Sashe 35
Ta Fita Zakka Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Umar yayi shuru kamar bazai yi mgana ba Jin haka yasa Aliyu yace"Tunda Sakina ga matsalan da ake Samu Shehi me zai hana ka Jaraba Sarood din itama mu gani..!
Nasan fa kana son ya"ya bama kai da abun nan yake Faruwa Dakai ba ni kaina abokinka i feel ur pain Umar ina Fatan kai ma ka ka ijiye masu yi maka addu"a watarana..!
Danmallam ya gyada,kai kamar Aliyu na ganinsa kafin yace"Shikenan Aliyu zan jaraba shawarka..bari na Kira mallam muyi mgana..!
Aliyu yaji Dadi suka rabu bayan ya Bisa da addu"an Allah yasa adace a samu waraka kamar yadda suke fata..
Nan take ya kira mallam sai dai baya gida yace mai yana Jigawa sun zo Taro ne nasu na Da"awa ammh bazai Dade ba zai koma gida in ya koma zai kirasa.
Dayake abun na ransa kuma ya Kudiri niyar fadama mallam komai yasa bayan awanni kadan ya Sake kiran mallam din Lokacin har ya koma gida Misalin goma na Dare anan madina Nageria kuma suna fitowa sallar mangariba.
Mallam Shashensa ya koma abunda ba Dabi"arsa ba sai sun gama Sallar Isha"a yake shiga gida ammh ganinsa da waya yasa aka san uziri ne ya taso ma mallam din.Tabbas Uzuri ne domin yadda yaga Umaru ya Damu yasa yasan ba lafiya ba wani abu na Faruwa.
Bayan ya Dauka sun gaisa da Tambayan gida da iyalai kamar kullum mallam yace"Umaru meke Faruwa ne.?
Wannan kiran naka bana Lafiya bane ko..?
Danmallam ya kaskastan da kansa Waje ma ya fito saboda ba ya so Sarood taji mganarsu cikin Ladabi yace"Eh ba Lafiyan ba mallam matsala ne dani tuntuni nayi iya bakin kokarina ta bangarena ammh abu ya ci Tura shiyasa na yanke Shawaran kiran ka na Sanar Dakai..!
Mallam ya koma ya zauna gefen gadonsa domin kurya ya shige kada ma wani abu ya katsesa a yadda yaji Umarun yasan da wani abu.
Cikin Dattakonsa yace"Ina jinka..Allah yasa Zan iya maka mganin matsalan ka Umaru..!
Cikin Kunya kamar yana ganinsa ya farama mallam bayanin Tundaga Farkon matsalan har karshe da Mganin Shafan Aljanun da siya mata Tayi amfani dashi ammh matsalan kuma bata kare ba har alokacin..!
Mallam yayi shuru yana jinsa har ya gama kansa ya Daure na wani Lokaci,daya sa ya kasa mgana Har sai da Umar ya Kira sunansa sannan ya amsa Cikin Alhininsa yace"Ta bangaranka da ita Sakinar lafiya kalau ko..?
Duk da yasanni ammh so yake ya Tabbatar in da lafiya ai in ba lafiya ba ta Dinga samun ciki hartana barinsa ba.
Danmallam ya amsa da Eh cikin kunya aransa yana addu"an Allah yasa kada mallan ya sako Amina Har ga Allah bai shirya fadamai ya haikema wannan yarinyar ba duk da ba Haramci yayi ba matarsace ta sunna.
Sai Addu"arsa ta karbu mallam bai Tsawaita tambayarsa ba illah kai da ya Jinjina kafin yace"Umaru kana jina ko..?
Ka bani nan da zuwa gobe zan yi Bincike na acikin littafan malaman musulunci sosai sunyi bayanai game da ira iran wadanan matsalolin naka..Insha Allahu zuwa gobe zan kiraka da kaina nayi maka bayanin komai..!
Danmallam yace"Shikenan mallam..Allah ya kara girma Allah ya kara nisan kwana..!
Mallam ya amsa da Ameen Ameen ya Cike da fadin"Kada ka damu da Yardan Allah zamu samu mafita..Domin Qur"ani waraka ne gamu bayin sa kaji ko..?
