Sashe 5
Rumana Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"kai Abu beyi kyauba wallahi kaga inda tana nan ai da duk ba'a yi wannan doguwar wahalar ba, toh amman duk da haka zancigita kaima saika cigita, ammafa namiji za'a samu ba mace ba kamin Allah yasa asamu wadda zata aureshin a haka.''
"Toh shikenan insha Allahu nima zan cigita bari na koma kafin ya tashi daga bacci ya hargitsa d'akin nasa.''
Har ya koma gidan bacci Haidar yake yi, lokacin har anyi sallar magriba yaje yayi shima, sai da ya sai mishi fura mai kyau da dad'i a hanyarsa da dawowa sannan ya shiga d'akinshi. Ido ya zuba mishi ganin yanda yake ta mutsu-mutsu amma yaki bud'e idanunshi, dafashi yayi yana cewa.
"Haidar...! Kai haidar..!!'' D'agoshi yayi yana kallon fuskarshi kafin yace.
''Yanzu haka fitsari zaka yi kaketa wannan mutsu-mutsun...,Yauwa ai dama na sani.''
Maganar shi ya yanke lokacin da yaga fitsari na biyo kafar wandon Haidar d'in dake kwance. Wasu irin hawaye ne yaji sun zubo mishi kamin kuka me sauti ya biyo baya yana furta.
''Innalillahi wayyo Allah ka kawo min d'auki.''
Sai da ya gyara mishi jikinshi sannan ya bashi furar yasha ya koshi, sannan ya bashi magungunan shi wanda kusan duk na bacci yafi yawa a ciki sabida yanayin ciwon nashi hankali yafi kwanciya idan bacci yake yi.
Fuskarshi yake kallo duk tayi gashi sam baya yadda a aske mishi shi yasa duk sai yai wani irin duguzun dashi sai dai farar fatar shi tana nan yanda take saima k'ara sheki da take yi sabida zama waje d'aya.
Bugun da yaji afuskar shi ne ya katse mishi tunanin da yake yi, ya maida kallonshi akan Haidar d'in yana zaune yana kallonshi shima yana dariya irin dai ta marasa hankalin nan. Gorar da ya gama shan furar ce ya kwalama uban ganin ya zuba mishi ido amma yai nisan kiwo a wajan tunani. Jawoshi yayi jikinshi ya rungume yana shafar bayan Haidar d'in zuciyar shi fal addu'ar Allah ya bawa yaron shi lafiya.
Ranar a nan cikin d'akin ya kwana wanda sai da Haidar d'in ya gama hargitsa ko'ina kamin maganin da ya sha ya fara yi masa aiki lokacin shima Abban shi ya samu ya runtsa.
*****
Tafe nake ina nanata haddar karatuna wanda ya kasance shine abokin hirata a koda yaushe, ban damu da ruwan da yaima jikina sharkaf ba balle na damu da mutanen dake kallona musamman matasa, basu gabana haka zalika bawai ta tasu nake yiba Kawata dije na had'u da ita a dai-dai kwanar gidan mu tana cewa.
"Kai Rumana duk kin jike karfa mura ta sargafeki kin dai san batai miki da sauki ko?'' Dariya nayi kafin nace.
''Uuhum aini yanzu mun zama k'awaye da murar ma kina ganin yanzu wankan asuba inna kesawa inyi kullum duk safiyar duniya wai sai taji ina d'an tsami-tsaki.''
"Allah yagani inna bata kyautawa wallahi kenifa inda nice da tuni na koma garinmu wallahi, da gata da komai amma in like inda ba'a san daraja taba, kai ina wallahi bazan iya ba.'' Cewar dije. Kallonta nayi kamin nace.
''Lallaima Dije, kindai san bani da uwa bani da uba yanzu komawa nayi, kilama gara nan d'in da can tunda can d'inma da ai neman kai suka dinga yi dani, kedai kawai Allah ya kyauta amma wallahi kunji dad'i tunda kuna tare da iyayenku.'' Cikin tausayawa Dije tace.
