Sashe 11
Rumana Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ina son Fatima sosai domin tana da matukar tarbiyya a zaman da muka yi bazan ce ga ranar da ta sab'a min ba, saima nine wani lokacin idan aka kawo zugarta tai kaza zanyi mata fad'a koda batai laifin ba. Kwatsam sai Fatima ta fara laulayi bayan watanni takwas da auren mu. Babu wanda ya kawo mata cewa ciki ne domin ni a lokacin na riga na saddak'ar da cewa lallai bana haihuwa. Tsabar sa ido na hajiya Saude yasa ta fahimci akwai matsala domin ni dai ban sani ba wata rana ina kwance cikin d'akina sai gata ta shigo, zama tayi kusa dani tace.
''Alhaji wai kakai matar ka asibiti kuwa?'' Ba tare da na bata wata kulawa ba nace.
''Ban kai taba amma tace min ita taje.''
"To katashi kaje ka bincika idan ba haka ba kakusa d'aukar shege a hannunka tunda kowa yasan baka haihuwa ita kuma ai laulayi take yi.''
Ban san lokacin da nakai d'akin Fatima ba a lokacin, aikuwa saina tarar da ita tana ta amai duk ta galabaita, ban yadda cewa Fatima zata iya cin amanata ba domin koda na aureta budurwa na sameta sannan suna da duki ya dai-dai bakin gwargwado bare nace kwadayi zaisa tayi min haka. Da kaina na taya ta tagyra jikinta sannan nace muje asibiti. Likita ne ya tabbatar min da cewa ciki ne da ita na wata uku.
A wannan lokacin rasa abinda zanyi nayi shin farin ciki zanyi ko kuwa bakin ciki. Yayinda ita Fatiman naji ta saka ihu harda birgima ita wallahi ba ta son cikin ya za'ai ace duk cikin matana babu wacce naiwa ciki sai ita, ita wallahi sai dai azubar dashi. Na shiga tashin hankalin jin kalamanta wanda yasani fallamata mari sai dai kuma tana kukan najawota jikina na rungume sabida tunanin da gaskiyarta fa kuma dole ta shiga damuwa.
Bayani naima likitan tun daga farko har karshe yayi min tambayoyi sannan yace zai min awo. Gado aka bata domin ta huta nikuma a lokacin naga likita, sai dai iyakar binciken su sun gaya min cewa iyakar kwan haihuwata guda d'aya ne kacal kuma na fitar dashi akan Fatima.
Kusan ban yadda da maganar su ba saina shirya mana tafiya nida Fatima a wannan lokacin zuwa India, nanma maganar d'aya ce domin har cikin Fatima sai da suka bincika min cewar lallai cikin nawa ne kumama namiji ne jinana ne. Saudiyya muka wuce nan ma saida suka gama binciken su amma duk maganar d'aya ce dan haka anan na zauna nayi addu'a-nayi addu'a tare da nuna godiya ta ga Allah. A lokacin jinake babu abinda nake kauna sama da Fatima da abinda ke cikinta.
Matana sune suka fara sheganta min yaro sabida suna ganin aisu basu haihu ba sun manta cewa Allah shine mai tsara komai kuma a sanda yaso. Sai da mukai masifa dasu harma nayiwa Bilkisu saki d'aya sannan suka saduda suka bari alokacin ne nayi musu bayanin duk abinda ke faruwa tare da musu bayanan da likita yayi min a lokacinma harna basu zabi cewa duk wacce ke bukatar haihuwa to tayi min magana na sallameta sabida kadda na shiga hakkin su. Amma sai suka nuna zasu ci gaba da zama dani.
A lokacin da aka haifi Haidar kowa sai ya kara tabbatarwa da cewa lallai yaron jinina ne domin beyi kama da maman shi ba dani yayi kama kamar nayi kaki sai dai ya dauko farar fatar mamarshi domin tafini fari nesa ba kusa ba. Nasami haihuwa Ruma a lokacin da na fidda rai da samu shi yasa nayi shagali iyakar shagali sannan na saki kudi sosai aka yi taron suna.
To nidai bazance ga abinda ya dinga faruwa ba a tasowar Haidar sai dai dole tasa na kai Fatima wani gidana sabida a lokacin tace in dai ban raba musu gida ba to wallahi gidan su zata tafi, gashi nayi-nayi ta gaya min menene matsalar amma taki, dole na kaita wani k'aramin gidana. A nan Haidar ya taso ba sai nace komai ba akan kulawar da yake samu sabida ban had'a sonshi da komai ba. Shekaran shi goma na fitar dashi waje karatu, sai dai dawowar shi ne mummunar kaddarar nan ta afku.''
