← Book details Rumana Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 22 OF 34

Sashe 22

Rumana Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Allah yasa nayi girki nan da nan nacika gabanshi da cima be taho da kowaba sabida beso wani yasan da matsalar ma balle labarin ya yadu cikin dangi shiyasa yataho shi kadai duk da ciwo ya manyanta sannan ya kwana biyu beyi tafiya me tsawoba.

Bayan sallar isha'i suka shigo lokacin nagama bashi abinci kenan ko barin wurin bamuyiba.
Kuma gaisawa mukai kamin ya kalli haidar ah lallai jiki yayi kyau sosai haka muke bukata Allah ya kara lafiya.
Da alama shedanun dake jikinshi sun barshi saidai basubar gidannan ba tunda suna waiwayarshi amma babu me zama jikinshi.

Yanzu idan sawu ya dauke zamuje bakin kofar gidannan mu toneshi domin tsiyar daganan ta fara.

Bakin Abba har kunne yake amsawa da to malam alhamdulillah ai hakan yayi mungode Allah,Kaima Allah yasaka maka da Alkhairi kuma yabar zumunci tsakaninmu.

Sai dare sosai sukai mana sallama tunda Abba yamatsa malam wajanshi zai kwana.

Tsaye nai bakin gado ina kallonshi atsorace banso yakumamin irinna jiya,Shiko yana kwance yai daidai abinshi yana kallona.
Gajiya nai da tsayuwar na lallaba gefenshi na kwanta ammafa kamar acemin kett in mike sabida tsoro.

Wani murmushin gefen baki yayi kamin ya rungumoni jikinshi.

To Dauko abun gini domin yanzune daidai lokacinda sawu ya dauke Allah yasa har mugama babu Wanda zai ganmu kaga babu Wanda yasan anyi kenan,Cewar malam liman yana zura hularshi akanshi.

Wani ruwa dake hannunshi na addu'ah ya watsa adaidai kofar shigowa get din gidan aiko nan take wani siririn hayaki yatashi fuuuu yai saima.
Abba Wanda yacika da tsoron yai baya atsorace yana salati.

Wani irin haskene aka dallarosu dashi Wanda yasa kirjin Abba bugawa fiye da farko.[4/2, 3:09 PM] Re@l💍 K@usy🌹: Rumana 50

Kasa kallon shi nayi bayan nagama sallar,Yayinda shikuma ya zubamin mayun idanunshi yana kallon duk wani motsina.
Ganin zaman zai min yawa yasani mikewa ina nade abin sallar har lokacin ban kalli inda yakeba.
Hucin numfashinya kawai naji wajan fuskata Dan Sam banji lokacinda ya mikeba balle harya iso kusa daniba.

'Baya nayi zanfadi ya taroni jikinshi yana murmushi tare da shafar Dan siririn gemunshi Wanda yakuma kayata fuskarshi.
Hijab din dake jikina ya cire sannan yajani gefen gado muka zauna,Idanunshi Lumshe yake lasar wuyana zuwa bayan kunnena nan da nan naji numfashi na yana Neman daukewa.

Wata siririyar dariya yasaki kamin ya matseni jikinshi,Muryarshi amatukar sanyaye yafara magana"Ruma sabida baki da kirki kinsami tsarki amma shine kikaimin shiru bakisan halin danake ciki bane?

Atsorace na kwace jikina ina kallonshi,"Ikon Allah kaji dadynsu da wata magana kawai dannasami tsarki saina gayamaka to kayi me da samun tsarkin nawa, Dukafa yau kwananmu sha biyar kai ko cewa nayi kayi wani Abu ai kace a a.

Hararara yakeyi kamar idanunshi zasu fado kamin yace "Dakata baby banson shirme ni babu ruwana da kwananki nawa da haihuwa kawai hakkina zaki bani nasandai wajan yai lafiya yanzu Dan inna bazatabarki haka ba.

Ganin yanda yake magana bilhakki da gaskiya yasani zabura na mike ina niyyar guduwa Dan wallahi wani lokacin Sam namiji beda kawaici akan wasu abubuwan oh jifa karfin hali.
.
Hard'oni yayi da kafafunshi nafado kanshi ina sakin k'aramin ihu,Manne bakina da nashi kawai yayi tare da cigaba da luluba da saurin gaske saikace Wanda betabayiba,Gashi ya toshemin baki danashi.
Kai haidar yasan takan tsiya nidai bansan yanda akaiba saidai naji namika wuya sai yanda yayi dani shaf na manta da maganar agida muke sannan koda yaushe wani zai iya shigowa cikin dakin.

