Sashe 22
Ta Fita Zakka Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Mamanmu taji Dadin haka yasa tace"To ai kin gani irin wannan abun na Gudar miki yasa naso araba wannan auran kika ki bani Dama..!
Amina tace"Bakomai Mamanmu hajiya da Mallam sun wuce komai a wajenmu..Sannan ni nayi alkwarin Aba bazai kara bacin rai saboda ni ba..!
Mamanmu tayi shuru tana kallon Amina kafin tace"Hakane kuma ammh ki Daina tankama Sakina Da shi din ne dai da nace ki yi tamai Fitsara har ya gaji ya sako min ke na aura miki mai sonki Aminullah..!
Amina tayi Tsai tana kallonta sai taji bata ji Dadi ba datace a asakota Saki fa ba Kyau ance sai al'arshin Allah ya girgiza sannan ita karan Hauka ya Cijeta da zata ma ya Danmallam rashin kunya sai dai Sakinar itace Daidai da ita.
Daganan bata kara mgana ba Mamanmu kuma sai janta take da Labari Amina ba domin Rokon Umar ta Boyema mamammu komai ba,,sai saboda Tana jin kunyarta da Tunanin in taji abunda ya faru zata yi mata Fada kila ma ranta ya baci shiyasa bata gayamata ba..
Ita kuma mamanmu adole Allah zatayi ma wayau batasan bakin Alkalami ya riga ya bushe ba,Haduwar jini ta Haifar da gudan jinin da zai yi Sanadiyar Fallasan duka sirrukansu.
Amina sai da taci ta koshi tayi sallah kan gadonta ta fada tana Fadin"Nayi kewarka gado na..!
Take fada tana Shafa gadon Hamida na kallonta kafin tace"Sai a Daukesa akai miki chan..!
Amina tace"Da naji dadi kuwa..!
Hamida ce tace"Hajiya sai da tambayeki fa Amina..!
Amina ta mike Tana fadin"Bari na shiga..!
Uniform dinta ta cire ta sauya dana gida akwai wasu cikin kwabarta na gida hamida ta rakata gidansu Hanne.
A bakin shashen Hajiya suka ga Haj.Uwa tunda taji zuwan Amina ta kasa zama tana ganinsu ta washe baki Tana fadin"Ga Amina Amarya..!
Sai kunya ya kama Amina ta Dukar dakai tana gaisheta
Hannu taja tana Fadin"Au bazaki shiga Shashena mu gaisa ba..?
Yar"uwarki ma Umaima bata da lafiya jiya ko barci bamu yi ba..!
Amina tace"Allah sarki bansani ba..!
Hamida tace"Mun manta ne bamu Fada miki ba..Jiya kwana tayi ihu mallam da su ya Akilu suka kwana suna mata karatu..!
Amina taji Tsausayi ya kamata sosai Ta kalli Hamida tana fadin"muje na Dubata Hamida..!
Da Sauri Hajiya Uwa tace"ai ita sun shigo sun dubata da Safe..Ke dai muje Diyata Amaryan Umaru Faruqu..!
Tafada tana jan Amina Hamida sai bata bisu ba tunda taga kamar Haj.uwa ta fi son Amina ita kadai.
Sai ta juya ita ta shige Shashen Hajiya babba.
Kafa kafa Haj uwani ta dinga yi da Amina har shashenta kai tsaye kuma har Dakin da Umaima ke kwance tana barcin Wahala duk ta kara ramewa sai Dogon wuya Amina ta kalleta Cikin Tsausayinta tace"Allah ya bata lafiya..!
Haj Uwani ta kalli Umaima sai ta fara Sharan kwallah kafin tace"Wlh ciwon nan na Umai ya fara damuna Sa"o'inta duk suna Dakunansu har da ku ma kannen bayanta ita ko kalli Halin Datake ciki..!
Amina tace"sai hakuri Allah ya bata lafiya..bari na tafi..!
Haj Uwa tace"Bazaki tafi ba sai kin sha wani abu muje..!
Ta kaita har falo ta zaunar da ita kan kujera tana fadin"Umaru dai ana Madina ko..?
