Sashe 12
Rumana Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
''Yauwa to maganar danake son ji kenan daga bakin ka, yanzu abinda ya kamata anan shine da farko dai za'a fara da almajirai yara ayi sauka ta alkur'ani sau d'aya, sannan za'a bawa mabuk'ata sadaka, Sai a fara bashi rubutu na sha da shafawa insha Allah wata rana sai labari. Sannan bayanin dakai min na auran da zaka yi mishi shima wannan naji dad'i kuma nayi farin ciki domin indai ita matar tashi ta fahimci lalurar tashi to lallai ko maganin zaifi tafiya yanda ya kamata ajikin shi, Amma ka daina maganar sha'awarshi eh gaskiya ne yana da yawan bukatar mace kuma koda bakin shi yasha gaya maka amman yanzu ma da lalaurar ta kamashi su aljanun basu tab'a mishi wannan b'angaren sha'awar tashi ba shi yasa take tashi lokaci zuwa lokaci amma dan Allah kadda kaba da kofar da zai kusanci yarinyar mutane alhalin baya cikin hayyacin shi dan lallai za'a iya samin matsala wacce bama fata.''
Kuma numfasawa alhaji Yusuf yayi jiyake jikin shi kamar anyi mshi duka sabida tashin hankali shi kam duk wanda ya yiwa Haidar haka bazai tab'a yafe mishi ba idan kuwa zai ganshi kila sai ya zama ajalin shi. Sallama yayi akan sai ya dawo sai a fara abinda ya dace ammafa har lokacin tunani yake anya kuwa gaske ne wani ne zai kauce hanya domin ya cutar da d'an uwansa musulmi?
Jiki a sanyaye ya koma gida ko b'angaren shi bai nufa ba sai dai ya fara nufar na Haidai d'in. Kwance yake yana bacci, shi kuma Mudi na saman kanshi yana ragemai sumar kanshi a hankali gudun kadda ya tashi yayi ta borin daya saba.
Zama yayi ragwaf tare da d'agawa Mudi hannu wanda yake gaidashi, Lumshe idanunshi yayi yana tunani wanda yanzu ya zame mishi jiki.
Yana zaune yana kallon Mudi har k'umba sai da ya rage mishi sannan ya gyara mishi sajen shi nan da nan fuskarshi tai wani fayau kai baka ce yana da wata lalurar ba.
"Mudi aure zan yiwa Haidar.'' Cewar alhaji Yusuf yana kallon yanayin Mudin, cikin washe baki yace.
''Kai alhamdulillah alhaji hakan yayi kyau wallahi Allah ya bashi ta gari wacce zata kula dashi tsakaninta da Allah.''
Bayan sati shida.Zuwa wannan lokacin gidanmu ya kacame da hidima sabida karatowar biki. Zaune nake inna tana ta lailayemin jikina da lalle dagani sai wata bak'ar bes a jikina, inna da kanta ta siyota a kasuwa sabida wannan aikin da take mim. Kirjina na kalla wanda yayi wani cirko-cirko kasancewa babu bra a jikina, har kirjin nawama be tsira ba tunda bani takeyi tace na shafa idan tagama.
Fatata ta canza sosai wani uban laushi da santsi takeyi sannan ga kamshi domin akwai wata madarar turare da ake zubawa cikin kwabin lallan yanzu wajan wata daya kenan dafara yi min wannan gyaran ammafa na canza nayi kyau ta yadda daka ganni zaka san cewar ni din amarya ce.
"Dan Allah duk gyaran nan da nake miki ki daure idan anyi auran nan kiciga ba da yi domin wallahi ba k'aramin temakawa jiki yake yiba, kune dai yaran zamani da sai kuce ku dole sai kayan shafe-shafe shi yasa da an kwana biyu sai jiki ya jeme ya lalace.'' Ban kalleta ba nace.
''Toh inna.''
Shigowar dije da wasu k'awayenmu yasa inna barin d'akin mukuma mukaci gaba da shirya yanda za'a yi duk da dai ni ina zaune iya kaci na dasu kallo.