Tuni ya dade dayin nisa musamman yanda jikinshi ke rawa tako ina.

Innalillahi wa inna lilaihirraji'un,Kai Dan ubanka dagata.
.
Shine sautin danaji saman kaina saikuma kukan jariri daya biyo baya,Shiko ai inaga beji metaceba saida na tureshi da karfina sannan yadan matsa kokarin kuma jawoni yakeyi nai gaggawar matsawa ina sauke numfashi na kaina duk jikina rawa yakeyi tsabar yanda yagama gigitamin tunani.

Sai lokacin yaga umma danhaka cike da sanyin jiki ya gyara kwanciyarshi tare da danne cikinshi Dan yasamu asirinshi yadan rufu😄.
Tana tsaye har lokacin rike da haba ko yaronma takasa cigaba da jijjigashi duk da kukan da yakeyi.
Saida nagama maida numfashi sannan tace amsarshi kibashi yasha kuka yakeyi.

Maida kallonta tayi kanshi tana mamakin jaraba irinta haidar duka yau kwana nawa da zai nuna wannan zalamar afili kenan inda anbiyeshi nazauna can da babu wani jego dazaibari inyi kenan? Oh ikon Allah.

Saida ta daidaici shima yadan nutsu sannan tafara magana"Kai yanzu sabida Allah haidar yarinya da danyen jegonta kake kokarin haikemata wato da karfinka zakayima ko?

Dakyar yatashi zaune yana yamutse fuska amma bece komaiba.
Niko ina gefe kunya tagama dabaibayeni wallahi.

Fada taitamishi sannan tabar dakin tana nanata aisaika fito kazo mutafi tun kamin ka aikata barnar dazata hanani kuma kallon masu gidan.

Wata uwar harara ya wurgamin lokacinda muka hada ido dashi saiwani ciccin magani yakeyi irin besami yanda yakeso dinnan ba.

Tashi yai tsaye ya zura hannunshi cikin aljihun rigarshi kudi yazaro masu yawan gaske ya dire gefena tare da sumbatar fuskar yaron sannan ya kalleni "Kidaina murna umma tashigo yanzu wallahi kiji tsoron haduwarmu ta gaba.

Juyawa yai yafice yana wani bubbudawa irin shi gashi ishashshe dinnan.
Nidai wata k'atuwar ajiyar zuciya na sauke ina godema Allah tunda nasami kubuta yanzu.

Kunya tasani kasa fita yin sallama da umman saida ita taleko taimin sallama.
[4/2, 3:09 PM] Re@l💍 K@usy🌹: Rumana 40

D'an murfin ya tara yasami kadan,Sannan yaimin tsarki bayan nagama gaba daya sai murmushi yake saki wai yaimin tsarki,Abun gwanin taushi.
Nidai kauda kaina kawai nayi ga barin kallonshi Sam haidar beji,Bantaba tunanin zansami kanshiba kamar haka.
Bantsaya jiranshiba nayo waje sonake indanyi barci ko kadanne kamin magriba Amma ya hana sai lagudeni yakeyi yana taramin gajiya.

Wani k'ayataccen murmushi ya saki lokacinda yaga layi biyu sunfito saidai da alama bejimaba dangashinan daya yai biji biji bakamar dayaba.

Rawa yafara takawacikin bayin yana tsalle saikace wani yaro lallai Ruma Alkhairice agareshi ta iya karbar sako yanda yakamata.

Bargo naja na rufe jikina ruf ina kallonshi, Girarshi ya dagamin yana murmushi " 'yanmata ya akaine kike kallona?

Rufe idonai ina murmushi wallahi wani lokacin sai inta tuno lokacinda beda lafiyar nan musamman idan sha'awarshi tatashi yai linkif dashi sai yanda nayi dashi.
Wata siririyar dariya nasaki ina lullube har kaina.

Da sauri ya hawo gadon yana dariya"muguwa gayamin me kikeyima dariya haka?

Sakarmin nauyinshi yayi yana dariya,Allah kiyi magana ko yanzu insaki kuka.

"Bafa wani abu bane tuno lokacinda baka da lafiya nayi,Idan sha awarka tatashi gwanin ban tausayi.

Murmushi yayi kamin yace Allah sarki!ni to gayamin ya kikemin?

Boyewa nai cikin kirjinshi ina murmushi, " Yo dibara nakeyi maka har insamu kadan sami nutsuwa,Shiyasa koda baka da lafiyarnan nasan indai ka warware bazakai saukiba.