Ya amsa cikin yakinin kamar ma ya Samu mafitan daganan sukayi sallama Mallam ya koma yayi jugum yana nazarin matsalan Umar..
Tabbas yana da zurfin ciki sannan yaga Hakurin ita Saratun,bazai ce ga matsalan ba kai Tsaye tunda Basir ko Sanyi na Haifar da haka ammh nasu sai dai Raunin gaban namiji ba ta ki yin amfani ba gabadaya sannan shi da Sakina lafiya lau ita Saratun ne matsalan.
Lalle akwai wata mgana a kasa shi ba Malamin Duba bane ko na Shirka shi malamin sunna ne da Qur"ani in an kawo matsala ba kansa Tsaye yake yi ba yana Duba Littafan addini na malamai da kuma Qur"ani Domin neman mafita sannan akwai Irin irin matsalolin nan na Sihiri da malamai Dabam dabam sukayi littafai da Dadama Domin warware ma Mutane kai dasamun Mafita shima haka zai yi bazai yi zargin wani abu kai Tsaye ba sai ya bincika.
Ana Idar da sallar isha"i ya Sake dawowa cikin gida yau ko Aba basu Tsawaita Hira ba sukayi sallama ya wuce Shashensa Ranar hajiya ke da Turaka ko da tazo ta iske malama nata Nazarin wasu littafai sama sama ma suka gaisa abinci ma sai da ta matsamai yaci kadan
Abun bai bata mamaki ba taga ko barci bai kwanta ba tasan sa da son nazari wani Lokacin ammh bai hanasa kwanciya ammh sai gashi ya kasa barci data tambayasa yace yana wani Nazari mai muhimmaci ne,tayi kwanciyarta in ya gama zai zo ya sameta Dole ta shiga ta kwanta ta kyalesa.
Shi kuma sai wajen biyu na Dare ya gama Bincikensa sannan bai kwanta ba ya Dauro alwala yayi nafilfilu da addu"o'i sannan ya kwanta wajen uku da Rabi Biyar na cika ya Farka ya Tada Hajiya ya fice zuwa masallaci.
Sai Chan Safe ya Dawo Shashensa ya Tsaya masallaci sun yi meeting da Dattajan anguwannin kusa dasu.
Wanka kawai yayi ya karya Lokacin Hajiya ta koma bangaranta ya Kira Umar bai Dauka ba sai da ta katse sannan ya Kirasa yana aji ne yana karatu yana ganin kiran maallam ya nemi lamini ya fita waje ya kirasa.
Bayan gaisa kamar yadda suka saba Mallam ya fara mgana cikin Dattakonsa kamar haka.
"Umaru ka yarda da Allah shine mai yi kuma mai hanawa..Sannan ka yarda da duk abunda ya samu bawa Daga garesa ne sannan kowata Lalura daga garesa ne sannan Waraka ma yana wajensa ko..?
Danmallam ya amsa da eh Mallam ya Cigaba da nuna mai Duk abunda zai Faru da bawa koma ya faru kada ya Zargin kowa ya Dauka Daga Allah ne kuma garesa zai nemi waraka bai Fito ya mai bayanin Sihiri bane ammh Cikin Dattakonsa yace"Ka san Acikin Qur"ani akwai ayoyin da Allah ya Fadamana suna karya sihiri ko asiri ko .?
Ai kasan su..?
Cikin Sanyinsa yace"Eh mallam..!
Maalllam yace"karantomin su naji..!
Umar ya gyara Tsayuwa ya fara fadin"SURORIN AL'QUR'ANI GUDA SHIDA DAKE KARYA SIHIR KO ASIRI.
1. SURATUL TAUBA: AYATA 14.
2.SURATUL YUNUS :AYATA 57.
3.SURATUL NAHIL: AYATA 69.
4.SURATUL ISRA"I :AYATA 82.
5.SURATUL SHU'ARA :AYATA 78_82
6.SURATUL FUSILAT: AYATA 44.
mallam ya jinjina kai kafin yace"Dakyau..To kamar yadda ka lissafasu ka samu ruwan zamzam ka karantasu duka ka tofe aciki ka rika Shafe al"auranka duk dare in zaka kwanta da jikinka gabadaya sannan ka rike addu"a da azkar domin koma menene Yana jikin ka ne ba jikin ita Saratun ba..!