Amina tace"Uhm..!
Daganan bata kara mgana ba mamaki abun ke bata Duk da Tasan Hajiya uwa bata da matsala ammh bata janta ajiki kamar na yau sai kawai taji bata yarda da ita ba.
Tana nan zaune sai gata ta fito da Jug da kofi ta kawo gaban Amina ta ja Center table ta dora lokaci Daya tana Fadin"Lemon kankana nayi tun Safe kinganshi nan yayi sanyi zaki ji Dadinsa Amina..!
Amina ta yi kasake tana kallonta ganin haka yasa ta Zauna gefenta tana Fadin"Kada ki damu nan Umaru ke karyawa indai yana gari dagashi har matansa abinci shashena basu da Shamaki dashi..!
Amina dai batace komwi ba ta Dauka ta Tsiyaya kadan Ta Daga kofin takai Bakinta Hj.uwa na kallonta zuciyarta Cike da Farinciki zata aiwatar da Tsarinta Cikin Sauki kamar yadda ta Saba.!
Amina acikin ranta taji bazata sha wannan abun ba,ba domin tana Zarginta ba sai domin cikinta ya cika sannan in ta fada mata bazata yarda ba Sai dai kamar an kwato bakinta Ta Furta.
Bismilallahi..!
Sannan ta Kurba kadan Haj.Uwa taji kamar an sakata acikin Aljannah Ta Bude zatayi mgana kenan Kukan Umaima ya katseta tatashi da gudu tatafi Dakin tana cema Amina tana zuwa..!
Tana shigewa Amina ta Dawo da na bakinta wanda bata gama Hadiye ba jin wani makaki a makogwaronta waige waige ta farayi ganin Haj.Uwa bata fito ba yasa tatashi Sadaf Sadaf ta shiga Kitchen dinta ta Juyesa a wajen wanke wanke taga yana wani yauki mamaki ya kamata da sauri ta Bisa da Ruwa ya wuce sannan ta samu ruwa ta Kuskure bakinta ta koma Falo da Sauri ta ijiye kofin ta zauna kenan sai gata fito Idonta kan kofin tana ganinsa ba komai ta wani Saki ajiyar rai kafin ma ta zauna Amina ta mike tana cemata zata tafi Cikin Murna da Cikar Burinta tace"To shikenan Aminatu Sai na shigo shashen Hajiyar..!
Harda Dari biyar ta bama Amina tace bazata karba ba ta matsa mata ta karba Amina ta fice cikin mamaki sannan uwa uba kuma Makogwaronta bai yi mata Dadi ba Tunda tasha wannan lemon
Tana Fita Haj.Uwa ta Daga Kofin kafin ta Sheke da wata Dariya a Fili ta Furta"Kema kin Hau keken beran kamar yadda na Dora na bayanki..!
Sai ta wani Saki shewa Duniya Sabuwa..burinta ya kusa cika Nazeem Sauransa wattani kadan ya gama makaranta Uzairu kuma ya gama Degree dinsa na farko Services ma yake shirin tafiya ta fara Hango kanta a matakin datake Wahala Shekaru masu yawa.
Abunda bata sani ba Kafin nata Tsarin Ta manta Allah ma da nashi..?
To nashi ya riga nata sannan abunda Allah ya rubuta shi zai faru wannan gudan jinin sai ya fito Duniya wannan Cewarsa ne..!
Amina haka taje Shashen Hajiya ba cikin natsuwarta ba cikinta nata Juya mata sai dai bata cema kowa komai ba suka gaisa da Hajiya tana ta Tambayanta ko ba matsala tace mata eh Dakin su hanne suka shige suna Hira Amina ta kasa natsuwa sai da ta shiga Tiolet ta dinga Tura Hannunta Cikin baki sai da ta samu Wannan dan Lemon daya shiga Cikinta ya fito harda Abincin data ci sai da ta Amayar dashi tayi sauri ta wanke wajen ta fito su hanne suna chan suna Hira basu ji karan Kakwazon aman nata ba.
Sai alokacin ta samu salama.