Usman shine wanda yayi ruwa yayi tsaki wajan ganin komai ya tafi dai-dai an shirya walima kadai kamar yadda mahaifin ango ya tsara sannan aka bani wadatattun kud'i koda zan buk'ata lefena kwananshi hudu da kawowa babu abinda babu akwatina shida masu shegen kyau da tsada sannan ga uwa uba kayan da aka zuba a ciki.
K'awayena sunata tayani murna tare da nanata suma Allah ya mai dasu kamar ni, Ni kam jinsu kawai nake yi domin ina cikin wani yanayi wanda ni kaina bazan ce ga kalarshi ba......
*MAMAN KHADY.*🙇🏻♀
[4/2, 11:15 AM] Re@l💍 K@usy🌹: Rumana 16
Zaune nake ina tilawar alkur'ani me girma shikuma yana gefena yai zugudun saikace mai tunanin wani abu.
Inuwa kawai nagani saman kaina,Kusan atsorace na dako kaina aiko wata mace nagani tsaye saman kaina tana taunar cingam tare da wani girgije girgije saikace karuwa agefen titi.
"Wani miyau na hadiye kamin ince sannu da zuwa ki zauna mana.
Wani kallon banza taimin kamin tace" Ke dallah dakata kekuma awa da zakice in zauna ko kina tunanin wani matsayi gareki?
Da mamaki nake kallonta,Kamin ince ikon Allah to Dan Allah kadda ki zauna kiyita tsayuwa.
Sabida raina tuni yafara baci dama wani lokacin fadane dani balle wannan ko sallama bataiminba kuma Dan iskanci naimata tayin wajan zama zata nunamin itama wata shegiyace.
Hannun haidar nakama na kaishi daki sannan nai zamana acan Dan banga amfanin dawowata falon ba.
Bansan ya akaiba saidai naji banbamin masifa natashi acikin falon,Mamaki da tsoro ya hanani ko motsin kirki Saida naji ana kwalamin kira da cewa ke matar mahaukaci kina ina fito.
Hijab dina na d'auka nasa sannan nafita.
Uwargidan Abba ce tsaye da wannan me zubin 'yan duniyar.
Duk'awa nai tare da cewa hajiya ina yini?
Wata shegiyar harara ta sakarmin kamin tace"Dallah can matsa bani guri algunguma kawai ubanme k'anwata taimiki kika zageta?
Idona waje na furta zagi kuma?Wallahi hajiya ban zagetaba itacema tashigo ko sallama bataima tana gayamin maganganu shine sai nikuma natashi nabata wuri dama ko zama bataiba.
"Mitsw aikin banza to Dallah dama ancemiki zama tazo to bari kiji wannan itace nafeesa wadda haidar zai aura kamin yazama mahaukaci kuma koyau ya warke itace matarshi nasan kedai kozai mutu bazai zauna dakeba domin yafi karfinki garama ki kama kanki ankawokine domin ki wahalamishi kamin yaji sauki ya sallameki wawuya kawai,Kenan har wata mace ce?
Hawaye share share idanuna nakebata hakuri yayinda zuciyata nakejin kamar zatayo waje tsabar tafarfasar da takeyi.
Saida tagama masifarta ta zagemin iyaye tas tare da kirana da kwadayayya sannan sukabar falon.
Kuka nacigaba dayi sosai hadda sheshsheka saiga Harun ya shigo.
" Subhanillahi Amarya meya faru?
Muryata ashake nace wallahi wannan hajiyarce tazo da kanwarta wai wacce zata auri ya haidar shine suka zagemin iyaye wa inda basusan me akeyiba.
"Kanshi ya dafe kamin yace ammadai kinban haushi wallahi shine kika tsaya kina kuka bakici uban shegu ba?Toma tsaya idan ita hajiyar kin ragamata shikenan sai itama wannan Mara kunyar ki kyaleta?