Danmallam ya jinjina kai yana Fadin"zanyi haka insha Allahu nagode mallam Allah ya kara girma..!
Mallam ya amsa da Ameen yana fadin"Allah ya warware mana..Allah yasa adace Allah yasa asamu waraka..!
Daga haka sukayi sallama Danmallam Ya Dade tsaye kafin ya koma cikin ajin sa ya cigaba da koyarwa karkashin Ransa kuma yana gasgasta mganar Aliyu koda mallam bai fito yace sihiri bane ammh Yanayin addu"o"in da ya basa na karya duk wani Sihiri ne ko asiri.
Yana fitowa da ga ajin ya koma Office ya Kira Aliyu ya fadamai yadda sukayi da maallam Aliyu ya rike baki kafin yace"Kaji mganata ko..?
To ka gaggauta fara abunda yace maka Fatan nasara Allah y bamu waraka..!
Daga haka suka rabu Daga cikin makaranta gida ya wuce daman yanaa da Ruwan zamzam din Sarood bata nan tana makaranta sannan in ta Dawo Zata biya gida Mami Sara na Fama da Zazzabi.
Alokacin ya samu Lokaci yayi Duk abunda mallam ya Umarcesa ya Tofesu acikin Ruwan zamzam din a kuma wannan Daran ya Fara amfani Dashi da yakinin Ciwonsa Daga Allah ne kuma waraka na wajensa..!
Sannu sannu dai..Bata hana zuwa sai dai a Dade ba"a je ba..!
Daga yanzu aikin nasu ya fara Lalacewa Alalan geronsu ya riga yayi Ruwan da bazasu taba iya Dauresa ba koda kuwa sun mai Cikon Gari acikinsa..!
*****
Sati dayan da Malam ya Dibar ma Anty Amarya na cika ya Kirata a waya Daman kiransa take jira tana Lissafe da Ranakun.
Sai dai yana fara bayanin Idanuwanta suka Rufe Daga sanda yace Wace ke Lalata Cikin Sakina tana cikin matan mallam sannan tafi kusa da Hajiya da kowa acikinsu sannan bama Take lalalata Cikin ba ko yau sakina ta kara Samun ciki bazai taba zama a mahaifanta ba akwai abunda aka bata Tacin ma cikinta wanda yake hana Cikin zama acikin maranta. !
Anty Amarya na Tsaye ne acikin Dakin su Sa"adatu in da su Sakina suke bata gama Sauraran mganar mallam ba ta yi wurigi da wayar sakina ta Tsorata tabi ta kallo ganin yadda ta fita a fusace.
Haj.Uwani na gaban madubin bedromm dinta tana Saka dan kunne a kunnenta Kamar Daga sama taji an bango kofar lokaci Daya da shigowa Cikin mamaki ta juyo tana kallon ikon Allah..
Idonta fes a na Anty Amarya wacce ke kallonta Cikin Jajayen idanuwanta da suka rine da bacin rai da wani Bakinciki.
Haj.Uwani Cikin mamaki tace"A"a Amarya Lafiya kika shigomin har Cikin kuryan Daki ba sallama..?
Kawai sai Anty Amarya ta Nufeta ta Shako wuyanta idanuwanta sun firfoto waje cikin Karaji take fadin"Ke baki chanchanci sallaama ba..Baka mai bakar aniya muguwa azzaluma mai fuska Biyu da izinin Lahi Uwani sai kin ga sakamokon ki Tun aduniya muguwa macuciya azzaluma kaawai..!
Haj.Uwani ta Fincike Wuyanta Cikin Wata irin kallo take bin Anty Amarya da shi kafin ta kece da wata irin Dariya tace"Azzalumai bakake masu bakar Aniya zaki ce Marliya sannan ki rika saka min jaye..Bazamu gama da Duniya Lafiya ba DA NI DA KE..tunda duk jirgi Daya ya kwasomu..!
Tafada tana dariya lokaci Daya tana mata kallon Nasan ki, ni tuntuni ke kuma sai yanzu kika sanni..?
