Sashe 49
Ta Fita Zakka Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*****
Abuja..!
Misalin karfe Shadaya na rana suka isa gidan Aisha Dake maitama Abuja Kwatsam sai dai ta ga Hajiya abun Farincikin ma harda da Amina Aisha ta kasa Boye Murnanta ta Daka Tsalle ta Rumgume Hajiya sannan ta rumgume Amina Hajiya ta kalleta tana Fadin"Ki mata a hankali bata jin Dadi..!
Sai alokacin Aisha ta Lura da yadda Amina tayi kiba Sannan Fuskarta ta Kumbura,haka ta jasu falonta Cikin murna tana da yar aiki wata yar matashiya ita ta cika gabansu da Kayan Taba ka Lashe,Amina sai Bin Gidan ya Aisha take da kallo mai kyau dashi.
Aisha ta rasa ina Zata saka su Hajiya Saboda Murna Hajiya ta kalleta tana Fadin"Aisha to ki Zauna mana..!.
Ta Zauna gefen Amina tana Fadin"Hajiya murna ce..Ga ki ga Amina.
Hajiya ta yi mirmishi kafin tace"Yanzu dai ba wannan ba. ki sama ma Idi waje yaci abinci ya Huta kafin mu tafi..!
Da azama ta mike tana amsa ma Hajiya yar aikinta mai suna Saude ta ma mgana taa shiga da Idi Dakin Baki na waje tazo takaimai ruwa da abinci.
Tana Dawowa tace ma Hajiya"Hajiya Zaku gaisa da yakaka kakar Usman. !
Hajiya tace"Zan shiga mu gaisa Aisha kada ki damu..!
Aisha ta koma ta Zauna kusa da Amina tana Fadin"Aminene ikon Allah Amaryan ya Danmallam ya naga kin yi Shuru ne bakya mgana..!
Nice fa ya Aisha..?
Ko bakin ya mutu ne basu Hamida..?
Amina tayi Mirmishi ta gaisheta ta amsa tana Fadin"Amina kinyi Kiba Lokacin Bikin su Abida kina lange Langenki fa..!
Hajiya tace"Na sanar Dake bata da Lafiya ne Dalilin zuwana ma kenan..!
Aisha tace"Eh usman ya Fadamin sunyi mgana da mallam..Dama Amina ce Zata Zauna damu Hajiya..?
Hajiya sai da ta gama shan ruwa sannan Ta gyada mata kai Aisha ta Zaro ido kafin tace"Hajiya ba ta tare gidan ya Danmallam ba..?
Ko ansamu wata matsala ne .?
Hajiya ta mike tana Fadin"Mu je Ciki mu yi mgana..Amina kici wani abu kafin mu gama. !
Ta daga ma Hajiya kai Aisha na gaba Hajiya na bayanta har bedroom dinta Gefen gado suka Zauna Aisha Duk ta Tsorata fatanta kada ace auran ne ya Lalace.
Hajiya ta kalleta tana Fadin"Kada ki damu ba wata matsala bane..Auran su na nan sannan da sanin shi Danmallam din da Mallam kanshi na kawota wajenki. !
Sai alokacin Aisha ta ji sanyi Tace"Hajiya har gabana ya fadi na Zata ko wani abu ne ya samu auran nasu..!
Hajiya tace"Ko Daya..Sai dai matakin dana Dauka duk saboda Kara Karfafa auran su ne Aisha..Ina mai Sanar Dake Amina na Dauke da Cikin yayanku har tsawon wata Hudu da kwanaki. !
Aisha ta zaro ido kafin tace"Ciki Hajiya..Aminar..?
Kai ta gyada mata tana fadin"Kwarai kuwa baki ga alama ba ko..?
Aisha ta washe baki tana Fadin"Bangani ba Hajiya sai kibar Data kara..Alhamdulillah na taya ya Danmallam Murna daman ga Sakina na ta samun bari Allah yasa na Amina ya Zauna ta sauka lafiya..!
Hajiya ta amsa da Ameen kafin ta Kira Sunan Aisha ta amsa mata Cikin bada Hankalinta ganin yanayin Hajiyar.
Hajiya tace"Aisha na yarda Dake kaf Cikin ya"yana shiyasa na Zabi Amina ta Zauna agidanki ki kula da ita ta Reni Cikinta na wani Lokaci Sannan na zabe ki saboda baki da Surutu achan gida dagani sa mallam sai Danmallam muka san da Amina nada Ciki sai ke yanzu sabida haka ina so ya Zama sirri Tsakanina Dake..Ban so wani yaji labarin Cikin jikinta ballatana labarin tana wajenki Shima ba wanda ya sani Harta ko da Sa"idu da su hanne basu san komai ba.ki kama Bakin ki koda tambayarki akayi kice baki sani ba Dani kadai zamu Dinga mgana in wani abu ya taso kina jina..?
