← Book details Raino Ne Sila Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 3 OF 30

Sashe 3

Raino Ne Sila Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Daga haka tayi mata sallama ta fita,mayar da idonta tayi kan Anusha sosai take kallon ƴar cike da so da ƙauna sosai yarinyar take da kyau mai ɗaukar hankali amma skin ɗinta dark Chocolate ce ga manyan ido masu ɗauke da zara-zaran gashi,sai ƙaramin baki mai ɗan kaurin lips haɗe da red lips masu kyau,sosai face ɗinta yake ɗauke da manyan dimples sai gashin girarta dake kwance zara-zara za'a iya kiranta mai oval face a taƙaice,gashin kanta sosai yake da tsawo har zuwa bayanta wanda aka rabashi 2 aka saka ribborn masu kyau sosai jikinta yake a buɗe da alamar saurin girma zatai gashima yanzo tana 6years inda jikinta yake a buɗe,cikin 10minutes Hajia ta gama ƙare mata kallo ɗan kallonta tayi tace.

"Beby maza jeki kiramin yayanki Mus'ab a wancan É—akin"ta faÉ—a tana nuna mata É—akin.

A hankali tayi hanyar ɗakin tana zuwa ta tura kofar ɗakin a hankali,cikin Rashin sani a dai² lokacin data kai kanta ɗakin dai² lokacin da Mus'ab yayi ƙasa ta towel ɗin jikinsa.

Dan Allah dukkan wacce ta karanta indai har yayi mata daɗi inason ta nunamin ƙauna wajan yin SHERE ɗinsa da kuma COMMENTS with her name nasan zai iso gareni pls guys.

Comments#
Shere#
Vote#

*🤱🏻RAINO ne SILA🤱🏻*
_ADOPTION IS THE REASSON BEHIND_

*_NIMCY LUV_*
👸🏻S@r@ut@👸🏻

@wattpad
Nimcyluv

*If you really love me* *then step up and prove it. If not*
*then walk away* *because I can't stand the pain.🤟🏻*

*21↪️22*

Wani baƙin cikine ya kama Ahmad A.j ganin turancin da Najwa tayi masa gaban members ɗinsa,wata irin tsawa ya daka mata haɗe da hankaɗeta ta faɗi ƙasa,nunata ya shigayi da hannu.

"Kee! Ashe baki da hankali,which kind of rubish is this?am i ur mate or what,so ki shiga hankali kafin na nuna maki fushi na"

Yana gama faɗin hakan yayi waje kafin ya ƙarasa fita tayi saurin tashi tasha gabansa,kallonsa tayi ido cikin ido tace.

"Haƙiƙa Allah shine ya ɗoramin sonka A.j,kuma ko wanne bawa akwai nashi ƙaddarar,rayuwace kaima zaka iya sintar kanka a irin halin dana tsince kaina,ina rokon Allah yasa maka son wata wacce son nata zai zama illa awajanka,kana ji kana gani za'a rabaka da ita badan baka da ikon samunta ba"

Wani huci ya fitar mai zafi gaske,ganin idan yayi mata magana zata ƙara yi masa wani haukan,hakan yasa yayi saurin ficewa daga Hall ɗin gaba ɗaya,wani irin zafi ya keji a maƙogaransa sabida baya iya long talking gashi waccen stupid ɗin yau tashi,da sauri yake taga steps ɗin benen cikin 2minutes ya gama sauka daga kai,hana zuwa compound na Hotel ɗin dake Singapure yayi saurin yin wajan motarsa drever na ganinsa yayi saurin ƙara suwa wajansa haɗe da buɗe masa kofar motar ya shiga,da sauri ya koma mazaunin drever yaja motar da gudu,gaba ɗaya idonsa ya sauya kala wani irin ciwo rabin head ɗinsa yake masa,idonsa ya lumshe yayinda hannunsa kekan mararsa tun lokacin da Najwa ta faɗa jikinsa yaji mararsa tayi wani irin ƙullewa yanzu haka ji yake kamar zata tarwa tse,yana wannan tunanin yaji anyi parking motar alamar sunzo,bai jira abinda drever ke cewa ba yayi ficewarsa daga motar,yana zuwa ɗakin yaga an gyarashi fes babbar rigarsa ya fara cirewa sannan ya cire sauran ya koma daga shi sai boxer,wata irin zufa ke keto masa ta ko ina sabida yadda mararsa take masa ciwo,saurin haɗa tea yayi haɗe da matsa lemon tsami a ciki,tea cup ɗin ya ɗauka haɗe da kafawa a bakinsa bai ajjiye ba saida ya shanye tas,kwanciya yayi luf akan bed ɗin yayinda yake ajjiye numfashi a hankali,wajan 5minutes ya samu realif daga pin daya keji,hakan ya nuna abinda ke damunsa yayi nasarar narkewa,gaba ɗaya zaman ƙasar ya dame shi burinsa kawai ya ganshi wajan Hajiyarsa hakan yasa yayir kwanan garin Abuja ayau.