*MAMAN KHADY*🙇🏻♀
[4/2, 11:15 AM] Re@l💍 K@usy🌹: 💞💞💞 *RUMANA* 💞💞💞
Na
*MAMAN KHADY*🙇🏻♀
(Mk)
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡
(Home of expert and perfect writer's)
Page 6
Kai tsaye b'angaren sauran abokan zamanta ta nufa hankali a tashe, razana tayi sosai lokacin da taga babu kowa a babban falon. Wayarta ta jawo ta danna musu kira d'aya bayan d'aya akan gatanan a babba falo tana jiransu. Mata ne mugayen mata suna da tsananin kishi tsakanin su amma sai suka had'ewa mahaifiyar Haidar kai, har sai da sukai yanda suka yi suka rabata da gidan bayan sun nakasa mata yaro.
Sunayin tarayya wajan ganin sun ruguza shi Haidar d'in gaba d'aya wannan dalilin ne yasa lokuta da dama suke danne kishin su, ammafa ko wacce cikin zuciyarta akwai wani mugun nufi dake makale wanda inda ko wacce zata samu dama tofa sai inda karfinta ya kare, amma a haka bazaka tab'a ganewaba domin ko wacce ta iya takunta.
D'aya bayan d'aya suka dinga shigowa cikin parlourn ko wacce taci gayunta sai kamshi ke tashi kai baka ce akwai wani mugun nufi a cikin zukatan suba. Hajiya bilkisu ta dai-daita nutsuwarta hanci a sama tace.
''Kun kuwa san meke shirin faruwa cikin a gidan nan?'' Hajiya saratu ta yatsina fuska tare da cewa.
"Babu abinda muka sani Bilki sai dai idan ke zaki gaya mana yanzu.''
"To akwai matsala babba ba k'arama ba domin kuwa alhaji na nan yana shirin yiwa Haidar aure wanda bamu san wace kala yarinyar zai auro mishi ba.''
Duk cikinsu babu wacce maganar bata doketaba amma da yake 'yan duniya ne babu wacce ta nuna, Saima hajiya Saude ce da tayi murmushi tace.
''Lallai daga gani makwad'ait ne idan ba haka ba waye zai ba mahaukaci d'iyarshi? kai bama haka ba anya ansan ya Haidar d'in yake kuwa da zasu bashi auran 'yarsu? kodai rufa-rufa aka yiwa iyayenta?''
Nanfa sukai shiru bayan sun tsayar da magana d'aya cewar duk wacce ta samu dama to lallai ta bugi cikin alhajin har sai ya fad'i gidan su yarinyar ta yanda zasuje su kashe maganar domin suna so su tona abinda shi alhajin ya rufe kowa yasan babu wani me hankali da zai d'auki d'iyar shi ya dankawa mahaukaci ita, kai ina bama zai yiwu ba.
*****
Bayan sati d'aya. A ranar muka dawo BAKORI bayan na gama zagaye dangina na uwa dana uba sunata nanata min sai sunzo biki insha Allah. Ni dai iyakata ido da murmushi domin gani nake yi kamar labari ne na kanzon kurege.
Aranar da muka dawo aranar alhaji Yahaya yazo gidan mu ya kuma ce wajena kawai yazo yana son magana dani. Rashin sabo tsakanin mu yasa duk hankalina ya tashi inna da kanta takai mishi tabarma har zaure sannan ta dawo gida bayan sun gaisa. Ban yarda na kalleshi ba a haka muka gaisa dashi sabida kunya inda ya fara da ce min.
"To Alhamdulillah *RUMANA* na san cewa babu wanda ya tuntub'e ki domin jin ta bakinki akan kina son auran Haidar ko bakya son shi, sabida ana ganin an isa dake. Toh nima ba tambayarki zanyi ba Rumana sai dai nayi miki godiya da amincewar da kika yi domin yin wannan jihadi, insha Allahu nasan zuwa gaba zakiji dad'i sannan zaki yi alfahari da hakan ina fatan Allah yai mana jagora kuma ya shigemana gaba a cikin wannan lamarin.''
Kaina a kasa na amsa da 'amin' ba tare dana bari ya jiba.