Aisha ta gyada kai Cikin mamaki Hajiya ta Cigaba da Fadin"Nasan Zaki yi mamakin meyasa nayi hakan..!?
To ina da Dalilina ammh ba yanzu zaku sani ba sai nan gaba..Fatana ki kula da ita don Allah da abunda ke Cikinta sannan ki koyamata Girke girke da Sauran Kissa na mata Amina haka tataso Sakaka ba wani abunda ta iya Kinsan Tana da abokan zama dole sai ta kara wayewa kan wasu abubuwan..!
Aisha tace"Insha Allahu Hajiya Zan yi Duk yadda kikace Sannan zan rike Amina kamar yadda Zan rike Hanne .!
Hajiya taji Dadi ta Dinga saka mata albarka sannan tace tatashi ta Rakata Dakin kakar mijin nata su gaisa.
Tare da Amina Hajiya tace suka shiga Dakin da Yakaka take Zaune Yar Dattijuwa kamar zata girme ma hajiya hutu ne da jin dadi suka boye girmanta ta amshe su da Fara"a tana Fadin bata son zuwansu ba,da ta fita sun gaisa Tana nan tunda ta idar da sallar walha bata matsa ba..Hajiya tace bakomai suka gaisa sai kallon Amina take yi Hajiya ta mata Bayanin kanwa take wajen Aisha tana da Ciki zata dan Zauna na wani Lokaci Tare dasu ta karishe da Fadin"Hajiya don Allah a kula..Daga Aishar har Aminan yara ne suna karkashin kulawarki Hajiya ga Amana nan..!
Yakaka na kallon Amina tace"Insha Allahu Hajiya..Na karba zan kuma kula da ita..Allah Sarki gata yarinya karama Allah ya bata..To Allah ya Rabasu lafiya..!
Su Hajiya suka amsa da Ameen Amina ta gaisheta ta amsa Cikin Sakewa tana da Sakin Fuska ga Fara"a nan da nan Hira ta barke tsakaninsu da Hajiya Har Aisha taja Amina suka fita ta nuna mata Dakin dake kusa da na yakaka nan takai mata kayanta Tace nan zata Zauna Daki ne babba mai katifa a kasa sai Cafet da Tiolet aciki Dakin ya Hadu sosai.
Nan Aisha ta bar Amina ta shiga wanka ta fito Cikin Farinciki zata Zauna da Amina sannan gefe Daya tana Tunanin yadda zata inganta Rayuwar Aminene jidali ZUWA Aminene mai aji da Haiba.
Taya Saude tayi suka yima su Hajiya girki ta Dibarma Idi da megadi ta Dibar ma Amina ta mika mata na Hajiya kuma da yakaka Saude ta mika musu Dakinsu.
Aisha tare da Amina sukaci abinci tana yi tana janta da Hira Farar shinkafa ce da wake mai miya Amina kadan taci sai Amai Aisha ta Tsausayama Amina ganin yadda ta wahala wajen amai sannan gata da karancin Shekaru Allah ya bata wannan kyautar ita da tana son Cikin ammh har yau ko bari bata taba yi ba Allah bai kawo ba. !
Ita ta Wanke inda tayi aman a Cikin Tiolet ta kamo Aminar suka tafi tana Tambayanta me zataci tace Tea shi ta Hado mata ta samu ta sha ya Tsaya Daganan Aisha ta barta ta koma Dakin Yakaka ta iske su Hajiya sai Hirar garinsu Bama suke da yakaka nan Hajiya ke fadamata ai su ma sun a zauna a bama su yakaka asalinsu yan Maiduguri ne a bama da labari ya yi Labari Hajiya ta san har gidan su yakaka anan bama kafin yan Boko Haram su Tarwatsa su kowa yayi ta kansa..
Daman ai Yakaka ba ruwanta akwai Hira tare suka ci abinci da Hajiya tayi Sallarta anan wajen Uku saura tayi Shirin Tafiya suka rabu da Yakaka Cikin Aminci kafin su tafi Hajiya ta Damka ma Amima wayar nan da Jafar ya taba kawo mata.
Ta bata ta Sanar da ita Tuntuni mijinta ya aiko da ita sai dai a wanchan Lokacin bata bata ita bane Saboda wasu Dalilai ammh yanzu gata nan zata Fadama Danmallam Saboda ya rika kira yana jin Lafiyarta Sannan tama Aisha bayanin Da Amina Zata Zana jarabawa ammh Dalilin haka yasa zata fasa sai wani Lokacin in ta Haihu.
