da yake yi wa mata, da ɗaukan haƙƙinsu ya aure ki ya wulakanta ki ya sake ki, shi a lamarinsa ma bai san mene ne so ba, don kowacce ba yana auren ta don so ba ne, kawai son zuciya ne.
Hudu ya ce
"Hudu akwai matsala fa a gidan" Ta faÉ—a tana nuna gidan da hannu. Hudu hankali tashe ya ce
"Mene ne?"
Haule ta ce
"Kuluwa"
Cike da fargaba ya ce
"Allah sa ba wankan manja ta masa ba, hana shi fitowa ta yi?"
Haule cike da ƙosawa da maganganub nashi duk da ya matso kusa da ita kuma ba kowa ne ya lura ba don kowa sabgar gabansa yake. Tana kallonsa ta ce
"Idan manja ne ra watsa masa da sauƙi, wallahi wandon ɗaurin auren ta ƙone" Idanu ya zaro tamkar za su faɗo ya dafe ƙirji ya ce
"Amma wannan mata an yi masifaffiya, ta san shaddar nawa ce wannan...Haule ta katse masa magana da faÉ—in
"Wallahi yana can ya ɗakko adda zai sare mata ƙafafu" Da sauri Hudu ya shige gaba ta mara masa baua, don ya san a yadda abokib nasa yake da son samu son kuɗi kamar tsohon da ya shekara casa,in, ga uban buri da ya ɗora a kan shaddar har cigiyar dillalai ya bashi bayan auren ya samo masa masu saye amma ta aikata wannan ƙanƙancin.
Da gudu gudu suka nufo cikin gidan gudun kar a yi aika-aika.
A can cikin gidan kuwa Malam Nura ganin aikain ɓalle ƙofar babba ne sai ya cire rigar ya rataye, kasancewar lokacin da ya saka rigar yana sauri daman ko singlet bai saka ba, don kiran da Hadiza ta masa ta ce za a ɗaura auren da wani in bai zo a kan lokaci ba shi ya dagula masa gabaɗaya lissafin da bai shirya a tsanake ba, ko mai bai shafa ba haka ya fito jiki fari tas, taimakon da Allah ya masa guda ɗaya wannan man da ya lakuta a saman hanci ba tare da sanin ya lakuta ba, shi ne Haule da ta saka ya murje fuskar ta yi dama dama duk da man ya yi yawan da ban da sheƙi da gumi babu abin da yake kamar ba sabon ango mai shirin angwancewa ba.
Ko da ya cire rigar ya rataye a kan igiya, ya ɗauki taɓarya ya shiga bugawa a jikin ƙofar tana ƙara duk ya loɓa ta, kasancewar akwai langa-langa a jikin ƙofar daga waje..
Hudu yana shigowa da ɗan gudu a kan hular Malam ta ɗaurin auren ya yi wa ƙafarsa masauƙi ba tare da ya sani ba, hular ta lotse, bai ƙaramin kai zuciya nesa ya yi ba da ya hangi Malam Nura ba sanye da wando gajere na shadda iya cinya duk ƙafar a ƙone baƙiƙƙirin tamkar wanda aka fito da wandon daga gidan da gobara ta kama. Ya daddage sai bugun ƙofar yake.
Yana zuwa ya kama shi yana riƙe shi yana bashi baki, Malam Nura rai a ɓace ya ce
"Hudu, Hudu, Hudu, sau nawa na kira ka?" Ya faɗa yana fisge riƙon da ya masa, Hudu ya ce
"Sau uku"
Malam Nura ya ce
"To babu ruwanka a cikin wannan magana, abu ɗaya za ka mini shi ne, ka tafi wajen Hadiza kake ta bata haƙuri ta yi wa iyayenta ta jira in zo a ɗaura auren nan da ni, wallahi aka ɗaura da wani na shiga uku na kaɗe har ganyena" Dariyarsa ya danne ganin duk abokin nasa ya susuce a kan mace, duk ya karaya ya rasa wane irin tafiya da zuciyarsa Hadiza ta yi.
Hudu ya ce
"Ka kwantar da hankalin ka abokina, ai Hadiza bata da wani miji sai kai"
Malam yana riƙe da taɓarya ya ce
"Kai dai ka je ka yi abin da na ce maka Hudu, baka san wace ce Hadiza ba, ita ta kirani a waya ta ce in zo kafin wasu daƙiƙu duk da bata faɗi daƙiƙa nawa ba ne, amma ta ce idan na haura daƙiƙu ban je ba da wani za a ɗaura mata aure" Kuluwa wacce take cikin ɗaki kunnuwanta a buɗe tamkar kunnuwan maciji jin wannan batu ranta fari ƙal, tana fatan Allah kai damo ga harawa, don za ta fi kowa farinciki wataƙila har ruwa sai ta zuba a ƙasa ta sha idan aka fasa ɗaura auren nan da Malam Nura ta ga ƙarshen tsiya da kuma tijara.
Hudu bai amsa masa waccan maganar ba ya ce
"Yanzu dai garin neman gira za ka rasa idanu gabaɗaya, domin kana nan kana ɓata lokacin ka za ta samu wani bazawarin a yi wufff da lokacin ɗaurin auren ka a ɗaura, yanzu abu ɗaya ya dace ka yi mu tafi a ɗaura auren idan ya so muna dawowa ka yi wa Kuluwa huluncin ƙona wandon nan" Kamar zai yi kuka ya ɗaga ido ya sake kallon windon ɗakin inda yake iya hango Kuluwa tare sa tsantsar ƙarfin hali a tare da ita domin babu da na sani a fuskarta, don ta ji an zo ceton ta gabaɗaya sai ma ya ga rawar kanta ya dawo.