Allah yayi ikon sa Ko tasha wannan nganin bazai zauna acikinta ba sai ya fita saboda ba koda yaushe kake aikata abu kaci nasara ba daga Lokacin daka fara Hango nasara Daga lokacin kila Lokacin bayyanan wasu abubuwan ne.
La"asar nayi suka shirya suka tafi islamiya irin su mariya sai kallon Amina suke domin Sa"adatu ta Fesa musu Amina ta auri yayansu mijin Anty Sakina to sanin Halin Amina Shiyaasa ba wanda ya Tareta da mganar har aka tashi.
Suna Dawowa gida Amina taso ta Tsaya wai taga Aba da Mallam Hajiya tace maza ta wuce idi ya maidata gida Mallam yana Hadeja sun je bude wani masallaci ba yanzu zai dawo ba shi da Aba Dole Amina taje tayima mamanmu sallama ko mangariba agidan ta tayi ta sai kunci take yi.
Aranar dai bata Hadu da Sakina ba sai Washegari da Idi ya maidota da yammah ta ganta afilo suka kalli juna kasa kasa kowacce ta kauda kanta bata Damu da abinci ba, tana ciko Cikinta Kafin ta Dawo da Safe kuma Tea kadai tashe sha watarana ma haka take Tafiya.
Asatin nan kaf haka Rayuwar Amina ta cigaba da gudana kudin hannunta sai da ta gama kashe ma su hanne gbadaya sannan Hankalinta ya kwanta Ranar jumma'a daga makaranta bata koma gida ba Ta jira sai da Mallam da Aba suka Dawo ta gaisheshesu Aba sai mamakin Amina yake a idonsa yaga kamar ta kara mishi girma sannan tayi hankali Kadan Mallam kuma kamar ya maidata Ciki saboda so Shiyasa bata koma gida ba sai Ranar Lahadi da yammah Mallam yace tayi kwana Biyu saboda Har da Hajiya bata so ba Ammh Tunda mallam ya saka baki shikenan.
Jafar kuwa sam ya manta da Kudin wayar da Danmallam ya barmasa ya siya ma Amina sai da Umar din yaji Shuru ya kirasa sannan ya Tuna Hakuri ya basa aranar bayan ya Dawo Daga wajen aiki ya biya ya siyama Amina waya karama Nokia sai washegari ya siya mata layi yayi mata Rigister sannan yazo ya kawoma Hajiya wayar Tunda Aminar na makaranta Hajiya ita har ta ma manta da Batun wayar sanda ya kawo mata Cikin wardrope dinta ta saka wayar sai kuma Allah ya mantar da ita har Amina ta dawo ba ta bata ba.
Wajen kwana Hudu da Jafar ya sanar ma da Danmallam ya siya waya ya kaima Hajiya ta bama Amina sannan ya Turama sa Layin Aminar sai dai tun Washegarin ranar yake ta faman kiran wayar a kashe sai ya fara Tunanin kodai Hajiya bata bama Amina wayar bane.?
Shi kuma ya kasa Hakuri ya rasa meke Damunsa Daidai da rana Daya Tunda ya Dawo madina Zuciyarsa bata manta Amina ba.
Wannan yarinyar daya ke kira kazama Kwaila itace ya kasa mantawa da ita ko Sakina da suka Dade tare baya jin nauyi da wani Damuwa da ita akan yadda yake ji kan Amina wani al"amari ne da Ubangiji ya barma kansa sani abu Daya ya sani yana matukar son yaji muryanta sannan yaji lafiyanta baya fatan ace yau yabar baya da kura.
Sannnan yarinyar itace ya Hada Abu mai muhimmanci da ita abunda bai Taba Hasaahen zai iya Faruwa Tsakaninsa da ita ba..
Abunda bai sani ba Addu"an Hajiya da Mallam ne Allah ya amsa sannan Addu"ar yaya ce Allah ya amsa ya Amintar da Ruhin Amina da Umaru waje Daya..Aminci na har Abada..!
