← Book details Tafita Zakka Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 43 OF 105

Sashe 43

Tafita Zakka Part 2 Complete Hausa Novel · about 9 min read

Hajiya tsabar mamaki da Rudewa sai da ta Bude baki kamar sau goma tana Rufewa Jikinta yayi wani irin sanyin mamaki da al"ajabin jin kalaman Dake Fitowa Daga Bakin Uwani Duniya Haka ta lalace bata sani ba..?
Kana Zaune da Mutum Tsakani ga Allah shi kuma yana nan yana Cutarka ta karkashin kasa duk da bata Fahimci wasu mganganun ba ammh ta Fahimci Daga marliyan har Uwanin basu da zuciya mai kyau sannan Duk Jirgi Daya ya kwasosu sannan abunda ya Faru jiya wannan Tsakaninsu ne sannan Daga baya Uwani ta maida abun kan Marliya..?
Ashe Uwani ke zubar da Cikin Sakina..?
Ita tayi ma su Nazir kurciya kin zama a kusa da mallam..?
Gabadaya sai taji kanta ya kulle ta kasa wani Tunani har zata tafi ta koma Shashenta sai ta fasa so take taga Idanuwan uwani taga ko zata iya Hada ido da ita Hajiya mace ce mai Juriya da Takwalli shiyasa koda taji haka Razanan Dake zuciyarta bai nuna a saman Fuskarta ba Murya ta Bude kadan ta kara yin wata sallaman tana Fadin"Uwani ko bakya Ciki ne..?
Haj.Uwani Dake waya taji kamar mganar Hajiya afalo gabanta ya fadi ko sallama bata yima Batula ba ta Datse kiran ta fito falo da Sauri har Zaninta na neman Faduwa har ga Allah sai da gabanta ya fadi data ga Hajiya Cikin Daburcewa da kinganta kinsan bata da gaskiya ta washe baki Tana fadin"Hajiya ke ce daman..?
Yaushe kika shigo. ?
Hajiya ta kalleta na wani Lokaci ganin yadda take zufa yasa tayi wani Mirmishi aranta tace ruwa ai ya kare ma Dan kada kuma Uwani a Fili kuma cewa tayi"Eh shigowata kenan ina ta Sallama shuru..!
Ajiyar zuciyar data saki sai da Hajiya ta jita ta sauke Numfashi tana Fadin"Eh wlh ina cikin Tiolet ne Fitowa ta kenan naji sallamanki..Sannu da zuwa hajiya..
Ki zauna mana kina Tsaye..?
Hajiya ta kada kai kafin tace"A"a ba zama nazo yi ba..Naga duk yau baki Fito bane shine na leko naga ko lafiya.?
Haj.uwani na sosa kanta tace"Lafiya lau barci ne a idona Hajiya jiya ban samu barci ba Umaima tatashi tana ta Kuka cikin Dare..!
Hajiya ta kada kai kafin tace"Allah ya Sauwake ya bata lafiya..!.
Uwani ta amsa da ameen Cikin Fuskar Tsausayi taso taja hajiyar da Hira sai hajiyar tace mata tana wani abun ne bari ta koma Shashenta sai ta shigo Suka Rabu da Uwanin akan zata shigo har da raka Hajiya tana fita ta kulle kofar Shashenta lokaci Daya tana Sauke Nunfashi Fatanta Daya Hajiya bataji wayar ta da batula ba ai da aikinta na Shekaru ya rushe alokaci Daya bata ma san meyasa ta bar Falon nata abude ba..!
Hajiya har ta kai Shashenta mamakin Abunda taji Uwani na Fadi bai bar ranta ba ko iya karisawa Dakinta batayi ba ta samu saman kujera afalonta ta Zauna tayi Tagumi tunani take ko Tun Zamanta da uwani tun suna Gusai tataba Cutar da ita ne..?
Balle itama ta rama ta Hanyar abunda take Fadin ta aikata..?
Sai taga bata samu komai ba sai Mutuntawa da girmama juna da Tarin Alherinta ga Uwani ashe daman alheri na komawa sharri..?
Allah Sarki Danmallam Uwani ta Curar dashi wajen salwantar mai da Cikinsa bama ita kadai ba tace har Amina in ta samu Ciki sai yabi Rariya..To ita Allah ne..?
Ta isa da taja da abunda yace ne..?
Sai jikinta ya fara rawa kada Uwani ta Farga da Cikin Amina shima ta ga bayansa Domin bata da Imani Allah Sarki Nasir bawan Allah har da shima bata barsa ba..?