Baki ya damƙe ya ce
"Ka san dai babu wanda zai ɗauki maƙudan kuɗi ya sayi rigar shadda kaɗai ko? Ta cuceni ta taƙaitani ai dai ba zan je wajen ɗaurin aure da gajeran wandon ba, wallahi babu mai cewa ma gajeran wando ne tun da ba a iya hango wandon sai zallar ƙwanrin ƙafata, kalli yadda ta mayar da wandon nan iya cinyata dab da tsantsa ta fa yake, banbancinsa da ɗan kamfai(Pant) Kaɗan ne"Ya faɗa yana saka hannu ya kama wandon yana nunawa Hudu. Hudu ya danne dariyarsa saboda arziƙin da Malam Nuran yake da shi ya wuce ya yi wannan abun a kan shaddar da bata kai dubu talatin ba har kuɗin ɗinkin, amma duk ya saka damuwa a ransa.
Hudu ya ce
"Ka bar batun wanna shaddar tata ta ƙare, don ko a Kano shagon da na siyo ita kaɗai ta rage a bandir ɗin ni na saye gabaɗaya, ka ga kuwa ko da an sake kawowa ba lallai a samu mai zanenta sak ba da sai a yanko a yi wandon ka siyar da ita tun da asarar kake hangowa" Kasa magana ya yi harara kawai yake aikawa Kuluwa ji yake tamkar ya zama ƙuda ya shiga ɗakin ta windown ya aiwatar da nufinsa ko ya samu sauƙi.
Maimakon ya yi wa Hudu magana sai ya juya wajen Kuluwa ya ce
"Kuluwa baki da zanen shadda kalar wannan?" ,Da mamaki take kallonsa har dariya ta so kuɓuce mata amma gudun masifarsa ta danne, saboda ta san tana darawa zai ce bata damu da halin da yake ciki ba, muryarta da alamar dariya domin sai da ta danne, yau ne ta tabbatar da cewar idan mutum yana neman mafita komai ma gani yake zai dace tana karkata kai cike da nuna damuwar da yake ciki ta ce
"Haba Malam ina ni ina shadda irin wannan mai tsada, kai ma ina jin a kaf rayuwarka wannan ne karon farko da ka É—inka kuma kananganin siyar da ita za ka yi ba za ka ci gaba da sakawa ba bare ni... Kamar zai kai mata duka ya ce
"To na ji abun da na tambaye ki da ban amsar da kike bani da ban... Hudu ya ce
"Ba fa ita ta kai zomon ba rataya aka bata, ga wacce ta yi abun can tana É—aki baka da damar hukuntata kawai don ita ce kuka mai daÉ—in hawa... Malam yana masifa ya ce
"Ya isheka matarka ce ko tawa?" ,Hudu ya ce
"Allah ya baka haƙuri, wai kana nufin zanin shaddar za ka ɗaura idan tana da akwai?" Ya faɗa yana haɗiye dariyarsa don har ya hango gogan nasa ɗauri da zani.
Malam Nura ya yi shiru yana tuno da yanzu fa yana can a cikin jama,a ana masa Allah sanya alkairi, ana ta musu hoto shi da Hadiza wataƙila ma har hannunsa dai ta kama, tana masa murmushi, da yanzu ta zama mallakinsa amma Kuluwar nan ta kawo masa tsaiko a lamarin auren nan.
Kamar ya kai wa Hudu duka ya ce
",Kamar wani bayerabe zan ɗaura zani, ka san dai na ɗaura zani na je wajen nan wallahi kwanan ɗaurin aurena da Hadiza ya ƙarw don ba za ta aureni ba, daman nufina a je a samu wani tela mai saurin ɗinki ya ɗinka mini wandon, ko zanin ba zai isa ba sai ya mini ƙafafun in ya so daga saman ko atamfa ce ya saka a mini kwanbileshin (Combination) ka ga idan na saka babu mai cewa zanin atamfa ne daga sama tun da rigar shaddar za ta rufe wajen.
Idanun Hudu gabaɗaya sun kawo kwalla, amma ba ta kuka ba sai ta tsabar dariyar da take cinsa yake dannewa, ba komai yake bashi dariya ba illa idan ya kalli Malam Nura da wannan ƙonannan wandon, abu na biyu idan ya tuna yadda ido ya juye da mujiya, wato Malam Nura ya je wajen Hadiza ne da soyayyar ƙarya saboda an ce mijin ta da suka rabu mai kuɗi ne, kuma ita ma tana da kuɗi shi ne ya je da nufin ya aure ta ya wanki banza, ya tatiƙe kuɗaɗen ya sake ta, ya tsakuri wani abu daga abin da ya mora daga gare ta ya auro wata, amma da yake Allah ya ga mugun ƙudirinsa aai ya jarabce shi da son ta na gaskiya, sannan sai gashi shi take wanka a maimakon ya wanke ta, ita take cin kuɗinsa har yanzu yana ganin idan ya aure ta, zai ci kuɗin ta ne. Abu na uku yana mamakin yadda Kuluwa ta shammace shi ta ƙona wandon shaddar, ya san ba komai ba ne yake faruwa da abokinsa sai irin tijarar da yake yi wa mata, da ɗaukan haƙƙinsu ya aure ki ya wulakanta ki ya sake ki, shi a lamarinsa ma bai san mene ne so ba, don kowacce ba yana auren ta don so ba ne, kawai son zuciya ne.
Hudu ya ce