"Haka ne Ruma to kema Allah ya saka miki ya kuma k'ara miki hakuri da juriya Insha Allah zakiga sakamako nan gaba.'' Da murmushi a fuskata nace.
''Amin dije na gode, wai ya maganar haddarki kingama kuwa?" Hab'a ta kama tana cewa.
''Tab inafa na tsaya wasa kedai na san kingama ai.''
Anan muka rabu kasancewar akwai gidaje hud'u tsakanin gidan mu da nasu. Wani mugun rankwashi ta bini dashi lokacin da na ajiye ruwan da alama shine sanun daya dace dani a wannan lokacin. Baba dake kwancewa kaza dabaibayi yace.
''Inalillahi mai tayi miki haka dan Allah?" Mtwsss taja dogon tsaki kafin tace.
''Yoo a ban zama zan sauke mata kenan? Ai kaima kasan bazai yiwu ba tunda na sauke mata ruwa dole na bata ladan ta.'' Kai ya girgiza kafin yace.
''Akwai Allah wallahi zaki mamakin ranar da zai kamaki akan zalintar yarinyar nan da kike yi.''
Nidai shigewa nayi d'akina ba tare da ko d'igon hawaye ya zabo min ba, duk da irin mugun zafin da naji kuwa, to yaushema zanyi kuka bayan inda sabo yaci ace na saba da duka da rankwashi....
*MAMAN KHADY*🙇🏻♀
[4/2, 11:15 AM] Re@l💍 K@usy🌹: 💞💞💞 *RUMANA* 💞💞💞
Na
*MAMAN KHADY*🙇🏻♀
(Mk)
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡
(Home of expert and perfect writer's)
Page 5.
Domin duk a tunanin shi zaiga yana wani hauka na daban lokacin da ya kama masa, sai yaga inaa..dan tuni ya lafe a jikin Mudin idanunsa a lumshe bakinsa a bud'e har wani miyau yake fitarwa da alama yana jin dad'in abinda Mudin yake yi mishi har cikin ranshi.
Cike da tausayin Hydar Mudi ya taimaka mishi har sai da yaga ya koma wani baccin sannan shima ya samu ya kwanta, sai dai zuciyarshi cike da tsoron Allah akan abinda ya aikata yanzu duk da cewar taimako yayi kuma shi ba wani abin yaji a cikin zuciyarsa ba, ya fara tunanin. yanzu ya san inda lafiyar Haidar qalau ai ko wajan motarshi bai isa yaje ba balle ai maganar kwanciya kusa dashi harma ya tab'a mishi jikinsa. Lallai komai na Allah tsare yake sannan bawa baya tab'a wuce k'addararshi.
****
Washe gari cikin garin BAKORI: Da kyar na samu na yakice baccin dake damuna na mike lokacin iyayena suna d'akin inna har lokacin suna maida yanda akai akan yanayin hidimar data gudana ajiya.
Da sallama na shiga tare da makurewa a gefe ina gaida su. Inna da kanta ta kawo min abin karyawa ta tana fadin.
"Sannu Ruma ya gajiyar ciwon kan ya sauka ko?''
Kaina na d'aga mata kawai naja kofin shayi zuwa gabana da biredi, yau da kayan dadi zamu karya kenan. Zuciya ta tayi murnar hakan dan ba sabawa aka yi ba.
Baba rabi'u da baba ne suka shigo, suma gaida su nayi na cigaba da karyawa ta ina jin duk abinda suke fad'a.
"Ruma duba rigunan nan kigani duk cikin kyautukan da kika samu ne.'' Cewar gwaggo lami.
Wasu riguna ne dogaye masu masifar kyau dan ban tab'a ganin irin suba bakina har kunne nake cewa.
''Amman dai sunyi kyau sosai na gode Allah ya saka da alkhairi.''
Baya na tashi da sauri ina niyyar guduwa lokacin da baba ya zube min wasu kud'i masu tsananin yawan gaske dami-dami dasu a jikin kaure, ba sabun ba.
Innace ta rikeni tana dariyar itama tare da cewa.