To bari kiji wallahi kinji na rantse matukar kuka zaki dinga musu to ki tabbata kwanan nan hawan jini zaikamaki domin ta dinga shigomiki kenan tunda dama takanzo idan sunyi hutun makaranta kuma tana dadewa danhaka ki kankaroma kanki mutunci tunkamin dare yaimiki.
Ina mutumin nawa? Yaya kike ganin jikin nashi?
" Alhamdulillahi da sauki sosai gaskiya domin komai yafara sauki.
"To Alhamdulillahi ai haka akeso yanzu abinda yai saura shine kiyi k'okarin ganin umma ta dawo k'asar nan kema hankalinki nasan saiyafi kwanciya.
Haidar ne ya fito da cup ahannu da kallo duk mukabishi Sabida ganin abinda zaiyi.
Yana zuwa saitina ya wurgomin shi da sauri na cabe ina ihun tsoro dannariga na sadakar saiya rushemin kai.
Da sauri na mike naje na hadomishi tea saida ya koshi sannan ya kwanta jikina yacigaba da sauke numfashi.
Haidar yace" Lallai kina kokari amarya lallai jiki yafara kyau kenan yanzu yafara sanin yunwar cikinshi kenan ko?
Dan murmurshi nayi kamin nace eh hakane kam anasamin cigaba sosai.
Da farinciki ya furta Allah yak'ara afuwa ammafa yakamata ki dinga lura kina kiyayewa kadda yadinga raunataki kwanakima Abba yacemin har yankarki yayi da wuka ko?
"Eh wallahi nashiga zanyi girki Ashe yabini saidai kawai naji sukar wuka ahannuna Ashe harya dauki wukar bansaniba.
" To Allah ya kiyaye gaba Sabida zai iyacigaba da faruwa tunda bawai tunanin daidaine akanshiba yanzu duk abinda yaga dama zakiga shizai aikata,Bari intashi in wuce insha Allah danadawo tafiyarnan zanfara nemamiki gurbin karatu tunda naji haka Abban yakeso ammadai ni nafiso umma ta dawo tukunna Sabida abubuwan suyimiki sauki.
Godiya naimishi sannan yaimana sallama yatafi.
Gaskiya Harun yanada kirki sosai shine ke kula dani matukar Abba benan kuma betaba nuna alamun gajiyawaba nikuma saina daukeshi amatsayin yayana kawai tunda bani da kowa ahalin yanzu.
Aunty nifa gaskiya hankalina atashe yake kinsan dai inason haidar sosai amma kalli yanda kikabari aka tsauna dukiya wajancan kuma ji matarshi ainasan ko warkewa yayi bazai kalleniba tunda ga wadda ta kula dashi shiyasa nacemiki na amince aimana auren zan zauna yanda yake kikace a a.
"Mitsw lallai sai yanzu nasan baki da hankali uban waye yacemiki zai warke?Ke yanzu da ajinki da komai amma saiki yadda ki zauna da mahaukaci? To bari kiji haidar ba warkewa zaiyiba wannan ciwon nashi mutu ka rabane itama matar tashi 'yar gidan matsiyatane shiyasa sukabada auranta garesu kuma inbanda aikin bauta metakeyi agidan ko kina tunanin akwai wani Abu bayan wannan?
Itadai nafeesa ba haka tasoba shiyasama ta tunzuro bakinta gaba domin ita tanason haidar sannan akwaita da bakin kwadayin tsiya domin inda an biyemata ma da ahakan ta aureshi,Musamman yau data shiga taga irin dukiyar da alhajin yabata ma wajan.
Misalin bakwai na magriba na lalubi wayata muryar umma kawai nakeson ji kwana biyu bata kiraniba bansan meyasaba haka kawai naji matar taimin ina tsananin sonta duk da bantaba ganintaba.
Yanke kiran tayi sannan ta kirani.
" Ummu Rumana ya kuke?
"Lafiya lau umma munyi kewarki Dan Allah ki dawo wallahi ina cikin kadaici da kewa.
