Sashe 70
Tafita Zakka Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Ana saura Kwana goma Bikin su Hanne Oder din kayan Dakin su ya iso har da Na Amina,Kowacee kuma Dakinta inda zata zauna aka wuce mata dashi Hamida dai yayarta Zulfa taje ta taimakama ma"aikatan aka Gyaran kayan aka saka komai a muhallimsa anan zaria zata zauna Gaskiya Layout.
Ita kuma Sa"adatu Gombe Kanwar Anty Amarya A"i sai Haj Nasara da Hajiya Babba suka je aka gyara Inda Sa"adatun zata zauna Sai washegari suka Dawo na Hannatu kuwa Haj.Uwani ce taje da Anty Amarya har Yola suka yi Jerin su,Tunda sun tafi da Kayan Kitchen din da Hajiya ta siyama Hanne da Hamida duka da Sauran na Hamidan da Mamanmu ta siya a mota ta saka ta aika ma Zulfa bata bari ko su Hajiya sun sani ba kada ta bar wata kafar da Za"a Zargeta.
Har Zulfa sai da tayi mata mganan ina ta samu kudin siyan wannan kayan saj tace ai kiwo tayi a gusai da Bikin Hamidan yazo sai ta saida tayi wannan Hidimar da ita Zulfa sai ta yarda bata kawo Tunanin komai ba na wajen Hajiyan wajen mamanmu aka barsu da niyar sai ranar Daurin airan in za"a wuce da Amarya sai a wuce dasu.
Bangaran gidan Amina kuwa batare da kowa ya sani ba Daga Hajiya sai Aliyu sai Mallam suka san an kawo kayan Dakin,Hajiya da bata samu kiran yar"uwanta yagana ba saboda Nisa Mallam ma yace ta kyalesu Fadila matar Nasir ta nema tare suka gyara gidan Amina ya fito Tsab komai an saka mata Labule ne kadai ba"a saka ba Aisha zata zo dasu Tunda tace ta siya ma Amima masu kyau oder dinsu tayi daga Dubai.
Har kuma aka gama gyaran gidan Fadila bata san ko gidan waye ba,Tunda dai Hajiyan ta nemeta da Nasir bai sani ba,sai bata ma Fadamai ba Tunda bata da Hayaniya,ta kama Bakinta tayi shuru ammh bata taba kawo Tunanin gidan nan da komai na Cikinsa na Amina bane Aliyum ma Data gani Tafi Tunanin ko nashi ne ko na wani nashi kila.
Shirye shirye ta ko"ina ya kamkama ana cikin kwanakin Bikin ne Sakina achan Madina tayi Zazzabi har da su Amaye amaye ana zuwa asibiti aka gwadata sai Ciki dan kimanin wata Biyu da kwanaki Labarin da ya yadu a Nageria abun mamaki shi Danmallan Da mallam kadai sukayi mgana ya fadamai hajiya ma mallam ya manta bai Fadamata a bakin Haj.Nasara take ji.
Anty Amarya haka take yada mganar Cikin tana Hura Hanci Hangowa kawai take komai ya kare ana gama auran Sa"adatu zata fara kokarin ganin bayan Haj.Uwa Ita kuwa daman Dariya take mata domin ta tabbatar da cewa kamar sauran shima haka zai bi Rariya Hajiya dataji labari Fatan Allah ya Tsayar tayi mata har aranta bata Fatan wannan karon Sakina ta rasa Cikinta ai mugunta Fitsarin Fako ne mai shi yake ci.
Amina ma taji labari abakin ya Aisha itama tace Sadiya ta kirata ta fadamata Amina sai taji Abu acikin Ranta ammh bata yarda ta Furtamai abunda taji ba shima kuma bai taba mata mganar ba sai mganar tafiyarsu Dayace Ranar Litini Jirginsu zai taso Daga jidda da Daddare zuwa Nageria shi da Sakina da Sarood.
Da farko yaso Sarood ta zauna Hajiya Dataji mganar tace bai yi adalci ba Sai dai Sakina ta Zauna shi kuma baya son Rigima yadda Sakina ta ke Hura Hanci da Cikin jikinta da kuma wannan sha"anin in yace ta zauna ai sai ta nemi mai hayaniya sannan yana da kudi a Hannunsa yasa kawai yaga gwara su taho gabadaya sannan yana su dan jima tunda hutun karshen shekara ne.
