← Book details Rumana Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 14 OF 34

Sashe 14

Rumana Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Dama tun shigowarta idona biyu danhaka saiwata irin kunya takamani kamar in nitse,Wani kuka nasaki na kunya domin bansan yanda zankuma kallontaba.
Cikin magagin barci yakuma rarumoni yana fadin sorry please waike baki gajiya da kukane? Kokarin komawa barcinshi yakeyi kwatsam saiyaji muryar umma na fadin " Haidar!!
Murje idanunshi yayi kamin yace na'am ummana.
Wata irin runguma taimishi kamin tafara zubar da hawayen dadi lallai Allah shine abun godiya.

Sakinshi tai tare da riko hannuwana tanafadin taso Ruma meyaimiki?
Shiru nai ina hawaye Sabida kunya.
Kallonshi tayi danhaka saiya kauda kai yana murmushi umma banyimata komaiba Allah kuwa.

Wata uwar harara na wurgamishi kamin ince wallahi umma karya yakeyi yaimin wani abu.

"Haidar meyasa?Cewar umma tana kallonshi.

Cikin shagwaba yace umma Allah banyiba nadaiso inyi amma banyiba,kallonshi ya maida kaina kamin yace zankamaki ahannuna indai nine me karyar Amma ni banyimata komaiba toma ina zanyi dawani abunta saikace na jarirai🙄.
Wata irin dariyace ta kama umman amma bataiba Sabida bataso inga kamar dani take,Saidai zuciyarta cike take da farinciki lallai haidar dinta yadawo,Kuma tunda yace beyiba to beyiba din domin azahiri dama haka yake Sam beda kawaici ko boyo akan abu komenene kuwa.

" Lallai haidar da abinda zaka sakamata kenan ko? Kyaleshi tashi muje in hadamiki ruwan wanka saiki gasa jikinki kaikuma zaka sani ne,Kamayi wankan kuwa?
Idanunshi na kaina yace banyiba jiranake taimin.

Dagani har ita idanu muka zubamishi Dan mamaki.

Harararshi nayi kamin ince Allah ya kyauta inkuma maka wanka kuma mugu kawai.

Wucewa umma tayi domin hadamin ruwan yayinda shikuma ya matso kusa dani dallah ke zakimin kima godema Allah dayabaki baiwar ganin sirrina yarinya kuma kadda kikuma cemin mugu tunda babu abinda naimiki waima tsaya ke wannan abun naki me kama dana jarirai sabuwar haihuwa kina tunanin ko dadi zaiyi ne?

Bakin ciki yasani sakamishi kuka da karfina Wanda har saida Abba dake zaune afalo yataho da sauri tunaninshi ko babu lafiya balle dama dayaji umman shiru.

Da kanta ta nunamin yanda zanyi sannan tafito tana kallon Abba Wanda yasawo kai cikin dakin yana tambayar lafiya?

Da hannunta ta nunamishi haidar Wanda yaketa murmushi kamar anbawa yaro hakorin maka.
Da sauri yatashi ya nufi Abban ya rungumeshi Sam bedamu da gajeran wandon dake jikinshiba.
Wani irin farincikine ya lullube Abba Wanda yasashi fitar da hawaye kamar yadda itama umman taketa sharenata akai akai.
Sunkasa magana saidai zukatansu cike suke da godiya ga Allah.

Sakinshi Abban yayi kamin yace ka gyara jikinka tukanna saiku taddamu falonku ina matar taka?
Ummace ta bada amsa da cewa lafiyarta lau tashiga wanka.

Ganin sunfita yasashi komawa daidai kofar bayin ya babyna in leko?

Inadaga ciki mamaki da tsoro ya kamani kai anya kuwa haidar ya warke gabadaya? Tsaki nai araina kamin ince aidama ance duk Wanda yai hauka becika warkewa dukaba,Da sauri na dauraye jikina na fito ko kallon inda yake banyiba Sabida wata irin kunyarshi danakeji.

Da Murmushi ya wuce toilet din yanafadin lallai yarinya kwanannan zan budaki insha Allah.

Inajinshi nai banza dashi domin daga jiya zuwa yau na fahimci Sam beda kunya,Amma har lokacin ban yarda da cewa be kusanceniba Sabida yanda naji sauyi awajan.