Murmushin farinciki tayi kamin tace Rumana kenan karki damu zandawo insha Allah.
Cikin shagwaba wacce bansan lokacinda nafarataba nace haba umma Dan Allah kullun fa haka kike cewa amma har yanzu kinki dawowa ko incema Abba ya kawomu?
Dariya tayi me sauti kamin tace lallai ma kuruciya na damunki kema basaikunzo zanzo insha Allah.
Bansoba amma haka mukai sallama bayan takuma bani shawarwari tare da yimin fatan Alkhairi.
Kuma numfasawa alhaji Yusuf yayi jiyake jikin shi kamar anyi mshi duka sabida tashin hankali shi kam duk wanda ya yiwa Haidar haka bazai tab'a yafe mishi ba idan kuwa zai ganshi kila sai ya zama ajalin shi. Sallama yayi akan sai ya dawo sai a fara abinda ya dace ammafa har lokacin tunani yake anya kuwa gaske ne wani ne zai kauce hanya domin ya cutar da d'an uwansa musulmi?
Jiki a sanyaye ya koma gida ko b'angaren shi bai nufa ba sai dai ya fara nufar na Haidai d'in. Kwance yake yana bacci, shi kuma Mudi na saman kanshi yana ragemai sumar kanshi a hankali gudun kadda ya tashi yayi ta borin daya saba.
Zama yayi ragwaf tare da d'agawa Mudi hannu wanda yake gaidashi, Lumshe idanunshi yayi yana tunani wanda yanzu ya zame mishi jiki.
Yana zaune yana kallon Mudi har k'umba sai da ya rage mishi sannan ya gyara mishi sajen shi nan da nan fuskarshi tai wani fayau kai baka ce yana da wata lalurar ba.
"Mudi aure zan yiwa Haidar.'' Cewar alhaji Yusuf yana kallon yanayin Mudin, cikin washe baki yace.
''Kai alhamdulillah alhaji hakan yayi kyau wallahi Allah ya bashi ta gari wacce zata kula dashi tsakaninta da Allah.''
Bayan sati shida.Zuwa wannan lokacin gidanmu ya kacame da hidima sabida karatowar biki. Zaune nake inna tana ta lailayemin jikina da lalle dagani sai wata bak'ar bes a jikina, inna da kanta ta siyota a kasuwa sabida wannan aikin da take mim. Kirjina na kalla wanda yayi wani cirko-cirko kasancewa babu bra a jikina, har kirjin nawama be tsira ba tunda bani takeyi tace na shafa idan tagama.
Fatata ta canza sosai wani uban laushi da santsi takeyi sannan ga kamshi domin akwai wata madarar turare da ake zubawa cikin kwabin lallan yanzu wajan wata daya kenan dafara yi min wannan gyaran ammafa na canza nayi kyau ta yadda daka ganni zaka san cewar ni din amarya ce.
"Dan Allah duk gyaran nan da nake miki ki daure idan anyi auran nan kiciga ba da yi domin wallahi ba k'aramin temakawa jiki yake yiba, kune dai yaran zamani da sai kuce ku dole sai kayan shafe-shafe shi yasa da an kwana biyu sai jiki ya jeme ya lalace.'' Ban kalleta ba nace.
''Toh inna.''
Shigowar dije da wasu k'awayenmu yasa inna barin d'akin mukuma mukaci gaba da shirya yanda za'a yi duk da dai ni ina zaune iya kaci na dasu kallo.
Usman shine wanda yayi ruwa yayi tsaki wajan ganin komai ya tafi dai-dai an shirya walima kadai kamar yadda mahaifin ango ya tsara sannan aka bani wadatattun kud'i koda zan buk'ata lefena kwananshi hudu da kawowa babu abinda babu akwatina shida masu shegen kyau da tsada sannan ga uwa uba kayan da aka zuba a ciki.