Su kuma su Amina suna ta shiri Ya Aisha bata siya ma Amina komai da kudin da Usman ya bata ba Daman kuma ta Bude Banki zuwanta Abuja sai da sukayi mgana da Hajiya tace ta barmata kudinta tunda kusan komai ta siya ma Aminar itama Aishan ta siya mata Zannuwan gado da sauran kayan Kitchen su blander Toster da Sauran su sai kayan Kamshin girki su kayan gyara kuma sai dai inda ta Haihu sannan har da Yakaka zata tafi gumel Usman baya nan yana Lagos za"a Yi Bikin Direba ne zai kawo su da kayan su.
Amina ta rasa Bakin godiya Data ga Uban kayan lefenta da kayan da ya Aisha ta siya mata sai da tayi kwallah Tace Gudummuwar malam da Hajiya ne suka Dauke ma Danmallam lefe tasani ba"a taba kawo lefen kowa ba sai dai in kaje gidanka ka gani ammh Sai gashi ita da nata Lefen zata koma Allah Sarki Rayuwa daman ai abunda ya baka Tsoro watarana shi zai sakaka kuka.
Ranar Talata da yammah Jirgin su Damallam ya sauka Filin saukan Jirage na kano Aliyu yazo ya Dauke su shi da Jafar suka kawo su Gumel gidansu suka sauka.
*Janafty*
[10/31, 8:12 PM] +234 814 039 1977: *TFZB2024*
*Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yada'ashi..Pay N500 via Jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan lambar 09069067488*
Saboda Gajiyan tafiya yasa ko washegari basu fita ko"ina ba Har shi Dannallam din bai iya fita ba sai Ranar Laraba suka zo gidan mallam Lokacin baki daga nesa duk sun fara Hallata irin su ya Fatima da su ya Nazifa,Mutanen Jordan kuma Suma Jiya suka iso Goggo Husai da Jadwa Sannan aranar Hidaya matar Nazir da Jaleela suka sauka suma da yammah kuma sai ga Mutanen Parthercourt su yaya zahra,Gida fa masha Allah ya fara shiga da Dangi na nesa dana kusa Sakina saiwani Hura hanci take yi tana iyayi ita a dole mai ciki sai Tsirfa take yi kala kala Saboda Sarood wanda ita batama nuna ta damu ba,Bangaran Anty Amarya kuwa itama Sai harkokinta take yi Cikin jin Dadi Saboda ai tana ganin ita yanzu bata da wata matsala ga Sakina na da Ciki gashi Zata aurar da Sa"adatu duk da abaya bata so hakan ba ammh zuwa yanzu ta hango hakan a matakin Nasararta.
Aranar bata koma gidan Danmallam ba nan ta kwana wai bata son kamshin Gidansu Danmallam ko ta kanta bai bi ba ya Dauki Sarood suka koma sai da Safe bayan sun Karya sun yi wanka ya Dawo da ita.
Aranar da Safe yan gusai suka iso da su ya Abida,ya zulaihat su ya Zeenatu da ya zulfa da su ya Ikram dukkansu duk sun iso domin in ba irin wannan Sha"anin ba baka samun damar zuwa gida har ka dan yi kwanaki mallam baya barin su suzo sai da wani Dalili mai karfi.
Hidaya wannan karon data zo Shashen Hajiya uwa ta sake sauka kamar yadda ta saba Hajiya bata nuna komai ba ko a Fuskarta,Shiyasa Hajiya uwa ta saki jiki anata kai da kawo da ita sai dai ta ciki na ciki in sun Hadu da Anty Amarya su rika ma juna kallon baki isa ba ita Hajiya Uwa Dariya Anty Amarya ke bata in taga tana wani iyayi saboda dai tasan Cikin Sakina ma wannan karon sai yabi Rariya kamar sauran ita kuma Anty Amarya tana takama da mallam yace Wannan matsalan ta kau har Abada.