Amina sai da taga Hajiya Zata tafin da gaske sannan ta riketa tana ta kuka Hajiya tana llashinta tace zasu yi mgana ta waya tana ji tana gani Hajiya ta tafi ta barta sai kuka Aisha ce ta Zauna ta na bata baki Saukinta Daya ma akwai ya Aishar duk da ba kamar su hanne ba ammh da Sauki akwai wanda ka sani a kusa Dakai....
Sai da tayi sallar La"sar barci ya Dauketa Yakaka kuma na jin ance Amina ta kwanta tace maza Aisha ta Tasheta ba kyau barcin yammah Sannan gata da Ciki Dole ta tasheta ita yakakan tazo Dakin Aminan ta Zauna da ita tana janta da Hira ai Tun Amina bata Saki ba har ta Saki jikinta Saboda Yakaka akwai ban Dariya da barkwanci haka ta Dage tana bama Amina labarin Lokacin suna bama farkon hareharen yan Boko haram yadda suka ringa Gudun ceton ransu sai ga Amina na Dariya harda kyatatawa Aisha taji Dadi sosai domin yakaka uwace kamar Hajiya yadda take Daukanta kamar yarta Shiyasa ta matsa sai da Usman ya Daukota daga kaduna wajen kaninsa ya dawo da ita wajensu tasan Amina Zataji Dadin ZaMa da ita sannan zata Dauki darasin wasu abubuwan..!
Hajiya sai Dare ta Kira tace sun isa lafiya har sukayi mgana da Amina ta bata Labarin yadda su hanne suka Dinga kuka ta Fada musu Ta kaita wani waje bazata Dawo ba yanzu Amina itama taji kamar tayi kuka Hajiya ta kara Lallashinta da Fadin kada ta saka Damuwa har ya shafi abunda ke Cikinta To in batayi hakuri ba ya Zatayi..?
Ai hakuri ya Zama Dole tunda haka Allah yayi da ita daga wannan sai wannan..!
*Janafty*
[10/19, 6:19 PM] +234 810 431 4972: *TFZB2018*
*Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yada'ashi..Pay N500 via Jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan lambar 09069067488*
Abuja..!
Misalin karfe Shadaya na rana suka isa gidan Aisha Dake maitama Abuja Kwatsam sai dai ta ga Hajiya abun Farincikin ma harda da Amina Aisha ta kasa Boye Murnanta ta Daka Tsalle ta Rumgume Hajiya sannan ta rumgume Amina Hajiya ta kalleta tana Fadin"Ki mata a hankali bata jin Dadi..!
Sai alokacin Aisha ta Lura da yadda Amina tayi kiba Sannan Fuskarta ta Kumbura,haka ta jasu falonta Cikin murna tana da yar aiki wata yar matashiya ita ta cika gabansu da Kayan Taba ka Lashe,Amina sai Bin Gidan ya Aisha take da kallo mai kyau dashi.
Aisha ta rasa ina Zata saka su Hajiya Saboda Murna Hajiya ta kalleta tana Fadin"Aisha to ki Zauna mana..!.
Ta Zauna gefen Amina tana Fadin"Hajiya murna ce..Ga ki ga Amina.
Hajiya ta yi mirmishi kafin tace"Yanzu dai ba wannan ba. ki sama ma Idi waje yaci abinci ya Huta kafin mu tafi..!
Da azama ta mike tana amsa ma Hajiya yar aikinta mai suna Saude ta ma mgana taa shiga da Idi Dakin Baki na waje tazo takaimai ruwa da abinci.
Tana Dawowa tace ma Hajiya"Hajiya Zaku gaisa da yakaka kakar Usman. !
Hajiya tace"Zan shiga mu gaisa Aisha kada ki damu..!
Aisha ta koma ta Zauna kusa da Amina tana Fadin"Aminene ikon Allah Amaryan ya Danmallam ya naga kin yi Shuru ne bakya mgana..!
Nice fa ya Aisha..?
Ko bakin ya mutu ne basu Hamida..?
Amina tayi Mirmishi ta gaisheta ta amsa tana Fadin"Amina kinyi Kiba Lokacin Bikin su Abida kina lange Langenki fa..!
Hajiya tace"Na sanar Dake bata da Lafiya ne Dalilin zuwana ma kenan..!
Aisha tace"Eh usman ya Fadamin sunyi mgana da mallam..Dama Amina ce Zata Zauna damu Hajiya..?