*Janafty*
[10/19, 6:19 PM] +234 810 431 4972: *TFZB2013*
*Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yad'ashi..Pay N500 via jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan Lambar 09069067488*
Nasan fa kana son ya"ya bama kai da abun nan yake Faruwa Dakai ba ni kaina abokinka i feel ur pain Umar ina Fatan kai ma ka ka ijiye masu yi maka addu"a watarana..!
Danmallam ya gyada,kai kamar Aliyu na ganinsa kafin yace"Shikenan Aliyu zan jaraba shawarka..bari na Kira mallam muyi mgana..!
Aliyu yaji Dadi suka rabu bayan ya Bisa da addu"an Allah yasa adace a samu waraka kamar yadda suke fata..
Nan take ya kira mallam sai dai baya gida yace mai yana Jigawa sun zo Taro ne nasu na Da"awa ammh bazai Dade ba zai koma gida in ya koma zai kirasa.
Dayake abun na ransa kuma ya Kudiri niyar fadama mallam komai yasa bayan awanni kadan ya Sake kiran mallam din Lokacin har ya koma gida Misalin goma na Dare anan madina Nageria kuma suna fitowa sallar mangariba.
Mallam Shashensa ya koma abunda ba Dabi"arsa ba sai sun gama Sallar Isha"a yake shiga gida ammh ganinsa da waya yasa aka san uziri ne ya taso ma mallam din.Tabbas Uzuri ne domin yadda yaga Umaru ya Damu yasa yasan ba lafiya ba wani abu na Faruwa.
Bayan ya Dauka sun gaisa da Tambayan gida da iyalai kamar kullum mallam yace"Umaru meke Faruwa ne.?
Wannan kiran naka bana Lafiya bane ko..?
Danmallam ya kaskastan da kansa Waje ma ya fito saboda ba ya so Sarood taji mganarsu cikin Ladabi yace"Eh ba Lafiyan ba mallam matsala ne dani tuntuni nayi iya bakin kokarina ta bangarena ammh abu ya ci Tura shiyasa na yanke Shawaran kiran ka na Sanar Dakai..!
Mallam ya koma ya zauna gefen gadonsa domin kurya ya shige kada ma wani abu ya katsesa a yadda yaji Umarun yasan da wani abu.
Cikin Dattakonsa yace"Ina jinka..Allah yasa Zan iya maka mganin matsalan ka Umaru..!
Cikin Kunya kamar yana ganinsa ya farama mallam bayanin Tundaga Farkon matsalan har karshe da Mganin Shafan Aljanun da siya mata Tayi amfani dashi ammh matsalan kuma bata kare ba har alokacin..!
Mallam yayi shuru yana jinsa har ya gama kansa ya Daure na wani Lokaci,daya sa ya kasa mgana Har sai da Umar ya Kira sunansa sannan ya amsa Cikin Alhininsa yace"Ta bangaranka da ita Sakinar lafiya kalau ko..?
Duk da yasanni ammh so yake ya Tabbatar in da lafiya ai in ba lafiya ba ta Dinga samun ciki hartana barinsa ba.
Danmallam ya amsa da Eh cikin kunya aransa yana addu"an Allah yasa kada mallan ya sako Amina Har ga Allah bai shirya fadamai ya haikema wannan yarinyar ba duk da ba Haramci yayi ba matarsace ta sunna.
Sai Addu"arsa ta karbu mallam bai Tsawaita tambayarsa ba illah kai da ya Jinjina kafin yace"Umaru kana jina ko..?
Ka bani nan da zuwa gobe zan yi Bincike na acikin littafan malaman musulunci sosai sunyi bayanai game da ira iran wadanan matsalolin naka..Insha Allahu zuwa gobe zan kiraka da kaina nayi maka bayanin komai..!
Danmallam yace"Shikenan mallam..Allah ya kara girma Allah ya kara nisan kwana..!
Mallam ya amsa da Ameen Ameen ya Cike da fadin"Kada ka damu da Yardan Allah zamu samu mafita..Domin Qur"ani waraka ne gamu bayin sa kaji ko..?
Ya amsa cikin yakinin kamar ma ya Samu mafitan daganan sukayi sallama Mallam ya koma yayi jugum yana nazarin matsalan Umar..