"Kedai wallahi Ruma kin cika tsoron masifa, dallah gani zaki yi kud'in da kika samu ne dubu dari bakwai da hamsin ne, amma mun yanke shawarar za'a sai miki kadara na dubu d'ari biyar sauran kuma za'a rabawa dangi, d'ari da hamsin nida malam d'arin kuma sai a ajiye miki kisai sababbin kaya da sauran abin da kike buk'ata muna fatan hakan yai miki?''
Kaina a k'asa ina hawaye babu abinda ya fad'o min sai tunanin iyayena inama suna da rayuwa suma su dangwali albarkacin haihuwata. Duk sai jikinsu yai sanyi ganin ina kuka, da kyar na daure nace da ita.
''Inna duk yanda kuka yi hakan yayi amma dan Allah cikin wanda aka bani ina so acire rabi aje akai masallaci asai wani abin mai muhimmanci ko tabarmi ko butuci ko alkur'anai domin suma iyayena su sami ladan.''
''Allahu Akbar Allah yai miki albarka Ruma" Cewar baba.
Da yamma Baba yana zaune inda yake yin alwala yana yin asuwaki nikuma ina zaune cikin baranda ina had'a littatafan dana samu bakina har kunne tsabar farin ciki da jin dad'i, Inna na gefe tana ta gyaran kajin da ta siyo dama inna akwai son dad'i ita dai a rayuwarta ta sami jin dad'i ace yau itace hajiya Suwaiba, Shi yasa ko kujerar makkan dana samu tana cewa itace zataje ta yiwa iyayena addua' babu wanda ya musa domin ansan bama zata yarda ba.
Sallama aka yi har sau uku kafin baba ya mike da sauri yana nanata ana zuwa. Har ya fita sai kuma gashi da sauri yana fad'in.
''Suwaiba kawo tabarma alhaji Yahaya ne da kaninsa wanda ya yiwa Ruma kyautar kujerar makka.'' Da sauri kuwa ta mike har jikinta na rawa
''Laallah! Kace manyan baki ne damu to sannunsu.''
Kasa zama tayi sabida zullumin me kuma ya dawo dasu har wani lekawa take yi ko Allah zaisa taji wani abu. Niko ina gefe ina dariya domin lokuta da dama lamarinta kan bani dariya.
Gefena ta dawo tace. ''Ruma kaddafa malam ya gayama alhajinnan cewar ba kece me zuwa makkan nan ba dan nasan zai iya wallahi.''
"Kai haba inna ya za ai yace haka dama ai dole ke zaki ai babu wanda yafi cancanta da zuwa saike, nidai kin san tsarabata ta da bance ko inna?''
Cike dajin dad'i ta dafani tana cewa. "Ah kwarai ma kuwa, insha Allah d'iya ta shi yasa nake sonki wallahi.''
A can zaure kuwa, Alhaji Yahaya ne ya kalli malam Sule bayan sun gama gaisawa yace.
"Nasan kila zakai mamakin ganinmu anan, toh malam wannan dai sunansa Yusufa nasan ba sai nayi maka bayanin shi ba, kasan na gayyaceshi wajan walimar jiya kuma gashi ya samu ya halarta harda da gudummawarshi wacce ba'a zata ba, to kuma daga baya sai ya nuna sha'awar Rumana akan shigowa cikin iyalinshi ma'ana yana so ya nemawa yaronshi Haidar auranta idan ba ayi mata mijiba shi yasa yana gaya min nace ai duk gida ne bari kawai muzo da wuri, gashinan ayi komai agaban shi domin da tun safema zai tafi amma sabida wannan maganar sai ya dakata.
Cikin farin ciki malam yake furta. "Alhamdulillah lallai abu yayi kya, Allah ya taimaka kuma ya shige mana gaba sannan ya zab'a mafi alkhairi. Toh amman wani hanzari ba gudu ba, nasan dai kasan cewa yarinyar nan marainiya ce ba uwa babu uba ita mai d'akin nawa itace yayar mahaifinta kaga kenan akwai yiwuwar dole sai anyi shawara da iyayenta nacan kadda suga kamar munayi musu karan tsaye akanta, kuma wallahi kaga ansami sab'ani domin sai d'azu suka wuce can gida maska.''
