← Book details Ta Fita Zakka Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 55 OF 105

Sashe 55

Ta Fita Zakka Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Yana kwance har ya fara barci yaji sallama kamar daga sama yana Bude idanuwansa ya ci karo da Hanne da Hamida suna rabe raben shigowa Hanne na Tura hamida itama tana Turata mikewa Zaune yayi Daga kan gadon yana fadin"Ku shigo mana..!
Jin haka yasa suka shigo Dakin kansu na kasa kamar wasu marayu duk suna Sanye da manya Hijabi har kasa mamakin ganinsu yayi gabansa suka Duka kamar masu neman gafara gaishesa sukayi ya amsa yana Dan Nazarinsa dazu a falon Hajiya yaga Hanne sun gaisa hamidan ne dai bai gani ba. !
Hamida kuma hanne ce taje ta jawota kan suzo su tambayi Ya Danmallam Tunda Hajiya taki fadamusu inda Amina take kila shi zai fadamusu shine suka zo a bakin Hajiya sukaji yana Dakin ya Nazeem Shine suka zo sun kuma kasa mgana saboda ba Sakewa Tsakaninsu sannan yana musu kwarjini.
Shine yaga suna Sunkuye sunkuye kai da taba juna yayi mirmishi kafin yace"Lafiya..?
Baku je makaranta bane yau..?

Hanne tace"ai jarabawa muke yi yau bamu dashi sai monday..!

Ya gyada kai sai yanzu ya tuna da Tsarin Tun farko,tunda Hajiya ta sanar dashi yadai manta ne,Cikin Sanyinsa yace"Kuyi mgana ina Fatan dai lafiya ko..?
Hamida ta sanda kanta kasa tana Fadin"Dama..Dama..Muna so mu tambayeka ne ya Danmaallan..!
Zama ya gyara yana Fadin"Allah yasa na sani..!
Hanne ta zungura ita kuma sai ta kara kasa da Murya tana Fadin"Dama kan mganar Amina ne yaya..
Kai Tsaye yace"Amina..?
Me ya faru da Aminar.?
Hanne tace"Bakomai tunda Hajiya ta tafi da ita har yanzu bata Dawo ba..Muna ta tambayanta ina take taki gayamana gashi har mun fara jarabawa ba Amina muna kewarta ne Hajiya sai tayi ta ce mana zata Dawo Zata Dawo ammh shuru..Shine mukace bari muzo mu tambayeka muji ko kasan inda take..?
Wlh kuma bamajin Dadin Zama ba Amina..!
Hanne ta karbe da cewa"Kawayen mu sai tambayan mu ita suke yi..Kowa sai yace ina Amina.?
Mu kan mu muna son sanin inda take..!

Sai da suka gama Mgana yana kallonsu kafin ya saki Mirmishi ya tuna sanda ya kira Amina yace ya Dawo abunda ta fara tambayansa yaga Hamida da Hanne..?
Don Allah ya gaishesu yace tana missing dinsu.ai shi shaida ne Saboda Rabin wayarsu mganar Hanne da Hamida ne ya Dade yana jinjina wannan kaunar Dake Tsakaninsu Amina tana matukar ji da Hanne da Hamida in tana Hiransu haka Zakaji Farinciki da Murna acikin muryanta Shi bai wani zauna dasu ba ammh yasan dai tare suke su uku ammh baisan Rayuwarsu ba gaskiya.

Gyaran Murya yayi kafin yace"Kada ku Damu Amina na Cikin koshin Lafiya..Itama tace na gaisheku sosai tana kewarku..!
Suka kallesa kafin su koma su kalli juna sai Hawaye duk ya Cicciko Idanuwansu Hanne tace"Muma muna kewarta don Allah tana ina..?
Kuma yaushe zata Dawo..?
Kai Tsaye yace"kuyi hakuri bazan iya Fada muku inda take ba..Ammh tana Cikin Koshin lafiya..Sannan zata Dawi kowani Lokaci itama bata manta daku ba koda yaushe Cikin Zencen ku take yi..!
Kawai sai suka fara mai sharan kwallah ya kallesu baki bude bai yi mamaki ba in ya Tuna yadda suka rika uban kuka Ranar da zai tafi da Amina gidansa.
Gyara zama yayi kallesu yana Fadin"ku share hawayenku..Ku Zauna Dakyau yau labarin Amina zaku bani Tundaga Farko har karshe..!
Yau ina so naji nima..!
Hama kurum yake son jin Labarin Amina,batare da yasan Dalili ba.
Jin haka yasa suka gyara zama suka Fara bashi Labarin Amina da yarintarsu Hanne tayi in ta gaji Hamida ta karbe in suka fadamai wani abu baya sanin ma yana Dariya jin jina Jidalin Amina kawai yake yi aransa ashe haka tayi nisa bai sani ba ?
Kirarinta ke basa Dariya in ya Tuna wai Aminene ikon Allah badai ta Mutum ba sai ta Allah lalle yarinyar nan sai Allah taci kuma kirarinta..
Hanne ta Karbe da Fadin"Wlh ya Danmallam Amina tana da kirki sai wanda ya Zauna da ita ya sani...Tana da son yan"uwanta sai dai akwai abu Daya Amina tana da riko in ta Tsaneka sai Alllah sannan tana da Fada da Tsiwa kuma bata Laushi ko bata da gaskiya sannan ga son jin gulma,Amina fada ko ba nata bane siyanta take yi a makarantar boko da Islamiya ba malami ko Dalibin da baisan Jidalin Amina ba,ba wanda ta Kyale tana da Fara"a sai dai bata Daukan Reni bata kuma son arainata kan Hamida da hanne Amina Zata iya yin komai tasha Fada saboda mu kuma duk wani abu da ake yi Amina ce gand leader din mu.
Ya Danmallam ga ni Amina wata Hudu ta bani Hamida kuma wata uku ta bata ammh nuna wa take kamar ta Girmemu Amina bata san Faduwa ba bata nuna gazawarta Wlh ko su ya Abida ban shaku dasu yadda na shaku da Amina ba tunda muka taso bamu taba Rabuwa ko na kwana Daya ba,Shiyasa Rashinta ya ke sakamu cikin Wani hali komai baya mana Dadi..!