*Janafty*
[10/19, 6:19 PM] +234 810 431 4972: *TFZB2008*
*Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yad'ashi..Pay N500 via jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan Lambar 09069067488*
Amina tace"Bakomai Mamanmu hajiya da Mallam sun wuce komai a wajenmu..Sannan ni nayi alkwarin Aba bazai kara bacin rai saboda ni ba..!
Mamanmu tayi shuru tana kallon Amina kafin tace"Hakane kuma ammh ki Daina tankama Sakina Da shi din ne dai da nace ki yi tamai Fitsara har ya gaji ya sako min ke na aura miki mai sonki Aminullah..!
Amina tayi Tsai tana kallonta sai taji bata ji Dadi ba datace a asakota Saki fa ba Kyau ance sai al'arshin Allah ya girgiza sannan ita karan Hauka ya Cijeta da zata ma ya Danmallam rashin kunya sai dai Sakinar itace Daidai da ita.
Daganan bata kara mgana ba Mamanmu kuma sai janta take da Labari Amina ba domin Rokon Umar ta Boyema mamammu komai ba,,sai saboda Tana jin kunyarta da Tunanin in taji abunda ya faru zata yi mata Fada kila ma ranta ya baci shiyasa bata gayamata ba..
Ita kuma mamanmu adole Allah zatayi ma wayau batasan bakin Alkalami ya riga ya bushe ba,Haduwar jini ta Haifar da gudan jinin da zai yi Sanadiyar Fallasan duka sirrukansu.
Amina sai da taci ta koshi tayi sallah kan gadonta ta fada tana Fadin"Nayi kewarka gado na..!
Take fada tana Shafa gadon Hamida na kallonta kafin tace"Sai a Daukesa akai miki chan..!
Amina tace"Da naji dadi kuwa..!
Hamida ce tace"Hajiya sai da tambayeki fa Amina..!
Amina ta mike Tana fadin"Bari na shiga..!
Uniform dinta ta cire ta sauya dana gida akwai wasu cikin kwabarta na gida hamida ta rakata gidansu Hanne.
A bakin shashen Hajiya suka ga Haj.Uwa tunda taji zuwan Amina ta kasa zama tana ganinsu ta washe baki Tana fadin"Ga Amina Amarya..!
Sai kunya ya kama Amina ta Dukar dakai tana gaisheta
Hannu taja tana Fadin"Au bazaki shiga Shashena mu gaisa ba..?
Yar"uwarki ma Umaima bata da lafiya jiya ko barci bamu yi ba..!
Amina tace"Allah sarki bansani ba..!
Hamida tace"Mun manta ne bamu Fada miki ba..Jiya kwana tayi ihu mallam da su ya Akilu suka kwana suna mata karatu..!
Amina taji Tsausayi ya kamata sosai Ta kalli Hamida tana fadin"muje na Dubata Hamida..!
Da Sauri Hajiya Uwa tace"ai ita sun shigo sun dubata da Safe..Ke dai muje Diyata Amaryan Umaru Faruqu..!
Tafada tana jan Amina Hamida sai bata bisu ba tunda taga kamar Haj.uwa ta fi son Amina ita kadai.
Sai ta juya ita ta shige Shashen Hajiya babba.
Kafa kafa Haj uwani ta dinga yi da Amina har shashenta kai tsaye kuma har Dakin da Umaima ke kwance tana barcin Wahala duk ta kara ramewa sai Dogon wuya Amina ta kalleta Cikin Tsausayinta tace"Allah ya bata lafiya..!
Haj Uwani ta kalli Umaima sai ta fara Sharan kwallah kafin tace"Wlh ciwon nan na Umai ya fara damuna Sa"o'inta duk suna Dakunansu har da ku ma kannen bayanta ita ko kalli Halin Datake ciki..!
Amina tace"sai hakuri Allah ya bata lafiya..bari na tafi..!
Haj Uwa tace"Bazaki tafi ba sai kin sha wani abu muje..!
Ta kaita har falo ta zaunar da ita kan kujera tana fadin"Umaru dai ana Madina ko..?
Amina tace"Uhm..!