Fes na fita falo lokacin har umma ta kawomana abin breakfast da kanta kuma suna zaune da Abba hira suke amma duk wacce ta shafi haidar ce.
Zama nai tare da gaishesu,Sai shimin albarka suke cike da farinciki.

Tunkamin ya karaso falon kamshinya ya cike ko ina cikin wata tafiyar kasaita ya karaso harwani budawa yakeyi fuskarnan fes da ita kai tatsaye ya rungumi umma tare da sakarmata Sumba agoshi sannan Abba,Niko muna hada ido saiya dagamin gira.
Uhumm aidama daga ganin idanun haidar nasan bazaiyi jin maganaba wlh, Abinda nafada cikin zuciyata kenan.

"Ke raguwa zoki hadamin break yunwa nakeji.

Turobakina gaba nayi ina hararar gefenshi,Ummace tace kai bansan shirme raguntar metaimaka nifa bansan tsokanar fada haidar.

Koda muka gama karyawa hira mukadasa cike da farinciki.

Babu Wanda yasan da samun warakar haidar sai iyamu kadai.

Yini nai kwance amma babu abinda kemin ciwo ammadai kasala ta dameni.
Bunu bunu umma taimin sannu shiko mugun saidai ya dagamin gira kan dole nadaina kallonshi.

Sai bayan sallar isha'i sukaimana sallama zasu wuce,Aiko nantake na buga tsalle tare da cewa umma zanbi.
Kallon kallo akai tsakanin Abba da umma kamin umma tace gaba Ruma kiyihakuri ki zamanki nan ai muna tare ko?
Bakina na turo nafara sharar hawaye to harna fara tunanin irin murzar da zaimin yau tunda shi mugune.

Dariya haidar din yayi sosai kamin yace to meye dankibi umma?zaki fara kuka saikace cinyeki zanyi tunda bakiji tsoron zama daniba sai yanzu sabida gulma ko?
Harararshi nayi ammadai bance komaiba,Abba ko ficewa yayi yana dariya.

" kiyi hakuri gobe saiki kwana wajena din ko?

A a barta kuje umma abun natama da ko dadi babu,Cewar haidar yana dariya.

Kuka nasaka me sauti inajin kamar in fallamishi mari.

Umma ma ficewa tai tana dariyar iskancin haidar,Amma taji dadin dabe nuna beson zama daniba dayaji sauki.

Saida yaga umma tafita harma tajamana kofar sannan ya mike tare dayin wata doguwar mika ya nufoni yana murmushi kai yau zan fafe sabuwar kaza.
[4/2, 11:15 AM] Re@l💍 K@usy🌹: RUMANA 17

Ganin tsayuwar taimusu yawa yasa tasaki kofar tare da juyawa ta shige.
Cike da wani irin farinciki da shauki yabi bayanta domin Fatima macece duk kwakwar mutun bazaice itace ta haifi haidar ba kodan dama da kuruciyarta ya aureta kai a a yanayin jikine kawai da Allah yaimata baiwa dashi musamman yanzu da Hutu ya zauna Jikinta.

Cikin sanyin jiki ya zauna kujerar dake kallon tata idanunshi kamar zasu sakko tsabar yanda yai kewarta.
Cikin daburcewa yace"Sannu Fatima nasameki lafiya?

Tad'anji kunya ganin babba dashi yana gaidata.
Wata yarinyace da bazata wuce shekaru 17 ba ta kawomishi ruwa da lemo akan faranti tare da gaidashi da harshen turanci,Kasancewar itama ba India ce.
Juyawa tai ta fice akunyace ganin yanda aketa jifan juna da kallon love.

Duk wani girma da yake takamar yanadashi saukeshi yayi ya aje gefe domin yana bukatar matarshi kuma yasan halinta tsaf zata iya kuma baudewa Sabida Fatima akwai tsananin hakuri da kauda kai,Amma tanada tsananin riko da fushi matukar ankaita karshe.

Duk'awa yayi gabanta cikin raunin murya tare da marairaicewa yace"Fatima ki dubi girman Allah kiyi hakuri da abinda ya wuce ke kanki kinsan cewa ba halina bane wulakanci balle akanki ina sonki ina kaunarki soyayyar da koni bazan iya misaltataba kuskure aka samu sannan kaddaratace tazo da hakan Dan Allah kiyi hakuri.