K'awayena sunata tayani murna tare da nanata suma Allah ya mai dasu kamar ni, Ni kam jinsu kawai nake yi domin ina cikin wani yanayi wanda ni kaina bazan ce ga kalarshi ba......
*MAMAN KHADY.*🙇🏻♀
[4/2, 11:15 AM] Re@l💍 K@usy🌹: Rumana 16
Zaune nake ina tilawar alkur'ani me girma shikuma yana gefena yai zugudun saikace mai tunanin wani abu.
Inuwa kawai nagani saman kaina,Kusan atsorace na dako kaina aiko wata mace nagani tsaye saman kaina tana taunar cingam tare da wani girgije girgije saikace karuwa agefen titi.
"Wani miyau na hadiye kamin ince sannu da zuwa ki zauna mana.
Wani kallon banza taimin kamin tace" Ke dallah dakata kekuma awa da zakice in zauna ko kina tunanin wani matsayi gareki?
Da mamaki nake kallonta,Kamin ince ikon Allah to Dan Allah kadda ki zauna kiyita tsayuwa.
Sabida raina tuni yafara baci dama wani lokacin fadane dani balle wannan ko sallama bataiminba kuma Dan iskanci naimata tayin wajan zama zata nunamin itama wata shegiyace.
Hannun haidar nakama na kaishi daki sannan nai zamana acan Dan banga amfanin dawowata falon ba.
Bansan ya akaiba saidai naji banbamin masifa natashi acikin falon,Mamaki da tsoro ya hanani ko motsin kirki Saida naji ana kwalamin kira da cewa ke matar mahaukaci kina ina fito.
Hijab dina na d'auka nasa sannan nafita.
Uwargidan Abba ce tsaye da wannan me zubin 'yan duniyar.
Duk'awa nai tare da cewa hajiya ina yini?
Wata shegiyar harara ta sakarmin kamin tace"Dallah can matsa bani guri algunguma kawai ubanme k'anwata taimiki kika zageta?
Idona waje na furta zagi kuma?Wallahi hajiya ban zagetaba itacema tashigo ko sallama bataima tana gayamin maganganu shine sai nikuma natashi nabata wuri dama ko zama bataiba.
"Mitsw aikin banza to Dallah dama ancemiki zama tazo to bari kiji wannan itace nafeesa wadda haidar zai aura kamin yazama mahaukaci kuma koyau ya warke itace matarshi nasan kedai kozai mutu bazai zauna dakeba domin yafi karfinki garama ki kama kanki ankawokine domin ki wahalamishi kamin yaji sauki ya sallameki wawuya kawai,Kenan har wata mace ce?
Hawaye share share idanuna nakebata hakuri yayinda zuciyata nakejin kamar zatayo waje tsabar tafarfasar da takeyi.
Saida tagama masifarta ta zagemin iyaye tas tare da kirana da kwadayayya sannan sukabar falon.
Kuka nacigaba dayi sosai hadda sheshsheka saiga Harun ya shigo.
" Subhanillahi Amarya meya faru?
Muryata ashake nace wallahi wannan hajiyarce tazo da kanwarta wai wacce zata auri ya haidar shine suka zagemin iyaye wa inda basusan me akeyiba.
"Kanshi ya dafe kamin yace ammadai kinban haushi wallahi shine kika tsaya kina kuka bakici uban shegu ba?Toma tsaya idan ita hajiyar kin ragamata shikenan sai itama wannan Mara kunyar ki kyaleta?
To bari kiji wallahi kinji na rantse matukar kuka zaki dinga musu to ki tabbata kwanan nan hawan jini zaikamaki domin ta dinga shigomiki kenan tunda dama takanzo idan sunyi hutun makaranta kuma tana dadewa danhaka ki kankaroma kanki mutunci tunkamin dare yaimiki.
Ina mutumin nawa? Yaya kike ganin jikin nashi?
" Alhamdulillahi da sauki sosai gaskiya domin komai yafara sauki.