Daganan bata kara mgana ba mamaki abun ke bata Duk da Tasan Hajiya uwa bata da matsala ammh bata janta ajiki kamar na yau sai kawai taji bata yarda da ita ba.
Tana nan zaune sai gata ta fito da Jug da kofi ta kawo gaban Amina ta ja Center table ta dora lokaci Daya tana Fadin"Lemon kankana nayi tun Safe kinganshi nan yayi sanyi zaki ji Dadinsa Amina..!
Amina ta yi kasake tana kallonta ganin haka yasa ta Zauna gefenta tana Fadin"Kada ki damu nan Umaru ke karyawa indai yana gari dagashi har matansa abinci shashena basu da Shamaki dashi..!
Amina dai batace komwi ba ta Dauka ta Tsiyaya kadan Ta Daga kofin takai Bakinta Hj.uwa na kallonta zuciyarta Cike da Farinciki zata aiwatar da Tsarinta Cikin Sauki kamar yadda ta Saba.!
Amina acikin ranta taji bazata sha wannan abun ba,ba domin tana Zarginta ba sai domin cikinta ya cika sannan in ta fada mata bazata yarda ba Sai dai kamar an kwato bakinta Ta Furta.
Bismilallahi..!
Sannan ta Kurba kadan Haj.Uwa taji kamar an sakata acikin Aljannah Ta Bude zatayi mgana kenan Kukan Umaima ya katseta tatashi da gudu tatafi Dakin tana cema Amina tana zuwa..!
Tana shigewa Amina ta Dawo da na bakinta wanda bata gama Hadiye ba jin wani makaki a makogwaronta waige waige ta farayi ganin Haj.Uwa bata fito ba yasa tatashi Sadaf Sadaf ta shiga Kitchen dinta ta Juyesa a wajen wanke wanke taga yana wani yauki mamaki ya kamata da sauri ta Bisa da Ruwa ya wuce sannan ta samu ruwa ta Kuskure bakinta ta koma Falo da Sauri ta ijiye kofin ta zauna kenan sai gata fito Idonta kan kofin tana ganinsa ba komai ta wani Saki ajiyar rai kafin ma ta zauna Amina ta mike tana cemata zata tafi Cikin Murna da Cikar Burinta tace"To shikenan Aminatu Sai na shigo shashen Hajiyar..!
Harda Dari biyar ta bama Amina tace bazata karba ba ta matsa mata ta karba Amina ta fice cikin mamaki sannan uwa uba kuma Makogwaronta bai yi mata Dadi ba Tunda tasha wannan lemon
Tana Fita Haj.Uwa ta Daga Kofin kafin ta Sheke da wata Dariya a Fili ta Furta"Kema kin Hau keken beran kamar yadda na Dora na bayanki..!
Sai ta wani Saki shewa Duniya Sabuwa..burinta ya kusa cika Nazeem Sauransa wattani kadan ya gama makaranta Uzairu kuma ya gama Degree dinsa na farko Services ma yake shirin tafiya ta fara Hango kanta a matakin datake Wahala Shekaru masu yawa.
Abunda bata sani ba Kafin nata Tsarin Ta manta Allah ma da nashi..?
To nashi ya riga nata sannan abunda Allah ya rubuta shi zai faru wannan gudan jinin sai ya fito Duniya wannan Cewarsa ne..!
Amina haka taje Shashen Hajiya ba cikin natsuwarta ba cikinta nata Juya mata sai dai bata cema kowa komai ba suka gaisa da Hajiya tana ta Tambayanta ko ba matsala tace mata eh Dakin su hanne suka shige suna Hira Amina ta kasa natsuwa sai da ta shiga Tiolet ta dinga Tura Hannunta Cikin baki sai da ta samu Wannan dan Lemon daya shiga Cikinta ya fito harda Abincin data ci sai da ta Amayar dashi tayi sauri ta wanke wajen ta fito su hanne suna chan suna Hira basu ji karan Kakwazon aman nata ba.
Sai alokacin ta samu salama.