Ba ruwansa mai Sanyi da Hakuri Duniya ma bata Damesa ba duk Cikin ya"yanta shi kadai ne tabbas maallam bai wani Damu da lamuransa ba ashe da Dalili .?
Ga Nazir da ya"yansa suma din badai kaji mallam na mganarsu ba duk da yake son ganin jikikinsa a gabansa shima ashe da Dalili..?
Sai dai Uwani tayi kuskure tana Takama da Boka da mallam ne su kuma Allah suka Rike ko Daya abunda tama ya"yanta bai Dameta ba don sun yi nesa da ita bashi ke nuna sun manta da iyayensu ba Bata bakinciki da Haka Tunda suna chan suna neman na kansu ne kuma tana da yakinin addu"arta garesu shi ke Tsare dasu Duk kwanan duniya sai sun kirata sun gaisheta sannan haka mallam sannan Duk wata Daga Nazir har Danmallam suna aiko ma ta da kudi hakama mallam koda basu Cikin wahala ammh Basu manta cewa iyayensu dana Hakki akansu ba ko Nasir sai dai tace Allah ya biyasa da gidan Aljannah Shi da Jafaru ga Sa"idu wh Tallahi yau ko mutuwa Umaru da Naziru sukayi bazata ce tayi kukan maraici ba Domin sa"idu da ne kamar da goma sannan ga Nasir da Jafaru da bai Taba sakawa ta Ji zafin Rashin Zaman ya"yanta Biyu kusa da ita ba ga matansu Tsakaninsu sai mutumtawa da Martabawa har ta Matar Nazir Hidiya in bata kirata yau ba zata kirata gobe ta gaisheta kuma in suka zo garin bata Sauka a ko"ina sai shashenta sai in itace tace taje shashen Uwani ko Nasara tafi ma Darajata Fiye da Sakina domin kaf Cikin Surukanta bama wacce ta raina ta irin Sakina to me zai Dameta..?
Ita Allah ta rike kuma dashi ta Dogara boka ko mallam basu isa su ja da Ikonsa ba..!
Zata numa Uwani da dukkan mugaye irinta su Marliya da ma wasu Boyayyin wadanda Allah bai bayyanasu ba Domin ta tsorata Ta kasa ma yarda da kowa gani take Tunda Uwani ta Cutar da ita to wanda batayi Tunani ba shima zai iya Cutar da ita kafin Su farga da Cikin Amina ya kamata tayi wani abu a matsayinta na Uwa yau dai ta cire kawaici da kunya da nuna ikonta in takamar su boka da mallan ita ta rike Allah sannan bawa bai isa yayi ma Mutum abunda Allah bai masa ba.
Zata kare Amina da abunda ke Cikinta Har sai ya bayyana Lokacin da Danzaki ya girma basu isa su ga karshensa ba Umaru zai haihu Tabbas zai ga kwansa Daga Tsatso mai Daraja Tsatson Sa"idu da Hadiza ta sani addu"arta ne Allah ya amsa ta Dade tana Fatan Ganin Zuru"a mai yawa ta bangaran Umar da Amina tun kafin mallam ya Hada wannan auran Burin haka ke ranta.
Zata nuna musu ba su isa ba..Allah ya Fisu sannan suna Raye za"ayi komai Da yardan Allah sun fara ganin Rashin Nasara har abada acikin Rayuwarsu sannan burikansu bazasu taba Cika ba..!
Tsam ta mike Amina ta leka taga ta Samu barci kafin ta kada kai ta Shiga Dakinta wayarta ta Sake Dauka ta Kira Dannallam har alokacin yana Cikin Daki bai fito farimcikin abunda Hajiya ta Fadamai ya kasa sakinsa Tsammamin abunda baka Taba Tsammani ba wajen wanda bakayi Tsammani ba..!
Sarood na falo tana ta samu barci ya lekata ya gani shiyasa ya Dawo Daki ya Zauna kawai yana ta Tasbihi da yima Allah kirari Lokaci Daya soyayyar abunda ke Cikin Amina ya shiga ransa shiga ran da ko Sakina in ta Samu Ciki bai taba jiba Fata yake da Addu"am Allah ya bar masa wannan Ciki shi kadai yake tunanin Haihuwar Amina Zai faranta ran mallam da Hajiya da Baba Sa"idu fiye da Tunaninsa alokacin Kirjinsa ke Budewa Da sunan Amina da dukkan abunda ya Faru Tsakaninsu sai ga wani Kira Daga Hajiya gabansa ya fadi ya rika Allah Allah yasa ba cewa Zatayi wasa take mai sai da ta gama Ringing sannan yabi bayan kiran.