"Ga wannan waya ce Yusufa yace a baki ko zaku dinga gaisawa tsakaninku dashi, sannan dan Allah kadda kidamu da rashin ganin mijinki a yanzu domin sainan da watanni biyar zai dawo, ke kuma kinga yanzu saura satittika ya rage ayi bikin ku, zan turo miki Usman na wajena ai na san kin sanshi, to abokin shi Haidar d'in ne saiku dinga aiwatar da komai dashi na hidimar bikin kinji ko? Koda kina bukatar wani abun shi zakiwa magana kin fahimceni ko?''
Kaina a kasa nace ''Ehh nagode Allah ya saka da alkhairi.''
Komawa nayi cikin gida jikina duk ya gama yin sanyi, jinai kawai hankalina be kwanta da wanda zan aura din ba to inba haka ba shi ace zamu gaisa din dashi mana amma sai ace da mahaifinsa zamu yi, gaskiya nifa dama can bana kaunar na auri wanda baya sona sabida idan namiji baya sonka wallahi komai zai iyayi dan ganin ya wulakantaka, bare shi wannan daga yanda naga labarinshi kudi sun gama bud'e mishi idanu, wai tsaya ma wani kalane shi mijin da zan aura..? Tambayar da bata da amsa a yanzu kenan.
******
''Alhaji kayi hakuri kamar yadda na gaya maka a wancan lokacin kaki yadda to yauma daka dawo maganar zan nanata maka, yaronka kwakwalwar shi lafiya lau take, sannan bashi da wata lalura mai alama da tabin hankali, kawai dai an kauce hanya ne aka had'ashi da mugayen aljanu wad'anda suke zuwa suna bidirinsu ajikin shi wani lokacin, shine zakaga ya koma kamar mahaukaci amma sam ba mahaukaci bane. A tun lokacin da nayi maka wannan bayanin idan da ka amince inaga da yanzu Allah ya bashi lafiya domin Allah zamu rok'a kuma shine zai yi maganin komai, Amma lokacin saika nuna kai a'a ba zai yiwu ba sabida kana tunanin baka nufin kowa da sharri dan haka babu wanda zai nufeka dashi ko? To yanzu ba k'aramin kuskure bane, dan wanima bakasan shi ba amma yana nan yana neman hanyar da zai cutar dakai balle kuma wanda kasani kuma yake jikinka, Bawai ina nufin wani naka bane yaiwa yaronka wannan sharrin a'a kawai dai inaso in nuna maka cewa k'addarar Allah yawa ne da ita sannan zakaga komai yana da sila da sanadi yanzu dai fatan mu Allah ya shige mana gaba ya kawowa yaron nan sauki.''
Muskutawa yayi kafin yace. ''Amin ya Allah, nagode malam to yanzu wane mataki ya kamata afara bi?''
''Alhaji wai kakai matar ka asibiti kuwa?'' Ba tare da na bata wata kulawa ba nace.
''Ban kai taba amma tace min ita taje.''
"To katashi kaje ka bincika idan ba haka ba kakusa d'aukar shege a hannunka tunda kowa yasan baka haihuwa ita kuma ai laulayi take yi.''
Ban san lokacin da nakai d'akin Fatima ba a lokacin, aikuwa saina tarar da ita tana ta amai duk ta galabaita, ban yadda cewa Fatima zata iya cin amanata ba domin koda na aureta budurwa na sameta sannan suna da duki ya dai-dai bakin gwargwado bare nace kwadayi zaisa tayi min haka. Da kaina na taya ta tagyra jikinta sannan nace muje asibiti. Likita ne ya tabbatar min da cewa ciki ne da ita na wata uku.
A wannan lokacin rasa abinda zanyi nayi shin farin ciki zanyi ko kuwa bakin ciki. Yayinda ita Fatiman naji ta saka ihu harda birgima ita wallahi ba ta son cikin ya za'ai ace duk cikin matana babu wacce naiwa ciki sai ita, ita wallahi sai dai azubar dashi. Na shiga tashin hankalin jin kalamanta wanda yasani fallamata mari sai dai kuma tana kukan najawota jikina na rungume sabida tunanin da gaskiyarta fa kuma dole ta shiga damuwa.
Bayani naima likitan tun daga farko har karshe yayi min tambayoyi sannan yace zai min awo. Gado aka bata domin ta huta nikuma a lokacin naga likita, sai dai iyakar binciken su sun gaya min cewa iyakar kwan haihuwata guda d'aya ne kacal kuma na fitar dashi akan Fatima.