Tabbas yana da zurfin ciki sannan yaga Hakurin ita Saratun,bazai ce ga matsalan ba kai Tsaye tunda Basir ko Sanyi na Haifar da haka ammh nasu sai dai Raunin gaban namiji ba ta ki yin amfani ba gabadaya sannan shi da Sakina lafiya lau ita Saratun ne matsalan.
Lalle akwai wata mgana a kasa shi ba Malamin Duba bane ko na Shirka shi malamin sunna ne da Qur"ani in an kawo matsala ba kansa Tsaye yake yi ba yana Duba Littafan addini na malamai da kuma Qur"ani Domin neman mafita sannan akwai Irin irin matsalolin nan na Sihiri da malamai Dabam dabam sukayi littafai da Dadama Domin warware ma Mutane kai dasamun Mafita shima haka zai yi bazai yi zargin wani abu kai Tsaye ba sai ya bincika.
Ana Idar da sallar isha"i ya Sake dawowa cikin gida yau ko Aba basu Tsawaita Hira ba sukayi sallama ya wuce Shashensa Ranar hajiya ke da Turaka ko da tazo ta iske malama nata Nazarin wasu littafai sama sama ma suka gaisa abinci ma sai da ta matsamai yaci kadan
Abun bai bata mamaki ba taga ko barci bai kwanta ba tasan sa da son nazari wani Lokacin ammh bai hanasa kwanciya ammh sai gashi ya kasa barci data tambayasa yace yana wani Nazari mai muhimmaci ne,tayi kwanciyarta in ya gama zai zo ya sameta Dole ta shiga ta kwanta ta kyalesa.
Shi kuma sai wajen biyu na Dare ya gama Bincikensa sannan bai kwanta ba ya Dauro alwala yayi nafilfilu da addu"o'i sannan ya kwanta wajen uku da Rabi Biyar na cika ya Farka ya Tada Hajiya ya fice zuwa masallaci.
Sai Chan Safe ya Dawo Shashensa ya Tsaya masallaci sun yi meeting da Dattajan anguwannin kusa dasu.
Wanka kawai yayi ya karya Lokacin Hajiya ta koma bangaranta ya Kira Umar bai Dauka ba sai da ta katse sannan ya Kirasa yana aji ne yana karatu yana ganin kiran maallam ya nemi lamini ya fita waje ya kirasa.
Bayan gaisa kamar yadda suka saba Mallam ya fara mgana cikin Dattakonsa kamar haka.
"Umaru ka yarda da Allah shine mai yi kuma mai hanawa..Sannan ka yarda da duk abunda ya samu bawa Daga garesa ne sannan kowata Lalura daga garesa ne sannan Waraka ma yana wajensa ko..?
Danmallam ya amsa da eh Mallam ya Cigaba da nuna mai Duk abunda zai Faru da bawa koma ya faru kada ya Zargin kowa ya Dauka Daga Allah ne kuma garesa zai nemi waraka bai Fito ya mai bayanin Sihiri bane ammh Cikin Dattakonsa yace"Ka san Acikin Qur"ani akwai ayoyin da Allah ya Fadamana suna karya sihiri ko asiri ko .?
Ai kasan su..?
Cikin Sanyinsa yace"Eh mallam..!
Maalllam yace"karantomin su naji..!
Umar ya gyara Tsayuwa ya fara fadin"SURORIN AL'QUR'ANI GUDA SHIDA DAKE KARYA SIHIR KO ASIRI.
1. SURATUL TAUBA: AYATA 14.
2.SURATUL YUNUS :AYATA 57.
3.SURATUL NAHIL: AYATA 69.
4.SURATUL ISRA"I :AYATA 82.
5.SURATUL SHU'ARA :AYATA 78_82
6.SURATUL FUSILAT: AYATA 44.
mallam ya jinjina kai kafin yace"Dakyau..To kamar yadda ka lissafasu ka samu ruwan zamzam ka karantasu duka ka tofe aciki ka rika Shafe al"auranka duk dare in zaka kwanta da jikinka gabadaya sannan ka rike addu"a da azkar domin koma menene Yana jikin ka ne ba jikin ita Saratun ba..!