Sai a wannan karon ne Hajiya ta bari suka gaisa Cikin Yanayinta na rashin Dadi tace"Ina fatan mganar da na Fadamaka baka Fadama kowa ba ko..?
Kai tsaye ya amsa mata da Eh Hajiya ta gyara Zama tana fadin"To ka min alfarman bazaka fadama kowa ba Ciki kuwa har da matanka da Sa'idu da abokinka Aliyu ko yan"uwanka ban amince ka Sanar da kowa Amina dana Ciki ba .!
Cikin mamaki yace"Hajiya har da mallam..?
Hajiya tace"Ni zan sanar dashi Dakaina wannan..Ta bangaranka ka bar mganar nan asirri Umar..Ban yarda da kowa ba za"a iya Cutar da Abunda ke Cikin Amina nayi alkawarin da sunan Allah zan bata kariya saboda haka kayi shuru da bakinka ..!
Cikin gamsuwa yace"Na Fahimta Hajiya..Allah ya saka da alheri..!
Hajiya ta amsa da Ameen ta Cigaba da Fadin"Sannan zan Dauke Amina Daga idon mutane..Saboda wasu Dalilaina bana son bayan ni dakai da mallam wani yasan da mganar Cikinta da kuma inda zan kaita ajiya har zuwa Lokacin da Cikinta zai isa Haihuwa..!
Cikin mamaki yace"Hajiya ina kenan..?
Kai Tsaye tace"Abuja zan kaita Wajen Aisha..Chan zata Zauna na wani Lokaci kafin abubuwa su Daidaita..!
Danmallam mamaki ya cikasa sai dai baya yima iyayensa gaddama yace"Shikenan Hajiya kiyi duk abunda ya kamata..!
Ta jinjina kai kafin tace"Kada ka Damu zuwa Lokacin duk zaku san Dalilina na hakan sannan zan bata Wayar nan a hannunta in ta koma chan ku cigaba da mgana ta waya..!
Cikin girmamawa ya amsa mata kafin Cikin wani yanayi yace"Tana Lafiya ko..?
Hajiya tayi Mirmishi kafin tace"Lafiya kalau..jiya ne ta kwana da Zazzabi shine yau mukaje asibiti likita ya auna jininta sai ga Ciki kaji abun Allah ko..?ko ni Da nike Tare da ita Allah bai bani ikon gano hakan ba..Shiyasa na yarda akwai abunda Allah ya Boye kan cikin nan na Amina..Umaru ka Dage da addu"a don Allah azkar safe da yammah da Karatun Qur"ani na yarda Bawa bai isa yayima Mutum abunda Allah bai mai ba addau"armu gareku bazata taba Faduwa kasa banza ba duk Salolinka kada ka manta da Rokar ma Amina Tsarewar Allah da ita da Abunda ke Cikinta kaji ko..?
Sai duk jikinsa yayi sanyi da kalaman Hajiya duk da tana yawan fada musu su dage da Addu"a ammh na yau na Dabam ne Cikin Sanyinsa ya amsa mata ta Dinga sakamai albarka kafin suyi sallama tace Zata kirasa in sun yi mgana da mallam zuwa gobe take son ta kai Amina Abujar bazata ba ta Lokaci ba.
Bayan ta gama mgana da Danmallam Nazir ta kira suka gaisa shima abunda tace ma Danmallam tacemai shima sai yaji wani iri Hajiya kamar tana barin Wasiya suna gama waya ya Kira Danmmallam a chan madina yana Tambayansa ko sun yi waya da Hajiya yace eh sai yake tambayansa ko ta yimai nasiha da rokom ya Dage da addu"a yace eh sai nazir ya fara Tambayansa ko Hajiya bata da lafiya ne ya Tabbatar mai da lafiyanta kalau sun Dade suna tattaunawa kafin su rabu kan Shi Nazir din ranar Lahadi zai zo yaga Hajiya ya koma saboda Hajiya is d Best mother in d word.
Bashi ba ko Hidiya na Fadin bata ga Uwa kamar Hajiya ba mai kirki mai kawaici sai ta kirata sau goma su gaisa bata kira dan data Haifa ba Tunda suke da Hajiya sai dai ta Bisu da addu"a bata taba Saka ido kan samun su ba bata taba tambayansu wani abu ba sai dai su Dauka su bata ta amsa tana godiya tana saka albarka ita da Mallam samun a iyaye is a Bleesing basu taba Dogara ga abun hannun ya"yansu ba sai dai su bisu da saka albarka da addu"an nasara.
Chapter 43 · 0% Book details