Kusan ban yadda da maganar su ba saina shirya mana tafiya nida Fatima a wannan lokacin zuwa India, nanma maganar d'aya ce domin har cikin Fatima sai da suka bincika min cewar lallai cikin nawa ne kumama namiji ne jinana ne. Saudiyya muka wuce nan ma saida suka gama binciken su amma duk maganar d'aya ce dan haka anan na zauna nayi addu'a-nayi addu'a tare da nuna godiya ta ga Allah. A lokacin jinake babu abinda nake kauna sama da Fatima da abinda ke cikinta.
Matana sune suka fara sheganta min yaro sabida suna ganin aisu basu haihu ba sun manta cewa Allah shine mai tsara komai kuma a sanda yaso. Sai da mukai masifa dasu harma nayiwa Bilkisu saki d'aya sannan suka saduda suka bari alokacin ne nayi musu bayanin duk abinda ke faruwa tare da musu bayanan da likita yayi min a lokacinma harna basu zabi cewa duk wacce ke bukatar haihuwa to tayi min magana na sallameta sabida kadda na shiga hakkin su. Amma sai suka nuna zasu ci gaba da zama dani.
A lokacin da aka haifi Haidar kowa sai ya kara tabbatarwa da cewa lallai yaron jinina ne domin beyi kama da maman shi ba dani yayi kama kamar nayi kaki sai dai ya dauko farar fatar mamarshi domin tafini fari nesa ba kusa ba. Nasami haihuwa Ruma a lokacin da na fidda rai da samu shi yasa nayi shagali iyakar shagali sannan na saki kudi sosai aka yi taron suna.
To nidai bazance ga abinda ya dinga faruwa ba a tasowar Haidar sai dai dole tasa na kai Fatima wani gidana sabida a lokacin tace in dai ban raba musu gida ba to wallahi gidan su zata tafi, gashi nayi-nayi ta gaya min menene matsalar amma taki, dole na kaita wani k'aramin gidana. A nan Haidar ya taso ba sai nace komai ba akan kulawar da yake samu sabida ban had'a sonshi da komai ba. Shekaran shi goma na fitar dashi waje karatu, sai dai dawowar shi ne mummunar kaddarar nan ta afku.''
*MAMAN KHADY*🙇🏻♀
[4/2, 11:15 AM] Re@l💍 K@usy🌹: 💞💞💞 *RUMANA* 💞💞💞
Na
*MAMAN KHADY*🙇🏻♀
(Mk)
*HASKE WRITER'S ASSOCIATION*💡
(Home of expert and perfect writer's)
Page 6
Kai tsaye b'angaren sauran abokan zamanta ta nufa hankali a tashe, razana tayi sosai lokacin da taga babu kowa a babban falon. Wayarta ta jawo ta danna musu kira d'aya bayan d'aya akan gatanan a babba falo tana jiransu. Mata ne mugayen mata suna da tsananin kishi tsakanin su amma sai suka had'ewa mahaifiyar Haidar kai, har sai da sukai yanda suka yi suka rabata da gidan bayan sun nakasa mata yaro.
Sunayin tarayya wajan ganin sun ruguza shi Haidar d'in gaba d'aya wannan dalilin ne yasa lokuta da dama suke danne kishin su, ammafa ko wacce cikin zuciyarta akwai wani mugun nufi dake makale wanda inda ko wacce zata samu dama tofa sai inda karfinta ya kare, amma a haka bazaka tab'a ganewaba domin ko wacce ta iya takunta.
D'aya bayan d'aya suka dinga shigowa cikin parlourn ko wacce taci gayunta sai kamshi ke tashi kai baka ce akwai wani mugun nufi a cikin zukatan suba. Hajiya bilkisu ta dai-daita nutsuwarta hanci a sama tace.
''Kun kuwa san meke shirin faruwa cikin a gidan nan?'' Hajiya saratu ta yatsina fuska tare da cewa.
"Babu abinda muka sani Bilki sai dai idan ke zaki gaya mana yanzu.''
"To akwai matsala babba ba k'arama ba domin kuwa alhaji na nan yana shirin yiwa Haidar aure wanda bamu san wace kala yarinyar zai auro mishi ba.''
Duk cikinsu babu wacce maganar bata doketaba amma da yake 'yan duniya ne babu wacce ta nuna, Saima hajiya Saude ce da tayi murmushi tace.
''Lallai daga gani makwad'ait ne idan ba haka ba waye zai ba mahaukaci d'iyarshi? kai bama haka ba anya ansan ya Haidar d'in yake kuwa da zasu bashi auran 'yarsu? kodai rufa-rufa aka yiwa iyayenta?''