Hajiya sai da ta gama shan ruwa sannan Ta gyada mata kai Aisha ta Zaro ido kafin tace"Hajiya ba ta tare gidan ya Danmallam ba..?
Ko ansamu wata matsala ne .?
Hajiya ta mike tana Fadin"Mu je Ciki mu yi mgana..Amina kici wani abu kafin mu gama. !
Ta daga ma Hajiya kai Aisha na gaba Hajiya na bayanta har bedroom dinta Gefen gado suka Zauna Aisha Duk ta Tsorata fatanta kada ace auran ne ya Lalace.
Hajiya ta kalleta tana Fadin"Kada ki damu ba wata matsala bane..Auran su na nan sannan da sanin shi Danmallam din da Mallam kanshi na kawota wajenki. !
Sai alokacin Aisha ta ji sanyi Tace"Hajiya har gabana ya fadi na Zata ko wani abu ne ya samu auran nasu..!
Hajiya tace"Ko Daya..Sai dai matakin dana Dauka duk saboda Kara Karfafa auran su ne Aisha..Ina mai Sanar Dake Amina na Dauke da Cikin yayanku har tsawon wata Hudu da kwanaki. !
Aisha ta zaro ido kafin tace"Ciki Hajiya..Aminar..?
Kai ta gyada mata tana fadin"Kwarai kuwa baki ga alama ba ko..?
Aisha ta washe baki tana Fadin"Bangani ba Hajiya sai kibar Data kara..Alhamdulillah na taya ya Danmallam Murna daman ga Sakina na ta samun bari Allah yasa na Amina ya Zauna ta sauka lafiya..!
Hajiya ta amsa da Ameen kafin ta Kira Sunan Aisha ta amsa mata Cikin bada Hankalinta ganin yanayin Hajiyar.
Hajiya tace"Aisha na yarda Dake kaf Cikin ya"yana shiyasa na Zabi Amina ta Zauna agidanki ki kula da ita ta Reni Cikinta na wani Lokaci Sannan na zabe ki saboda baki da Surutu achan gida dagani sa mallam sai Danmallam muka san da Amina nada Ciki sai ke yanzu sabida haka ina so ya Zama sirri Tsakanina Dake..Ban so wani yaji labarin Cikin jikinta ballatana labarin tana wajenki Shima ba wanda ya sani Harta ko da Sa"idu da su hanne basu san komai ba.ki kama Bakin ki koda tambayarki akayi kice baki sani ba Dani kadai zamu Dinga mgana in wani abu ya taso kina jina..?
Aisha ta gyada kai Cikin mamaki Hajiya ta Cigaba da Fadin"Nasan Zaki yi mamakin meyasa nayi hakan..!?
To ina da Dalilina ammh ba yanzu zaku sani ba sai nan gaba..Fatana ki kula da ita don Allah da abunda ke Cikinta sannan ki koyamata Girke girke da Sauran Kissa na mata Amina haka tataso Sakaka ba wani abunda ta iya Kinsan Tana da abokan zama dole sai ta kara wayewa kan wasu abubuwan..!
Aisha tace"Insha Allahu Hajiya Zan yi Duk yadda kikace Sannan zan rike Amina kamar yadda Zan rike Hanne .!
Hajiya taji Dadi ta Dinga saka mata albarka sannan tace tatashi ta Rakata Dakin kakar mijin nata su gaisa.
Tare da Amina Hajiya tace suka shiga Dakin da Yakaka take Zaune Yar Dattijuwa kamar zata girme ma hajiya hutu ne da jin dadi suka boye girmanta ta amshe su da Fara"a tana Fadin bata son zuwansu ba,da ta fita sun gaisa Tana nan tunda ta idar da sallar walha bata matsa ba..Hajiya tace bakomai suka gaisa sai kallon Amina take yi Hajiya ta mata Bayanin kanwa take wajen Aisha tana da Ciki zata dan Zauna na wani Lokaci Tare dasu ta karishe da Fadin"Hajiya don Allah a kula..Daga Aishar har Aminan yara ne suna karkashin kulawarki Hajiya ga Amana nan..!
Yakaka na kallon Amina tace"Insha Allahu Hajiya..Na karba zan kuma kula da ita..Allah Sarki gata yarinya karama Allah ya bata..To Allah ya Rabasu lafiya..!
Su Hajiya suka amsa da Ameen Amina ta gaisheta ta amsa Cikin Sakewa tana da Sakin Fuska ga Fara"a nan da nan Hira ta barke tsakaninsu da Hajiya Har Aisha taja Amina suka fita ta nuna mata Dakin dake kusa da na yakaka nan takai mata kayanta Tace nan zata Zauna Daki ne babba mai katifa a kasa sai Cafet da Tiolet aciki Dakin ya Hadu sosai.