"Toh shikenan insha Allahu nima zan cigita bari na koma kafin ya tashi daga bacci ya hargitsa d'akin nasa.''
Har ya koma gidan bacci Haidar yake yi, lokacin har anyi sallar magriba yaje yayi shima, sai da ya sai mishi fura mai kyau da dad'i a hanyarsa da dawowa sannan ya shiga d'akinshi. Ido ya zuba mishi ganin yanda yake ta mutsu-mutsu amma yaki bud'e idanunshi, dafashi yayi yana cewa.
"Haidar...! Kai haidar..!!'' D'agoshi yayi yana kallon fuskarshi kafin yace.
''Yanzu haka fitsari zaka yi kaketa wannan mutsu-mutsun...,Yauwa ai dama na sani.''
Maganar shi ya yanke lokacin da yaga fitsari na biyo kafar wandon Haidar d'in dake kwance. Wasu irin hawaye ne yaji sun zubo mishi kamin kuka me sauti ya biyo baya yana furta.
''Innalillahi wayyo Allah ka kawo min d'auki.''
Sai da ya gyara mishi jikinshi sannan ya bashi furar yasha ya koshi, sannan ya bashi magungunan shi wanda kusan duk na bacci yafi yawa a ciki sabida yanayin ciwon nashi hankali yafi kwanciya idan bacci yake yi.
Fuskarshi yake kallo duk tayi gashi sam baya yadda a aske mishi shi yasa duk sai yai wani irin duguzun dashi sai dai farar fatar shi tana nan yanda take saima k'ara sheki da take yi sabida zama waje d'aya.
Bugun da yaji afuskar shi ne ya katse mishi tunanin da yake yi, ya maida kallonshi akan Haidar d'in yana zaune yana kallonshi shima yana dariya irin dai ta marasa hankalin nan. Gorar da ya gama shan furar ce ya kwalama uban ganin ya zuba mishi ido amma yai nisan kiwo a wajan tunani. Jawoshi yayi jikinshi ya rungume yana shafar bayan Haidar d'in zuciyar shi fal addu'ar Allah ya bawa yaron shi lafiya.
Ranar a nan cikin d'akin ya kwana wanda sai da Haidar d'in ya gama hargitsa ko'ina kamin maganin da ya sha ya fara yi masa aiki lokacin shima Abban shi ya samu ya runtsa.
*****
Tafe nake ina nanata haddar karatuna wanda ya kasance shine abokin hirata a koda yaushe, ban damu da ruwan da yaima jikina sharkaf ba balle na damu da mutanen dake kallona musamman matasa, basu gabana haka zalika bawai ta tasu nake yiba Kawata dije na had'u da ita a dai-dai kwanar gidan mu tana cewa.
"Kai Rumana duk kin jike karfa mura ta sargafeki kin dai san batai miki da sauki ko?'' Dariya nayi kafin nace.
''Uuhum aini yanzu mun zama k'awaye da murar ma kina ganin yanzu wankan asuba inna kesawa inyi kullum duk safiyar duniya wai sai taji ina d'an tsami-tsaki.''
"Allah yagani inna bata kyautawa wallahi kenifa inda nice da tuni na koma garinmu wallahi, da gata da komai amma in like inda ba'a san daraja taba, kai ina wallahi bazan iya ba.'' Cewar dije. Kallonta nayi kamin nace.
''Lallaima Dije, kindai san bani da uwa bani da uba yanzu komawa nayi, kilama gara nan d'in da can tunda can d'inma da ai neman kai suka dinga yi dani, kedai kawai Allah ya kyauta amma wallahi kunji dad'i tunda kuna tare da iyayenku.'' Cikin tausayawa Dije tace.
"Haka ne Ruma to kema Allah ya saka miki ya kuma k'ara miki hakuri da juriya Insha Allah zakiga sakamako nan gaba.'' Da murmushi a fuskata nace.