"Kauda kanta gefetai kamin tace lallaima abban haidar kana tunanin zan iya cigaba da zama dakai bayan ka dauki son duniya ka dorama matanka?Harfa marina kayi batare da nasan laifin da naimakaba sannan ka rabani da yarona Wanda ke cikin hali na ciwo kaimin korar kare nikuwa me zaikuma hadani dakai?
Zandaici gaba da zama da igiyar auranka har zuwa lokacinda zaka gaji ka sawwakemin.

" Ki rufamin asiri Fatima naji kuma na karbi laifina amma Dan Allah kiyi hakuri na tuba bazan kuma aikata kuskure irin wannan ba wallahi wannan dinma bansan nayiba kimin alfarma kikuma bani dama Fatima yaronmu na bukatar kulawarmu.

Harararshi tayi kamin ta kauda kai batare datace komaiba.

Tashi yai ya koma kusa da ita tare da d'auko wayarshi ya mikamata kalli yaronki kigani wallahi yana bukatarki.

Saida tagama jamishi aji sannan tafara kallon hotunan haidar wasu yana cikin ciwon wasu yana barci wasu uban namishi shafa wasukuma zaune kawai yake aka daukeshi hoton.
Wasu irin hawayene sukafara zarya kumatunta tuni zuciyarta tajima da karyewa oh wai haidar dintane ya koma haka sai yanda akai dashi?Allah ka yayema yarona wannan lalura.

Atsorace ya rungumota jikinshi yana lallashi,Dadi yakamashi ganin takuma rikeshi tana kuka Alhamdulillahi yaita nanatawa cikin zuciyarshi yasan insha Allah ta hakura da wannan fishin.

Kasancewar akwai soyayya me karfi tsakaninsu yasa nan da nan yasami galaba akanta daga lallashi saiya zarce da lallasa itama tai kewarshi danhaka da kanshi ya lalubi inda bedroom dinta yake suka shige,Mamaki har kamata yayi ganin yanda ya rudemata saikace Wanda beda wasu iyalin.
Uhun uhum wata irin zazzafar soyayya suke gudanarwa kaikace sabbin aurene.To saimuce Abba barka da arziki.

******************

Nagama shirin barcina bayan na idasa ma haidar rushine agabana ina zuba hayakin da zanyi mishi,Kokarin mikewa yake inaga guduwa zaiyi na rikeshi ina dariya haba yayana yi hakuri yashiga jikinka kaji ko bakaso ka warkene kayi rayuwarka kamarta sauran mutane?

Bazai tsaya ta dadiba danhaka saina kyaleshi kadda yajema ya kifar da ita mu soye.
Jin ana kwankwasamin kofa yasani mamaki amma saina saka hijab dina na isa bakin kofar,Waye?

"Oho miki idan zaki budemin kofa ki bude.

Nan da nan na dauki murya nafisa ce, Wani murmurshi nayi me sauti kamin ince to bazan budeba saiki koma domin yanzu lokacin kwanciyarmune kema saiki kama gabanki.

Tafiyata nai nabar bakin kofar,Yayinda nabarta nan tsaye rike da haba ita mamaki take anya ma nice nai maganar musamman idan ta tuna yanda naita kuka jiya inaba hajiya hakuri.

Saida na kwanta nagama addua sannan nafada duniyar tunani kenan da gaske Ya Harun yake dayace indai zandinga mata kuka nabani domin da alama kwanaki zatayi gidan lallai zan dinga rufe kofata inko tsautsayi ya gitta tashigo zan kartamata rashin mutunci matukar batazomin dashi ba.

Saidai maganar da suka gayamin tun jiya har yanzu takasa barin zuciyata idan ya haidar ya warke ya koreni ya zanyi nikuwa sannan koda yake cikin lalurarnan Allah yasani inasonshi ahakan addua nafara Allah yasa ya hakura ya zauna dani koda zai auro mata uku ne daga baya.

Tunaninane ya yanzu lokacinda naji yana lalubata,Nifa lamarinshi yafara dauremin kai gaskiya wani lokacin sai inga kamar yasami lafiya musamman da yanzu ciwon yadaina bugunshi kwata kwata.

Cikin shagwaba wadda tafara zamemin jiki yanzu nace Dan Allah ka barni wallahi kirjina duk ciwo yakeyi yanzu kai baka iya tabawa da hankali.
Chapter 14 · 0% Book details