← Book details Tafita Zakka Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 58 OF 105

Sashe 58

Tafita Zakka Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Amina ko kanta bata Dago ba har ta kariso falon Aliyu Sai kallonta yake yi ya Bude baki yafi a kirga yana Rufewa saboda mamaki Danmallam kuma Hannayensa Sarke saman kirjinsa yana kare ma Amina kallon Tundaga sama har kasa yana mamakin girmanta yarinyar daya barta marabanta da kwaila kadan ne itace ta koma wata Big mama..? Ko"ina ya cika haka? Cikinta kawai yake kallo duk nacinsa taki yarda su hada ido shi ko Aliyu ba mamakin ganin Amina bane ya Razana shi ba illah Cikin Dake jikinta ne ya fi bashi mamaki ya kalli Umar yafi sau goma ya kasa mgana shi kuma sai ya basar dashi bai shirya mgana dashi ba yanzu. Amina kuwa kanta na kasa ta nemi kasan Cafet ta zauna Dakyar yakaka na fadin"kada ki takura kanki kowa yasan Lalurace hau kujera ki zauna mana..! Ko kallon yakaka batayi ba tayi zamanta Saman cafet kanta na kasa Ya Aisha sai kallon Amina take yi tana Hararanta ganin yadda ta hade rai Yakaka ta saki baki tana kallonta kafin tace"Yau naga Tsiya Indo..? Amina fa sai Addu"a jira take su gaisheta kenan..? Amina sai alokacin ta Dago kanta karaf suka Hada ido da ya Danmallam Daya gama kafeta da ido tun shigowarta ya kasa dauke ganinsa akanta yana ta mamakin girmanta sannan yana Tunanin yadda yaganta da Cikin nan bai taba Hasaso hakan nan kusa ba akanta ba sai gashi Allah ya nuna nashi Ikon. Saurin Dauke kanta tayi Saboda wani Dum dataji da yanayin kallon nasa sai da taji dan Cikinta ya koma gefe daya Ta Cikin Hijabin ta dora hannunta kan cikinta tana jin wani kaunar abunda ke Cikinta na kara shiganta Tun ranar da sukaje Scan aka hasko mata abunda ke Cikinta wani soyayyarsa ta ratsa kirjinta taji duk duniya bata da wanda take so kamarsa abun ya bata sha"awa dan mutum acikinta yana Rayuwa.. Bata kara kallonsu ba cikin shakewar murya tace"sannun ku da zuwa..! Aliyu ne ya amsa yana kallonta Cikin Shanye mamakin sa yace"Yauwa Amina ko..? Amina ta dago ta kallesa kafin ta maida kanta kasa ta gyada mai kai Cikin mirmishi yace"Allah Sarki ashe kina nan..? Ya nauyin jiki kuma..? Sai ta kasa mgana Yakakace ke fadin"Ai ta Dade anan watan ta biyu ko Aisha..? Ya Aisha tace"Eh ta dan jima..! Aliyu ya jinjina kai yana kallon Amina yace"Allah ya rabasu lafiya..! Yakaka da Aisha suka amsa mai da Ameen ya Danmallan dai bai ce komai ba,Sai kallon Amina yake yi kasa kasa. Aisha tana Lura dashi sai ta isa wajen Amina tana fadin"Amina taso na ganki mana..! Tafada tana taimaka mata ta mike Tsaye yakaka ta kalleta tana Fadin"Ahto gwara ki jata ki Fadamata gaskiya ko zataji..Koda yake ta makara na riga na kwace mijin Dani zai koma garin Manzo..! Aliyu na Dariya yace"Kwarai baba. ! Hararanta Amina tayi tana Tura baki Yakaka tace"Ni miye nawa..? Ga wanda zaki tura ma bakin nan..!. Tafada tana nuna Danmallam da suka Hada ido da Amina ta Tura mai bakin sannan tabi bayan Aisha Mirmishi ya subucemai tuna Kirarinta Aminene ce fa..badai ta mutum ba sai ta Allah .! Yakaka ta bita da kallo tana rike baki tace"Mun shige su ta ko turamai bakin Ali kana dai gani