Allah yayi ikon sa Ko tasha wannan nganin bazai zauna acikinta ba sai ya fita saboda ba koda yaushe kake aikata abu kaci nasara ba daga Lokacin daka fara Hango nasara Daga lokacin kila Lokacin bayyanan wasu abubuwan ne.
La"asar nayi suka shirya suka tafi islamiya irin su mariya sai kallon Amina suke domin Sa"adatu ta Fesa musu Amina ta auri yayansu mijin Anty Sakina to sanin Halin Amina Shiyaasa ba wanda ya Tareta da mganar har aka tashi.
Suna Dawowa gida Amina taso ta Tsaya wai taga Aba da Mallam Hajiya tace maza ta wuce idi ya maidata gida Mallam yana Hadeja sun je bude wani masallaci ba yanzu zai dawo ba shi da Aba Dole Amina taje tayima mamanmu sallama ko mangariba agidan ta tayi ta sai kunci take yi.
Aranar dai bata Hadu da Sakina ba sai Washegari da Idi ya maidota da yammah ta ganta afilo suka kalli juna kasa kasa kowacce ta kauda kanta bata Damu da abinci ba, tana ciko Cikinta Kafin ta Dawo da Safe kuma Tea kadai tashe sha watarana ma haka take Tafiya.
Asatin nan kaf haka Rayuwar Amina ta cigaba da gudana kudin hannunta sai da ta gama kashe ma su hanne gbadaya sannan Hankalinta ya kwanta Ranar jumma'a daga makaranta bata koma gida ba Ta jira sai da Mallam da Aba suka Dawo ta gaisheshesu Aba sai mamakin Amina yake a idonsa yaga kamar ta kara mishi girma sannan tayi hankali Kadan Mallam kuma kamar ya maidata Ciki saboda so Shiyasa bata koma gida ba sai Ranar Lahadi da yammah Mallam yace tayi kwana Biyu saboda Har da Hajiya bata so ba Ammh Tunda mallam ya saka baki shikenan.
Jafar kuwa sam ya manta da Kudin wayar da Danmallam ya barmasa ya siya ma Amina sai da Umar din yaji Shuru ya kirasa sannan ya Tuna Hakuri ya basa aranar bayan ya Dawo Daga wajen aiki ya biya ya siyama Amina waya karama Nokia sai washegari ya siya mata layi yayi mata Rigister sannan yazo ya kawoma Hajiya wayar Tunda Aminar na makaranta Hajiya ita har ta ma manta da Batun wayar sanda ya kawo mata Cikin wardrope dinta ta saka wayar sai kuma Allah ya mantar da ita har Amina ta dawo ba ta bata ba.
Wajen kwana Hudu da Jafar ya sanar ma da Danmallam ya siya waya ya kaima Hajiya ta bama Amina sannan ya Turama sa Layin Aminar sai dai tun Washegarin ranar yake ta faman kiran wayar a kashe sai ya fara Tunanin kodai Hajiya bata bama Amina wayar bane.?
Shi kuma ya kasa Hakuri ya rasa meke Damunsa Daidai da rana Daya Tunda ya Dawo madina Zuciyarsa bata manta Amina ba.
Wannan yarinyar daya ke kira kazama Kwaila itace ya kasa mantawa da ita ko Sakina da suka Dade tare baya jin nauyi da wani Damuwa da ita akan yadda yake ji kan Amina wani al"amari ne da Ubangiji ya barma kansa sani abu Daya ya sani yana matukar son yaji muryanta sannan yaji lafiyanta baya fatan ace yau yabar baya da kura.
Sannnan yarinyar itace ya Hada Abu mai muhimmanci da ita abunda bai Taba Hasaahen zai iya Faruwa Tsakaninsa da ita ba..
Abunda bai sani ba Addu"an Hajiya da Mallam ne Allah ya amsa sannan Addu"ar yaya ce Allah ya amsa ya Amintar da Ruhin Amina da Umaru waje Daya..Aminci na har Abada..!
*Janafty*
[10/19, 6:19 PM] +234 810 431 4972: *TFZB2008*
*Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yad'ashi..Pay N500 via jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan Lambar 09069067488*