Nan Aisha ta bar Amina ta shiga wanka ta fito Cikin Farinciki zata Zauna da Amina sannan gefe Daya tana Tunanin yadda zata inganta Rayuwar Aminene jidali ZUWA Aminene mai aji da Haiba.
Taya Saude tayi suka yima su Hajiya girki ta Dibarma Idi da megadi ta Dibar ma Amina ta mika mata na Hajiya kuma da yakaka Saude ta mika musu Dakinsu.
Aisha tare da Amina sukaci abinci tana yi tana janta da Hira Farar shinkafa ce da wake mai miya Amina kadan taci sai Amai Aisha ta Tsausayama Amina ganin yadda ta wahala wajen amai sannan gata da karancin Shekaru Allah ya bata wannan kyautar ita da tana son Cikin ammh har yau ko bari bata taba yi ba Allah bai kawo ba. !
Ita ta Wanke inda tayi aman a Cikin Tiolet ta kamo Aminar suka tafi tana Tambayanta me zataci tace Tea shi ta Hado mata ta samu ta sha ya Tsaya Daganan Aisha ta barta ta koma Dakin Yakaka ta iske su Hajiya sai Hirar garinsu Bama suke da yakaka nan Hajiya ke fadamata ai su ma sun a zauna a bama su yakaka asalinsu yan Maiduguri ne a bama da labari ya yi Labari Hajiya ta san har gidan su yakaka anan bama kafin yan Boko Haram su Tarwatsa su kowa yayi ta kansa..
Daman ai Yakaka ba ruwanta akwai Hira tare suka ci abinci da Hajiya tayi Sallarta anan wajen Uku saura tayi Shirin Tafiya suka rabu da Yakaka Cikin Aminci kafin su tafi Hajiya ta Damka ma Amima wayar nan da Jafar ya taba kawo mata.
Ta bata ta Sanar da ita Tuntuni mijinta ya aiko da ita sai dai a wanchan Lokacin bata bata ita bane Saboda wasu Dalilai ammh yanzu gata nan zata Fadama Danmallam Saboda ya rika kira yana jin Lafiyarta Sannan tama Aisha bayanin Da Amina Zata Zana jarabawa ammh Dalilin haka yasa zata fasa sai wani Lokacin in ta Haihu.
Amina sai da taga Hajiya Zata tafin da gaske sannan ta riketa tana ta kuka Hajiya tana llashinta tace zasu yi mgana ta waya tana ji tana gani Hajiya ta tafi ta barta sai kuka Aisha ce ta Zauna ta na bata baki Saukinta Daya ma akwai ya Aishar duk da ba kamar su hanne ba ammh da Sauki akwai wanda ka sani a kusa Dakai....
Sai da tayi sallar La"sar barci ya Dauketa Yakaka kuma na jin ance Amina ta kwanta tace maza Aisha ta Tasheta ba kyau barcin yammah Sannan gata da Ciki Dole ta tasheta ita yakakan tazo Dakin Aminan ta Zauna da ita tana janta da Hira ai Tun Amina bata Saki ba har ta Saki jikinta Saboda Yakaka akwai ban Dariya da barkwanci haka ta Dage tana bama Amina labarin Lokacin suna bama farkon hareharen yan Boko haram yadda suka ringa Gudun ceton ransu sai ga Amina na Dariya harda kyatatawa Aisha taji Dadi sosai domin yakaka uwace kamar Hajiya yadda take Daukanta kamar yarta Shiyasa ta matsa sai da Usman ya Daukota daga kaduna wajen kaninsa ya dawo da ita wajensu tasan Amina Zataji Dadin ZaMa da ita sannan zata Dauki darasin wasu abubuwan..!
Hajiya sai Dare ta Kira tace sun isa lafiya har sukayi mgana da Amina ta bata Labarin yadda su hanne suka Dinga kuka ta Fada musu Ta kaita wani waje bazata Dawo ba yanzu Amina itama taji kamar tayi kuka Hajiya ta kara Lallashinta da Fadin kada ta saka Damuwa har ya shafi abunda ke Cikinta To in batayi hakuri ba ya Zatayi..?
Ai hakuri ya Zama Dole tunda haka Allah yayi da ita daga wannan sai wannan..!
*Janafty*
[10/19, 6:19 PM] +234 810 431 4972: *TFZB2018*
*Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yada'ashi..Pay N500 via Jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan lambar 09069067488*