ko..? Dariya yayi yana Fadin"Kyalesu yakaka chan tsakaninsu ne mu ba ruwanmu..!. Yafada yana kallon Umar Dayaki yarda su hada ido. Inda su Amina suka shiga ya kurama Ido Yakaka da Aliyu suka cigaba da Hirarsu tana ta mai Hirar zuwanta Saudiya ne na farko yana shan Dariya shiko Danmallam gabadaya hankalinsa na kan Amina shi yasan Laifinsa tun kafin ta fada. Suna shiga Dakin ya Aisha ta ja ta tsaya tana Hararan Amina.. Amina ta nemi gefen gado ta Zauna tana Fadin."To wai ni me nayi ne..? Ya Aisha tace"Bansani ba..Kada kiban Haushi na make ki wlh..! Amina ta tura baki batace komai ba ya Aisha ta zauna gefenta tana Fadin"Haka ake gaida mutane .? Shi fa ya Dannallam ko gaishesa baki yi ba ballatana ya Aliyu..! Amina tace"To ba nace musu sannu da zuwa ba.! Ta fada tana Hura Hanci Aisha tace"Ai sannu da zuwa ba gaisuwa bace malama. ! Amina ta tura baki tana fadin"Ni ba ruwana dashi sai fa yau yazo alhalin yafi kwana hudu da zuwa kuma kuma ma sau daya ya kirani tunda yazo wato yana chan wajen guzumayen matansa ni kuma yamin ciki ya barni da Wahala..! Sai hawaye Ya Aisha ta saki baki tana kallon Amina Dariya na cinta tana auna Dimarar da za"ayi in zama waje Daya ya tabbata Tsakanin Amina da su Sakina akwai kallo. Ya Aisha data Fahimci kishi Amina ke yi bata sani ba yasa Cikin sigar lallashi tace"To ai gashi yazo yanzu ko..? In ma zaki nuna bacin ranki bata haka Zaki nuna ba kamata yayi yanzu ki tashi kiyi wanka ki sauya kaya ki gyara Jikin ki kina tashin kamshi,Sai in dan ya shigo kuka gaisa sai ya ce ya kike..? Ko ya bby na..? Sai kice ai baka so kasan ya nake ba Tunda kazo su Anty na sun sa ka manta dani..! Irin haka dai cikin shagwaba..! Amina ta kalleta Sheke sheke kafin tace"Tab uban wa zai ce musu Anty..? Allah ya Tsareni ni ko abaya ban ce mata Anty ba ballatana yanzu da muka Hada miji kowa yayi ta kansa .! Ya Aisha na danne Dariyanta tace"To naji Kiyi hakuri ki tashi kiyi wanka ni yanzu Kitchen zani na sama musu abunda zasu ci ni da Saude kin karya ko..? Tana kunkuni tace"nasha kunin da Saude ta Damama yakaka..! Ya Aisha ta mike tana Fadin"To yi wanka in mun gama sai Saude tayi miki wainar Fulawanki..! Da haka ta fice bayan ta kara Lallaba Aminar ganin kishin Ya Danmallam take yi bata sani ba.. Falon ta koma yakaka dai da Aliyu sai hira suke sha,Danmallam kuma na Zaune yayi shuru,Tace bari ta shiga Kitchen suka amsa mata sai da ta leka Usman ta iskesa yana waya sai ta fice ta shiga Kitchen domin taya Saude wasu ayyuka,sun saba tun agida basu taso da son jiki ba. Amina tana Fushi tana kunkuni tatashi tayi wanka tazo ta Shafa Lotion din da Ya Aisha ta siya mata ta Dauko Cikin Dogayen rigunan da Aisha ta siya mata mai kalan baki da Zanen ja ajiki. Ta saka Rigar kenan ta juya saman gado ta Dauko bakin Dankwalin Rigar sai ta dan taka Rigar ta kasa ta dan Zame tayi baya zata fadi har ta Sadakar ta sha kasa taji ta ta Fada Hannun mutum tana Bude ido suka Hada ido da ya Danmallam har Gemunsa na taba Fuskarta. Kallon kallon sukama juna kowa da abunda yake sakawa gajiya yayi da Zaman falo yakaka da Aliyu na Hiransu ya tashi ya shigo Dakin da Amina ta shiga tun dazu Aliyu ya Bisa da kallon mamaki