Danmallam ya jinjina kai yana Fadin"zanyi haka insha Allahu nagode mallam Allah ya kara girma..!
Mallam ya amsa da Ameen yana fadin"Allah ya warware mana..Allah yasa adace Allah yasa asamu waraka..!
Daga haka sukayi sallama Danmallam Ya Dade tsaye kafin ya koma cikin ajin sa ya cigaba da koyarwa karkashin Ransa kuma yana gasgasta mganar Aliyu koda mallam bai fito yace sihiri bane ammh Yanayin addu"o"in da ya basa na karya duk wani Sihiri ne ko asiri.
Yana fitowa da ga ajin ya koma Office ya Kira Aliyu ya fadamai yadda sukayi da maallam Aliyu ya rike baki kafin yace"Kaji mganata ko..?
To ka gaggauta fara abunda yace maka Fatan nasara Allah y bamu waraka..!
Daga haka suka rabu Daga cikin makaranta gida ya wuce daman yanaa da Ruwan zamzam din Sarood bata nan tana makaranta sannan in ta Dawo Zata biya gida Mami Sara na Fama da Zazzabi.
Alokacin ya samu Lokaci yayi Duk abunda mallam ya Umarcesa ya Tofesu acikin Ruwan zamzam din a kuma wannan Daran ya Fara amfani Dashi da yakinin Ciwonsa Daga Allah ne kuma waraka na wajensa..!
Sannu sannu dai..Bata hana zuwa sai dai a Dade ba"a je ba..!
Daga yanzu aikin nasu ya fara Lalacewa Alalan geronsu ya riga yayi Ruwan da bazasu taba iya Dauresa ba koda kuwa sun mai Cikon Gari acikinsa..!
*****
Sati dayan da Malam ya Dibar ma Anty Amarya na cika ya Kirata a waya Daman kiransa take jira tana Lissafe da Ranakun.
Sai dai yana fara bayanin Idanuwanta suka Rufe Daga sanda yace Wace ke Lalata Cikin Sakina tana cikin matan mallam sannan tafi kusa da Hajiya da kowa acikinsu sannan bama Take lalalata Cikin ba ko yau sakina ta kara Samun ciki bazai taba zama a mahaifanta ba akwai abunda aka bata Tacin ma cikinta wanda yake hana Cikin zama acikin maranta. !
Anty Amarya na Tsaye ne acikin Dakin su Sa"adatu in da su Sakina suke bata gama Sauraran mganar mallam ba ta yi wurigi da wayar sakina ta Tsorata tabi ta kallo ganin yadda ta fita a fusace.
Haj.Uwani na gaban madubin bedromm dinta tana Saka dan kunne a kunnenta Kamar Daga sama taji an bango kofar lokaci Daya da shigowa Cikin mamaki ta juyo tana kallon ikon Allah..
Idonta fes a na Anty Amarya wacce ke kallonta Cikin Jajayen idanuwanta da suka rine da bacin rai da wani Bakinciki.
Haj.Uwani Cikin mamaki tace"A"a Amarya Lafiya kika shigomin har Cikin kuryan Daki ba sallama..?
Kawai sai Anty Amarya ta Nufeta ta Shako wuyanta idanuwanta sun firfoto waje cikin Karaji take fadin"Ke baki chanchanci sallaama ba..Baka mai bakar aniya muguwa azzaluma mai fuska Biyu da izinin Lahi Uwani sai kin ga sakamokon ki Tun aduniya muguwa macuciya azzaluma kaawai..!
Haj.Uwani ta Fincike Wuyanta Cikin Wata irin kallo take bin Anty Amarya da shi kafin ta kece da wata irin Dariya tace"Azzalumai bakake masu bakar Aniya zaki ce Marliya sannan ki rika saka min jaye..Bazamu gama da Duniya Lafiya ba DA NI DA KE..tunda duk jirgi Daya ya kwasomu..!
Tafada tana dariya lokaci Daya tana mata kallon Nasan ki, ni tuntuni ke kuma sai yanzu kika sanni..?
*Janafty*
[10/19, 6:19 PM] +234 810 431 4972: *TFZB2013*
*Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yad'ashi..Pay N500 via jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan Lambar 09069067488*