Hamida ta karbe da Mirmishi tace"kuma ba"a zaman minti goma da ita ba"ayi fada da ita ba..tafi Fada dani Fiye da Hanne saboda ni bana gani na kyale Hanne kuma bata da yawan mgana,Mu yi fada mu Shirya hakanan muke zaune duk duniya ba wanda yakaimu sanin Amina sannan mun san Halinta sai muka ci Mganin zama da ita, jidalin Amina ni da Hanne kadai muke iya Daukan ta, ko Ciwo tayi kowa sai yaji wani iri saboda Amina mai Fara"a ce sannan tana da Dadin zama ga wanda ya santa sai dai kawai Fada da Zafin rai sannan bata Daukan Reni Haka Aminene take bata da tsoro bata Shakka Kirarinta badai ta mutum ba sai Allah..!
Ko abunda ya faru na Aminu Tsausayi ne wlh ba Halin Amina bane nan ta shiga bashi labarin soyayyar ta da Aminu tundaga farko Har karshe da abun da ya Faru Hamida ta kareshe da Rantsuwan wlh tallahi ya Danmallam Tsautsayi ne ammh wannan ba Halin Amina bane barta da Jidalanta ammh Namiji baya gabanta soyayyarta da Aminu kaddara ne ta Ubangiji..!
Da Dukkan Hankalinsa yake sauraranasu duka labaransu suna shiga kansa wasu labaran na Amina abun Dariya ne wasu kuma ya Dauki wasu abubuwa da mganar Data Fadamai akwai kamshin gaskiya ko wani yaro akawai irin yarintarsa ammh na Amina yayi yawa wannan Rashin Tsoro da rashin jinta yayi yawa ba nata bane ita kadai da gaske an kara mata ne duk da abun ya Tarda Halinta ne ya gasgasta mganar ta Dalilai da dama sannan ga abunda ya Lura dashi a wajenta lokacin da ya kusanceta din nan ya Fahimci akwai matsala sannan ga mgangan su Hamida sosai yaji tsausayin Amina da wani Kaunarta na shiga ransa bai sani ba..
Mganar Aminu kuma mallam yadan Fadamai kadan Daga Cikin abun da ya faru Lokacin bai wani mai da kai ba kan mganar tunda alokacin yana ganin Aaminar kamar ta riga ta gagarane aransa kuma sai yaji ya baci da jin Labarin yadda su Jafar suka Dinga Dukan mai mata gaskiya ransa ya baci da Yana Kasar sai ya hanasu ai wannan abun yayi yawa kamar sun sanu jaka su bazasu Fahimci wani abu kan Amina ba..?
Yayi mamakin da ko mallam bai Taba kaawo wani abu acikin Ransa ba sai dai kila wani abu Allah bai Cika bayyanasa da wuri ba sai Tafiya tayi tafiya mganar Aminu kuma bai Damu ba yasan ba son shi Amima ke yi ba yarinta ne da kuma kaddaran auransa da Amina shi kamar ma taimakonsa yayi sannan da kuma karfin rabon dake Tsakaninsa da ita

Mirmishi yayi har Hakoransa suka bayyana kafin yace"Wato Aminene dai ikon Allah ce badai ta mutum ba sai ta Allah..!
Hamida da Hanne sukayi Dariya suka Dukar dakai shima Dariya yayi yana tuna wai tace ma malamar corper dinsu tana warin maza kawai sai yaji wani abu mai gardi da Zumudi kan Amina na kara mamaye ransa
To ai a jidalin nata zata zama uwa..!
Lalle akwai kallo sannan Jidalin akwaishi kam
Nan ya samu ya lallaba su hanne yace zai hadasu suyi mgana da Amina ammh bai sanar dasu inda take ba sun ji Dadi da sanyi tunda Amina dai tana Lafiya sannan tunda yace zai hadasu susan bazai musu karya ba sannan yace kada su fadama ko Hajiya mganar da sukayi.
Adaran yayi ma Hajiya mganar zuwa Abuja Hajiya tace ko da yaushe ya shirya yaje mana ya ganta..
Kansa na kasa yace zai sanar da Mallam jibi sai ya tafi gobe zai je Dutse shi da su Sarood su gaida Aliya matar Aliyu tana asibiti Ciki na bata Wahala...
Hajiya ta jajanta kai Tsaye tace ma Danmallam ya Dauki Aliyu ya rakasa Abujan mana.
Cikin mamaki yace"Hajiya kin manta kin ce ko shi kada yasan komai..?
Hajiya tace"Ka sanar dashi nasan shima bazai sanar da kowa ba..Bai kyautu kaje kai kadai bane..!
Ko Jiya sai da nayi ma Sa"idu Tsiya kawaicinsa yayi yawa bai Taba Tambayana ina Amina ba ko ina na kaita ba.?
Anya akwai Uba irin Sa'idu kuwa..?
Cemin yake yarda da nayi Dake Hajiya yarda kika rikeni Tsakani ga Allah na Tabbata duk inda Zaki kai Amina Za"a kula da ita kuma bazaki kaita inda Za"a Cutar da ita ba .!
Chapter 55 · 0% Book details