''Amin dije na gode, wai ya maganar haddarki kingama kuwa?" Hab'a ta kama tana cewa.
''Tab inafa na tsaya wasa kedai na san kingama ai.''
Anan muka rabu kasancewar akwai gidaje hud'u tsakanin gidan mu da nasu. Wani mugun rankwashi ta bini dashi lokacin da na ajiye ruwan da alama shine sanun daya dace dani a wannan lokacin. Baba dake kwancewa kaza dabaibayi yace.
''Inalillahi mai tayi miki haka dan Allah?" Mtwsss taja dogon tsaki kafin tace.
''Yoo a ban zama zan sauke mata kenan? Ai kaima kasan bazai yiwu ba tunda na sauke mata ruwa dole na bata ladan ta.'' Kai ya girgiza kafin yace.
''Akwai Allah wallahi zaki mamakin ranar da zai kamaki akan zalintar yarinyar nan da kike yi.''
Nidai shigewa nayi d'akina ba tare da ko d'igon hawaye ya zabo min ba, duk da irin mugun zafin da naji kuwa, to yaushema zanyi kuka bayan inda sabo yaci ace na saba da duka da rankwashi....
*MAMAN KHADY*🙇🏻♀
[4/2, 11:15 AM] Re@l💍 K@usy🌹: 💞💞💞 *RUMANA* 💞💞💞
Na
*MAMAN KHADY*🙇🏻♀
(Mk)
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡
(Home of expert and perfect writer's)
Page 5.
Domin duk a tunanin shi zaiga yana wani hauka na daban lokacin da ya kama masa, sai yaga inaa..dan tuni ya lafe a jikin Mudin idanunsa a lumshe bakinsa a bud'e har wani miyau yake fitarwa da alama yana jin dad'in abinda Mudin yake yi mishi har cikin ranshi.
Cike da tausayin Hydar Mudi ya taimaka mishi har sai da yaga ya koma wani baccin sannan shima ya samu ya kwanta, sai dai zuciyarshi cike da tsoron Allah akan abinda ya aikata yanzu duk da cewar taimako yayi kuma shi ba wani abin yaji a cikin zuciyarsa ba, ya fara tunanin. yanzu ya san inda lafiyar Haidar qalau ai ko wajan motarshi bai isa yaje ba balle ai maganar kwanciya kusa dashi harma ya tab'a mishi jikinsa. Lallai komai na Allah tsare yake sannan bawa baya tab'a wuce k'addararshi.
****
Washe gari cikin garin BAKORI: Da kyar na samu na yakice baccin dake damuna na mike lokacin iyayena suna d'akin inna har lokacin suna maida yanda akai akan yanayin hidimar data gudana ajiya.
Da sallama na shiga tare da makurewa a gefe ina gaida su. Inna da kanta ta kawo min abin karyawa ta tana fadin.
"Sannu Ruma ya gajiyar ciwon kan ya sauka ko?''
Kaina na d'aga mata kawai naja kofin shayi zuwa gabana da biredi, yau da kayan dadi zamu karya kenan. Zuciya ta tayi murnar hakan dan ba sabawa aka yi ba.
Baba rabi'u da baba ne suka shigo, suma gaida su nayi na cigaba da karyawa ta ina jin duk abinda suke fad'a.
"Ruma duba rigunan nan kigani duk cikin kyautukan da kika samu ne.'' Cewar gwaggo lami.
Wasu riguna ne dogaye masu masifar kyau dan ban tab'a ganin irin suba bakina har kunne nake cewa.
''Amman dai sunyi kyau sosai na gode Allah ya saka da alkhairi.''
Baya na tashi da sauri ina niyyar guduwa lokacin da baba ya zube min wasu kud'i masu tsananin yawan gaske dami-dami dasu a jikin kaure, ba sabun ba.
Innace ta rikeni tana dariyar itama tare da cewa.