Yakaka dai batama Lura dashi ba Ta tsinke da Hira abunta. Amina ta lumshe ido jin kallon nasa har Cikin kanta Saurin tashi tayi ya taimaka mata ta tsaya sosai yana Fadin"Ki kula fa Aminene..! Da mugun mamaki ta kallesa tana Tunanin ina yasan ana ce mata Aminene..? Gira ya Daga mata yana Sakin mata Mirmishinsa na koda yaushe Daga sama har kasa yake kallonta yana kara more kallonta Har da jingina jikin Madubin Dakin yana dunkule hannayensa saman kirjinsa yana binta da kallo da dukkan zuciyarsa. Ita kuma ganin yadda yake kallonta yasa ta Tura mai Baki ta juyamai baya tana kokarin Daukan Dankwalinta ta Rufe Kitson kalaban da ya Aisha ta mata. Kawai sai jinsa tayi a bayanta gemunsa na taba wuyanta saboda ya fita Tsawo ita tana iya kirjinsa ne Dankwalin ya karba ya rankwafa yana mata rada"Ya kika juya..? Kada kimin rowan ganin Yadda Cikina ya sa kika tashi daga kwaila kika koma Big mama .! Batasan Sadda ta sakarmai Dankwalin ba ga kunya sannan ga fushi sai ta ki juyowa tana Tura baki hannunsa duka Biyu ya sa ya juyo da ita yana kallonta Runtse ido tayi taki Budewa. Dariya ta basa sai ya ja karan Hancinta yana fadin"Duk fushin ne yasa ko kallona ma an kasa yi..? Kara Turo bakin tayi sai ji tayi ya Sakar mata Kiss a saman bakin da Sauri ta Bude manyan idanuwanta ta ware akansa cikin mamaki gira ya Daga mata yana kallonta itama shi take kallo ya kara fari sannan yayi kiba Yana sanye da Shadda fara dinkin Tazarce da hula sai tashin Sayayyan kamshin Turaransa yake yi mai Dadin Shaka wanda Amina taji yana mata Dadi har Hancinta take Budewa tana kara shaka.. Gemunsa take kallo ganin ya kara Tsawo sai dai yana sheki yaji gyara sosai ya shagala da kallonta yaji ta jamai gemu da Sauri ya kalleta yana Waro ido tura baki tayi lokaci Daya ta kara Juya baya.,Mirmishi yayi kafin ya taka zuwa Gabanta yana kaallonta kokarin kara juyawa take yi ya rikota Cikin mararaicewar da baisan ya iya ba yace"Haba MEENA..a daure a fadamin Laifina mana..? Meenar da yace ne yasa ta Kallesa Cikin wani yayi a baya Aminu kadai ke kiranta da wannan sunan a kuma Lokacin sai taji yafi kowa iya Kiranta da haka sai dai yau sai taji Duk Duniya sunan a bakin mai Daraja wato Danmallam yafi dadi Lumshe ido tayi sannan ta Bude tana kallonsa hannunta Daya ya rike Dayan kuma ya Dafa Cikinta yana Fadin"Ko saboda Abunda ke Cikin ki Amina .! Baki ta kara Turawa kafin tace"Ba kai bane..Sai yau kazo ganina..! Sai ido ya kawo ruwa da Sauri yace"Am sory kiyi hakuri kinsan gajiyan hanya..Sannan kinsan Dole sai na natsa na samu natsuwa ko .? Amina ta Hura hanci tana Fadin"kuma ai baka kara kirana ba Tun ranar da kace zaka kirani. ! Sai hawaye sharr suka zubo baisan Lokacin Daya jawota jikinsa ba ya Rungumeta har Cikinta na Dukansa bai Damu ba kam ya rumgumeta yana jin wata natsuwa da salama abun mamaki itama hannayenta tasa ta Zagayo bayansa ta rikesa kanta ta baje saman kirjinsa domin sai taji kamar ta samu kafadan data Dade tana nema domin tayi kuka ta kauda kuncin zuciyarta yau ba yaya aduniya ita kadai ce zata kwanta ajikinta tayi kuka son ranta to sai Mijinta Datake ganin bata da kamarsa sannan yasan abunda
Chapter 58 · 0% Book details