"To Alhamdulillahi ai haka akeso yanzu abinda yai saura shine kiyi k'okarin ganin umma ta dawo k'asar nan kema hankalinki nasan saiyafi kwanciya.
Haidar ne ya fito da cup ahannu da kallo duk mukabishi Sabida ganin abinda zaiyi.
Yana zuwa saitina ya wurgomin shi da sauri na cabe ina ihun tsoro dannariga na sadakar saiya rushemin kai.
Da sauri na mike naje na hadomishi tea saida ya koshi sannan ya kwanta jikina yacigaba da sauke numfashi.
Haidar yace" Lallai kina kokari amarya lallai jiki yafara kyau kenan yanzu yafara sanin yunwar cikinshi kenan ko?
Dan murmurshi nayi kamin nace eh hakane kam anasamin cigaba sosai.
Da farinciki ya furta Allah yak'ara afuwa ammafa yakamata ki dinga lura kina kiyayewa kadda yadinga raunataki kwanakima Abba yacemin har yankarki yayi da wuka ko?
"Eh wallahi nashiga zanyi girki Ashe yabini saidai kawai naji sukar wuka ahannuna Ashe harya dauki wukar bansaniba.
" To Allah ya kiyaye gaba Sabida zai iyacigaba da faruwa tunda bawai tunanin daidaine akanshiba yanzu duk abinda yaga dama zakiga shizai aikata,Bari intashi in wuce insha Allah danadawo tafiyarnan zanfara nemamiki gurbin karatu tunda naji haka Abban yakeso ammadai ni nafiso umma ta dawo tukunna Sabida abubuwan suyimiki sauki.
Godiya naimishi sannan yaimana sallama yatafi.
Gaskiya Harun yanada kirki sosai shine ke kula dani matukar Abba benan kuma betaba nuna alamun gajiyawaba nikuma saina daukeshi amatsayin yayana kawai tunda bani da kowa ahalin yanzu.
Aunty nifa gaskiya hankalina atashe yake kinsan dai inason haidar sosai amma kalli yanda kikabari aka tsauna dukiya wajancan kuma ji matarshi ainasan ko warkewa yayi bazai kalleniba tunda ga wadda ta kula dashi shiyasa nacemiki na amince aimana auren zan zauna yanda yake kikace a a.
"Mitsw lallai sai yanzu nasan baki da hankali uban waye yacemiki zai warke?Ke yanzu da ajinki da komai amma saiki yadda ki zauna da mahaukaci? To bari kiji haidar ba warkewa zaiyiba wannan ciwon nashi mutu ka rabane itama matar tashi 'yar gidan matsiyatane shiyasa sukabada auranta garesu kuma inbanda aikin bauta metakeyi agidan ko kina tunanin akwai wani Abu bayan wannan?
Itadai nafeesa ba haka tasoba shiyasama ta tunzuro bakinta gaba domin ita tanason haidar sannan akwaita da bakin kwadayin tsiya domin inda an biyemata ma da ahakan ta aureshi,Musamman yau data shiga taga irin dukiyar da alhajin yabata ma wajan.
Misalin bakwai na magriba na lalubi wayata muryar umma kawai nakeson ji kwana biyu bata kiraniba bansan meyasaba haka kawai naji matar taimin ina tsananin sonta duk da bantaba ganintaba.
Yanke kiran tayi sannan ta kirani.
" Ummu Rumana ya kuke?
"Lafiya lau umma munyi kewarki Dan Allah ki dawo wallahi ina cikin kadaici da kewa.
Murmushin farinciki tayi kamin tace Rumana kenan karki damu zandawo insha Allah.
Cikin shagwaba wacce bansan lokacinda nafarataba nace haba umma Dan Allah kullun fa haka kike cewa amma har yanzu kinki dawowa ko incema Abba ya kawomu?
Dariya tayi me sauti kamin tace lallai ma kuruciya na damunki kema basaikunzo zanzo insha Allah.
Bansoba amma haka mukai sallama bayan takuma bani shawarwari tare da yimin fatan Alkhairi.