Hajiya babba kuwa bata bi ta kansu ba harkan gabanta kawai take yi,Shashenta itama ba Matsaka tsinke Danginta yan maiduguri sun iso suma kwansu da kwarkwatansu Tunda ai Auta Hajiya zata aurar wannan karon Ita in kaga tana mgana ko Shawara da mallam ne ban dashi ta daina yarda da kowa Tunda ta lura yanzu Rayuwar ga yadda ta zama sai addu"a kawai wanda bakayi Tsammani ba sai ya Cutar dakai ko Hajiya Nasara da bata taba kamata da wani abu bata Saki Jiki da ita ba an ce Sau Daya ruwa yake dukam mutum yayi hankali ita kanta ya Daketa kuma tayi Hankalin Sosai.
Achan gidan Aba kuwa shima yana cike da Baki na nesa dana kusa yan Gusai Dangin Aba da Dangin mamanmilu Wannan karon yadda taci Burin Bikin nan yasa gayyata ba kama hannun yaro har da wadanda basu zo nasu Zeenatu ba sun zo wannan karon Mamanmu sai shiga take tana Fita Domin tun jiya ta fara sawa tana Cirewa Da Sabbin kaya Bakinta kamar zai Tsage saboda Fara"a kanta na Fashewa duk inda ta shiga ana Balaraba sannu da kokari Allah ya Biyaki da Aljannah.
Tana amsawa da Ameen tana kara jin Dadi ita ta samu Duniya,Domin yadda ta amshi kudade hannun Aba Allah kadai yasan yawansu data Mika hannu bai gaddama yake bata sannan Duk abunda tace ko bai kwantamai ba ta ZAuna Hajiyar banza ai yanzu ta sha gabanta ballatana wani chan Tsoho mallam da kansa A tunanin ta ayadda ta ci wannan Burin bata taba Hasaahen ko kawo kanta da wani abu zai iya faruwa da ita da zai Tsawarwata wannan Burin nata ba ita kawai har kan gabanta take yi Ranta Fes da Tunanin Burinta ya Cika sannan tana kan cin Duniyarta ne kamar yadda ta Tsara.
Abunda bata sani ba suna nasu ne Allah ya riga ya gama nasu..Basu sani ba Ranar tonon asirinsu ya kusa zuwa..Dama dama ace suna da sani da Allah wlh kafin Ranar hakan duk zasu gudu kafin bayyanan boyayyun Fuskokinsu.
Ita kuma Sa"adatu Gombe Kanwar Anty Amarya A"i sai Haj Nasara da Hajiya Babba suka je aka gyara Inda Sa"adatun zata zauna Sai washegari suka Dawo na Hannatu kuwa Haj.Uwani ce taje da Anty Amarya har Yola suka yi Jerin su,Tunda sun tafi da Kayan Kitchen din da Hajiya ta siyama Hanne da Hamida duka da Sauran na Hamidan da Mamanmu ta siya a mota ta saka ta aika ma Zulfa bata bari ko su Hajiya sun sani ba kada ta bar wata kafar da Za"a Zargeta.
Har Zulfa sai da tayi mata mganan ina ta samu kudin siyan wannan kayan saj tace ai kiwo tayi a gusai da Bikin Hamidan yazo sai ta saida tayi wannan Hidimar da ita Zulfa sai ta yarda bata kawo Tunanin komai ba na wajen Hajiyan wajen mamanmu aka barsu da niyar sai ranar Daurin airan in za"a wuce da Amarya sai a wuce dasu.
Bangaran gidan Amina kuwa batare da kowa ya sani ba Daga Hajiya sai Aliyu sai Mallam suka san an kawo kayan Dakin,Hajiya da bata samu kiran yar"uwanta yagana ba saboda Nisa Mallam ma yace ta kyalesu Fadila matar Nasir ta nema tare suka gyara gidan Amina ya fito Tsab komai an saka mata Labule ne kadai ba"a saka ba Aisha zata zo dasu Tunda tace ta siya ma Amima masu kyau oder dinsu tayi daga Dubai.
Har kuma aka gama gyaran gidan Fadila bata san ko gidan waye ba,Tunda dai Hajiyan ta nemeta da Nasir bai sani ba,sai bata ma Fadamai ba Tunda bata da Hayaniya,ta kama Bakinta tayi shuru ammh bata taba kawo Tunanin gidan nan da komai na Cikinsa na Amina bane Aliyum ma Data gani Tafi Tunanin ko nashi ne ko na wani nashi kila.