"Kedai wallahi Ruma kin cika tsoron masifa, dallah gani zaki yi kud'in da kika samu ne dubu dari bakwai da hamsin ne, amma mun yanke shawarar za'a sai miki kadara na dubu d'ari biyar sauran kuma za'a rabawa dangi, d'ari da hamsin nida malam d'arin kuma sai a ajiye miki kisai sababbin kaya da sauran abin da kike buk'ata muna fatan hakan yai miki?''
Kaina a k'asa ina hawaye babu abinda ya fad'o min sai tunanin iyayena inama suna da rayuwa suma su dangwali albarkacin haihuwata. Duk sai jikinsu yai sanyi ganin ina kuka, da kyar na daure nace da ita.
''Inna duk yanda kuka yi hakan yayi amma dan Allah cikin wanda aka bani ina so acire rabi aje akai masallaci asai wani abin mai muhimmanci ko tabarmi ko butuci ko alkur'anai domin suma iyayena su sami ladan.''
''Allahu Akbar Allah yai miki albarka Ruma" Cewar baba.
Da yamma Baba yana zaune inda yake yin alwala yana yin asuwaki nikuma ina zaune cikin baranda ina had'a littatafan dana samu bakina har kunne tsabar farin ciki da jin dad'i, Inna na gefe tana ta gyaran kajin da ta siyo dama inna akwai son dad'i ita dai a rayuwarta ta sami jin dad'i ace yau itace hajiya Suwaiba, Shi yasa ko kujerar makkan dana samu tana cewa itace zataje ta yiwa iyayena addua' babu wanda ya musa domin ansan bama zata yarda ba.
Sallama aka yi har sau uku kafin baba ya mike da sauri yana nanata ana zuwa. Har ya fita sai kuma gashi da sauri yana fad'in.
''Suwaiba kawo tabarma alhaji Yahaya ne da kaninsa wanda ya yiwa Ruma kyautar kujerar makka.'' Da sauri kuwa ta mike har jikinta na rawa
''Laallah! Kace manyan baki ne damu to sannunsu.''
Kasa zama tayi sabida zullumin me kuma ya dawo dasu har wani lekawa take yi ko Allah zaisa taji wani abu. Niko ina gefe ina dariya domin lokuta da dama lamarinta kan bani dariya.
Gefena ta dawo tace. ''Ruma kaddafa malam ya gayama alhajinnan cewar ba kece me zuwa makkan nan ba dan nasan zai iya wallahi.''
"Kai haba inna ya za ai yace haka dama ai dole ke zaki ai babu wanda yafi cancanta da zuwa saike, nidai kin san tsarabata ta da bance ko inna?''
Cike dajin dad'i ta dafani tana cewa. "Ah kwarai ma kuwa, insha Allah d'iya ta shi yasa nake sonki wallahi.''
A can zaure kuwa, Alhaji Yahaya ne ya kalli malam Sule bayan sun gama gaisawa yace.
"Nasan kila zakai mamakin ganinmu anan, toh malam wannan dai sunansa Yusufa nasan ba sai nayi maka bayanin shi ba, kasan na gayyaceshi wajan walimar jiya kuma gashi ya samu ya halarta harda da gudummawarshi wacce ba'a zata ba, to kuma daga baya sai ya nuna sha'awar Rumana akan shigowa cikin iyalinshi ma'ana yana so ya nemawa yaronshi Haidar auranta idan ba ayi mata mijiba shi yasa yana gaya min nace ai duk gida ne bari kawai muzo da wuri, gashinan ayi komai agaban shi domin da tun safema zai tafi amma sabida wannan maganar sai ya dakata.
Cikin farin ciki malam yake furta. "Alhamdulillah lallai abu yayi kya, Allah ya taimaka kuma ya shige mana gaba sannan ya zab'a mafi alkhairi. Toh amman wani hanzari ba gudu ba, nasan dai kasan cewa yarinyar nan marainiya ce ba uwa babu uba ita mai d'akin nawa itace yayar mahaifinta kaga kenan akwai yiwuwar dole sai anyi shawara da iyayenta nacan kadda suga kamar munayi musu karan tsaye akanta, kuma wallahi kaga ansami sab'ani domin sai d'azu suka wuce can gida maska.''