Nanfa sukai shiru bayan sun tsayar da magana d'aya cewar duk wacce ta samu dama to lallai ta bugi cikin alhajin har sai ya fad'i gidan su yarinyar ta yanda zasuje su kashe maganar domin suna so su tona abinda shi alhajin ya rufe kowa yasan babu wani me hankali da zai d'auki d'iyar shi ya dankawa mahaukaci ita, kai ina bama zai yiwu ba.
*****
Bayan sati d'aya. A ranar muka dawo BAKORI bayan na gama zagaye dangina na uwa dana uba sunata nanata min sai sunzo biki insha Allah. Ni dai iyakata ido da murmushi domin gani nake yi kamar labari ne na kanzon kurege.
Aranar da muka dawo aranar alhaji Yahaya yazo gidan mu ya kuma ce wajena kawai yazo yana son magana dani. Rashin sabo tsakanin mu yasa duk hankalina ya tashi inna da kanta takai mishi tabarma har zaure sannan ta dawo gida bayan sun gaisa. Ban yarda na kalleshi ba a haka muka gaisa dashi sabida kunya inda ya fara da ce min.
"To Alhamdulillah *RUMANA* na san cewa babu wanda ya tuntub'e ki domin jin ta bakinki akan kina son auran Haidar ko bakya son shi, sabida ana ganin an isa dake. Toh nima ba tambayarki zanyi ba Rumana sai dai nayi miki godiya da amincewar da kika yi domin yin wannan jihadi, insha Allahu nasan zuwa gaba zakiji dad'i sannan zaki yi alfahari da hakan ina fatan Allah yai mana jagora kuma ya shigemana gaba a cikin wannan lamarin.''
Kaina a kasa na amsa da 'amin' ba tare dana bari ya jiba.
"Ga wannan waya ce Yusufa yace a baki ko zaku dinga gaisawa tsakaninku dashi, sannan dan Allah kadda kidamu da rashin ganin mijinki a yanzu domin sainan da watanni biyar zai dawo, ke kuma kinga yanzu saura satittika ya rage ayi bikin ku, zan turo miki Usman na wajena ai na san kin sanshi, to abokin shi Haidar d'in ne saiku dinga aiwatar da komai dashi na hidimar bikin kinji ko? Koda kina bukatar wani abun shi zakiwa magana kin fahimceni ko?''
Kaina a kasa nace ''Ehh nagode Allah ya saka da alkhairi.''
Komawa nayi cikin gida jikina duk ya gama yin sanyi, jinai kawai hankalina be kwanta da wanda zan aura din ba to inba haka ba shi ace zamu gaisa din dashi mana amma sai ace da mahaifinsa zamu yi, gaskiya nifa dama can bana kaunar na auri wanda baya sona sabida idan namiji baya sonka wallahi komai zai iyayi dan ganin ya wulakantaka, bare shi wannan daga yanda naga labarinshi kudi sun gama bud'e mishi idanu, wai tsaya ma wani kalane shi mijin da zan aura..? Tambayar da bata da amsa a yanzu kenan.
******
''Alhaji kayi hakuri kamar yadda na gaya maka a wancan lokacin kaki yadda to yauma daka dawo maganar zan nanata maka, yaronka kwakwalwar shi lafiya lau take, sannan bashi da wata lalura mai alama da tabin hankali, kawai dai an kauce hanya ne aka had'ashi da mugayen aljanu wad'anda suke zuwa suna bidirinsu ajikin shi wani lokacin, shine zakaga ya koma kamar mahaukaci amma sam ba mahaukaci bane. A tun lokacin da nayi maka wannan bayanin idan da ka amince inaga da yanzu Allah ya bashi lafiya domin Allah zamu rok'a kuma shine zai yi maganin komai, Amma lokacin saika nuna kai a'a ba zai yiwu ba sabida kana tunanin baka nufin kowa da sharri dan haka babu wanda zai nufeka dashi ko? To yanzu ba k'aramin kuskure bane, dan wanima bakasan shi ba amma yana nan yana neman hanyar da zai cutar dakai balle kuma wanda kasani kuma yake jikinka, Bawai ina nufin wani naka bane yaiwa yaronka wannan sharrin a'a kawai dai inaso in nuna maka cewa k'addarar Allah yawa ne da ita sannan zakaga komai yana da sila da sanadi yanzu dai fatan mu Allah ya shige mana gaba ya kawowa yaron nan sauki.''
Muskutawa yayi kafin yace. ''Amin ya Allah, nagode malam to yanzu wane mataki ya kamata afara bi?''