Shirye shirye ta ko"ina ya kamkama ana cikin kwanakin Bikin ne Sakina achan Madina tayi Zazzabi har da su Amaye amaye ana zuwa asibiti aka gwadata sai Ciki dan kimanin wata Biyu da kwanaki Labarin da ya yadu a Nageria abun mamaki shi Danmallan Da mallam kadai sukayi mgana ya fadamai hajiya ma mallam ya manta bai Fadamata a bakin Haj.Nasara take ji.
Anty Amarya haka take yada mganar Cikin tana Hura Hanci Hangowa kawai take komai ya kare ana gama auran Sa"adatu zata fara kokarin ganin bayan Haj.Uwa Ita kuwa daman Dariya take mata domin ta tabbatar da cewa kamar sauran shima haka zai bi Rariya Hajiya dataji labari Fatan Allah ya Tsayar tayi mata har aranta bata Fatan wannan karon Sakina ta rasa Cikinta ai mugunta Fitsarin Fako ne mai shi yake ci.
Amina ma taji labari abakin ya Aisha itama tace Sadiya ta kirata ta fadamata Amina sai taji Abu acikin Ranta ammh bata yarda ta Furtamai abunda taji ba shima kuma bai taba mata mganar ba sai mganar tafiyarsu Dayace Ranar Litini Jirginsu zai taso Daga jidda da Daddare zuwa Nageria shi da Sakina da Sarood.
Da farko yaso Sarood ta zauna Hajiya Dataji mganar tace bai yi adalci ba Sai dai Sakina ta Zauna shi kuma baya son Rigima yadda Sakina ta ke Hura Hanci da Cikin jikinta da kuma wannan sha"anin in yace ta zauna ai sai ta nemi mai hayaniya sannan yana da kudi a Hannunsa yasa kawai yaga gwara su taho gabadaya sannan yana su dan jima tunda hutun karshen shekara ne.
Su kuma su Amina suna ta shiri Ya Aisha bata siya ma Amina komai da kudin da Usman ya bata ba Daman kuma ta Bude Banki zuwanta Abuja sai da sukayi mgana da Hajiya tace ta barmata kudinta tunda kusan komai ta siya ma Aminar itama Aishan ta siya mata Zannuwan gado da sauran kayan Kitchen su blander Toster da Sauran su sai kayan Kamshin girki su kayan gyara kuma sai dai inda ta Haihu sannan har da Yakaka zata tafi gumel Usman baya nan yana Lagos za"a Yi Bikin Direba ne zai kawo su da kayan su.
Amina ta rasa Bakin godiya Data ga Uban kayan lefenta da kayan da ya Aisha ta siya mata sai da tayi kwallah Tace Gudummuwar malam da Hajiya ne suka Dauke ma Danmallam lefe tasani ba"a taba kawo lefen kowa ba sai dai in kaje gidanka ka gani ammh Sai gashi ita da nata Lefen zata koma Allah Sarki Rayuwa daman ai abunda ya baka Tsoro watarana shi zai sakaka kuka.
Ranar Talata da yammah Jirgin su Damallam ya sauka Filin saukan Jirage na kano Aliyu yazo ya Dauke su shi da Jafar suka kawo su Gumel gidansu suka sauka.
*Janafty*
[10/31, 8:12 PM] +234 814 039 1977: *TFZB2024*
*Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yada'ashi..Pay N500 via Jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan lambar 09069067488*
Saboda Gajiyan tafiya yasa ko washegari basu fita ko"ina ba Har shi Dannallam din bai iya fita ba sai Ranar Laraba suka zo gidan mallam Lokacin baki daga nesa duk sun fara Hallata irin su ya Fatima da su ya Nazifa,Mutanen Jordan kuma Suma Jiya suka iso Goggo Husai da Jadwa Sannan aranar Hidaya matar Nazir da Jaleela suka sauka suma da yammah kuma sai ga Mutanen Parthercourt su yaya zahra,Gida fa masha Allah ya fara shiga da Dangi na nesa dana kusa Sakina saiwani Hura hanci take yi tana iyayi ita a dole mai ciki sai Tsirfa take yi kala kala Saboda Sarood wanda ita batama nuna ta damu ba,Bangaran Anty Amarya kuwa itama Sai harkokinta take yi Cikin jin Dadi Saboda ai tana ganin ita yanzu bata da wata matsala ga Sakina na da Ciki gashi Zata aurar da Sa"adatu duk da abaya bata so hakan ba ammh zuwa yanzu ta hango hakan a matakin Nasararta.