Kayanshi ya tube kamin yace hakane wallahi danni banhada komai ba da biyan bukatata shiyasama naimaza na sakarmiki kwayayena inafatan Allah yasa Wanda kika dauka yafi daya nasan shikenan zaki bude hanya lallai dasu Abba sunyi alfahari damu kinga Abba beda kwan haihuwa da yawa to ni inafatan ace na jikina basu da iyaka kuma duk ke zaki haifesu taso kiyi aikin lada.

Lafewa nayi cikin jikinshi nidai a a gaskiya barci nakeji.

"To aiko cikin jikinki zanshiga yanzu danni wallahi atakure nake,Waima tsaya zona tambayeki,Anya kinfarajin dadin da akeji kuwa?

"Yauwa wallahi nima tambayar da nakeso naimaka kenan nifa bangane komai har yanzu garama idan kanadanmin wasannin nan inajin dadi amma dakafara abun sai inji zaka kasheni gashi sai inga kai duk ka rude da alama dadi kakeji ko?

Matseni yai jikinshi yana murmushi,Ai yarinya fadi baci akwai tarin jin dadi farinciki da samun nutsuwa aduk lokacinda mutun hai tarayya da iyalinshi,Shiyasa nakejinki daban Ruma kece farincikina, Sannan inasamin jin dadi Wanda yafi karfin na misaltashi aduk lokacinda nake kwance dake.

Cikin shagwaba nace to Amma meyasa ni bazakamin me dadin ba?

" Hahhhha kimma bani dariya to ai me dadin kenan, ke kincika tsorone sannan har yanzu baki sakin jikinki sosai kin Riga kinsama zuciyarki tsoron abun balle kiji dadin da akeji shiyasa nikuma naketa shagalina.
Ganin zankuma magana yasashi rufemin baki da nashi yayinda yakecigaba da shafar marata jiyake kamar ya saka ihu sabida farinciki wane kalar murna Abba zaiyi idan yaji wannan labarin balle umma.

**** ******

Cikin kwanaki biyu kacal da suka biyo baya nayi matukar farinciki dajin dadi iyayen mijina na matukar kula dani balle kuma oga duk da yana matsamin da bukatarshi amma yana kula dani sosai,Kuma bandainajin tashin zuciyaba lokaci zuwa lokaci nakanjishi musamman idan naci na koshi.

Irin kulawar da yake bani har mamaki nakeji wallahi ban zataba kullun ada ina tunanin kilama dayasami sauki zai sakeni saidai yabani mamaki sosai domin son da yake nunamin har gani nake yana nema yayi yawa.

Cikinmu babu Wanda yakumajin duriyar hajiya saude domin Abba yace kadda aneshi duk abinda yadace suyimata amma abangarenmu munyafe.
Shiyasa yanzu kacokan ya maida sa idonshi akan hajiya saratu sabida ita alokacinma ta kanta takeyi kullun sai zarya zuwa asbt kullun fatanta tasamu lafiya,Sannan jikinta duk yagama sanyi sabida ganin babu hajiya bilkisu babu hajiya saude sai ita kadai cikin wa inda suka kasance masu muguntar,Ga haidar yana rayuwarshi qalau haddama iyali, Lallai hassadarsu bata kasance komaiba agaresu sai k'arin budi.

****

Kwance yake nanike da matarshi hankalinshi kwance yake yanzu jiyake beda sauran mata sai fatiman hankalinshi kwance Dan hajiya saratu babu ruwanshi da ita tunda yai fama da ita taimishi bayanin lalurar dake damunta taki, Sannan yace suje asbt tare nan ma taki shiko ya rantse bazai kuma kusantartaba saiya tabbatar da ingancin lafiyarta,Dan yanzu tsoro suke bashi balle yasan duk abinda ake agidan itama dasa hannunta.

Kuma matseta yayi jikinshi yanajin kamar su dawwama ahaka tsabar dadin da yakeji.

"Waikai alhaji bazaka fitabane yau ga wayarka can mafa anata kira tun dazu kuma nasan kanaji.
Maidata yai cikin jikinshi yana murmushi, " Maman haidar kincika mita yanzu wallahi bansan meyasaba babu halin ince zan huta agida kindinga korafi kenan meyasa?

"To Alhaji ba dole inyi korafiba tunda nasan hutun naka akaina yake k'arewa, Wallahi shiyasa Rumana takebani tausayi yaro ya biyo hali irin na uba yabi ya hana yarinya sakat saima wata rama takeyi atsaye jiya har tambayarta nayi tacemin lafiyanta lau,Koson fita beyi aikinma nasan adaddafe yake yinshi.
Chapter 22 · 0% Book details