Aranar bata koma gidan Danmallam ba nan ta kwana wai bata son kamshin Gidansu Danmallam ko ta kanta bai bi ba ya Dauki Sarood suka koma sai da Safe bayan sun Karya sun yi wanka ya Dawo da ita.
Aranar da Safe yan gusai suka iso da su ya Abida,ya zulaihat su ya Zeenatu da ya zulfa da su ya Ikram dukkansu duk sun iso domin in ba irin wannan Sha"anin ba baka samun damar zuwa gida har ka dan yi kwanaki mallam baya barin su suzo sai da wani Dalili mai karfi.
Hidaya wannan karon data zo Shashen Hajiya uwa ta sake sauka kamar yadda ta saba Hajiya bata nuna komai ba ko a Fuskarta,Shiyasa Hajiya uwa ta saki jiki anata kai da kawo da ita sai dai ta ciki na ciki in sun Hadu da Anty Amarya su rika ma juna kallon baki isa ba ita Hajiya Uwa Dariya Anty Amarya ke bata in taga tana wani iyayi saboda dai tasan Cikin Sakina ma wannan karon sai yabi Rariya kamar sauran ita kuma Anty Amarya tana takama da mallam yace Wannan matsalan ta kau har Abada.
Hajiya babba kuwa bata bi ta kansu ba harkan gabanta kawai take yi,Shashenta itama ba Matsaka tsinke Danginta yan maiduguri sun iso suma kwansu da kwarkwatansu Tunda ai Auta Hajiya zata aurar wannan karon Ita in kaga tana mgana ko Shawara da mallam ne ban dashi ta daina yarda da kowa Tunda ta lura yanzu Rayuwar ga yadda ta zama sai addu"a kawai wanda bakayi Tsammani ba sai ya Cutar dakai ko Hajiya Nasara da bata taba kamata da wani abu bata Saki Jiki da ita ba an ce Sau Daya ruwa yake dukam mutum yayi hankali ita kanta ya Daketa kuma tayi Hankalin Sosai.
Achan gidan Aba kuwa shima yana cike da Baki na nesa dana kusa yan Gusai Dangin Aba da Dangin mamanmilu Wannan karon yadda taci Burin Bikin nan yasa gayyata ba kama hannun yaro har da wadanda basu zo nasu Zeenatu ba sun zo wannan karon Mamanmu sai shiga take tana Fita Domin tun jiya ta fara sawa tana Cirewa Da Sabbin kaya Bakinta kamar zai Tsage saboda Fara"a kanta na Fashewa duk inda ta shiga ana Balaraba sannu da kokari Allah ya Biyaki da Aljannah.
Tana amsawa da Ameen tana kara jin Dadi ita ta samu Duniya,Domin yadda ta amshi kudade hannun Aba Allah kadai yasan yawansu data Mika hannu bai gaddama yake bata sannan Duk abunda tace ko bai kwantamai ba ta ZAuna Hajiyar banza ai yanzu ta sha gabanta ballatana wani chan Tsoho mallam da kansa A tunanin ta ayadda ta ci wannan Burin bata taba Hasaahen ko kawo kanta da wani abu zai iya faruwa da ita da zai Tsawarwata wannan Burin nata ba ita kawai har kan gabanta take yi Ranta Fes da Tunanin Burinta ya Cika sannan tana kan cin Duniyarta ne kamar yadda ta Tsara.
Abunda bata sani ba suna nasu ne Allah ya riga ya gama nasu..Basu sani ba Ranar tonon asirinsu ya kusa zuwa..Dama dama ace suna da sani da Allah wlh kafin Ranar hakan duk zasu gudu kafin bayyanan boyayyun Fuskokinsu.