********
Yana fita ta durkoshe a wajan tana wani irin wahalallan kuka mai tsuma zuciya.

"Why?meyasa zai mata hakan meye nata bai cika ba a mantan da akeso?wallahi ko zata rasa komai nata sai A.j ya zama mallakinta"da wannan tunanin ta goge hawayen face dinta tayi waje.

Haka mutanan Hall É—in suka dinga fita,wasu nayi Najwa kallan mara tarbiya wasu kuma nayiwa Chairman A.j kallan mara tausayi da haka kowa ya kama gabansa.

*****
Saurin yin ƙasa da kai Anusha tayi,a fusace ya ɗauki towel ɗin ya ɗaura a weast ɗinsa zata juya kenan taji yayi saurin tamkota.

"Kee! Daman baki da hankali dan Ubanki"

ÆŠan turo baki tayi gaba sannan tace.

"to Yah-ya menene?nima Mamata tana yimin Tsirara fa,tace wai babu komai ni ƙarama ce" ta faɗa tana washe fararen hakoranta masu haske da sharning.

Gwalo ido Mu'ab yayi waje jin abinda ta faÉ—a,yace.

"to dan Ubanki ni ƙarami ne kamarki?"

Ɗan ya motsa face tayi kana ta turo baki gama tace."to kai Yah-ya me kake ɓoyewa ne?ta faɗa lokacin da take taɓa gaban towel ɗin.

Saurin janye hannunta yayi ji yaye kamar anyi masa shocking,hannu yasa ya dalle mata baki nan take ta fara kuka haÉ—e da yin tsalle.

"dan Ubanki na ƙara ganinki a ɗakin nan saina ɓallaki,banza talkative,kuma ke cewa Hajia ina zuwa dan nasan abinda ya kawoki kenan,shegiyar ƴar mai surutun tsiya"

Da gudu ta fita a É—akin tana kuka tana zuwa ta faÉ—a cinyar Hajia haÉ—e da sauke ajjiyar zuciya.

"A'a Beby wane ya taɓamin ke?"

Turo baki tayi lokacin da take kwanciya a ƙirjin Hajia tace.

"ba Yah-ya bane wai danna ganshi..kafin ta ƙarasa taji ya daka mata wata uwar tsawa.

*******
Bayan tayi Alwalal ta shinfiɗa wani ƙaramin ɗan kwali ta shiga yin salla,wajan 10minutes ta iddar da sallar nan ta fara kaiwa Allah kukanta tana zubar da hawaye.

"Ya Allah kaine gata na,dukkan abinda zai sami bawa saida yardarka,komai ya samu bawa to an rubuta hakan a Lauhil mahafus nayarda da ƙaddara mai kyau ko mara kyau Allah ka bani hakuri da juriya,Allah ka kawomin sauki cikin rayuwata,Ya Allah duhun dake cikin rayuwata Allah kasa haske ya maye gurbin"ta shafa Addu'ar tana zubar da hawaye.

Juyi kawai take hannunta riƙe da cikinta wani irin ciwo ta keji kamar zata mutu,hakan ya farune sakamakon Rashin cin abinci da ba tayi tun jiya,yanzu ina zata ga abinci?waye zai mata abincin?jin wannan tunanin bazai mata ba yasa tayi saurin ɗaukan Hijab ɗinta take ajjiye wanda shi kaɗai ya rage mata gaba ɗaya Inna Talatu ta kwashe su,cikin sauri ta fita aɗan ƙaramin gidan nan ta fara bin layi² ko Allah zaisa ta samu abinci,amma abu kamar wasa har kusan magari ba bata samu ba,jin an fara kiran salla yasa tayi hanyar gida ko gabanta bata gani sabida yunwa da kuma wani jiri take ɗibanta,sam bata iya ganin gabanta sabida duhun da take gani,tana gaf da yin layin gidanta ta hango wani yana rabon birede cikin sauri ta nufi wajan tana zuwa ta hau layi kamar yadda taga anayi.

Haka aka dinga bawa kowa 1 by 1 har layi yazu kanta,daman guda É—aya ya rage haka aka É—auko da niyar bata wani Almajiri yasa hannu ya fisge haÉ—e da rugawa da gudu.

Sorry for the short typing,hakan ya faru ne sabida book É—in kuÉ—i da nake,gaba É—aya hankali na kansa (sai na aureta)08119237616

Comments#
Vote#
Shere#

*🤱🏻RAINO ne SILA🤱🏻*
_ADOPTION IS THE REASSON BEHIND_

*_NIMCY LUV_*
👸🏻S@r@ut@👸🏻

@wattpad
Nimcyluv

_Guys a kakkaɓe zani😛sadaukar ga my fans🤟🏻pls shere_

*بسم الله الرحمن الرحيم*
*____________________________________*

*🌈🇰AINUWA 🇼RITER'S✍🏼*
*🇦SSOCIATION🤝🏻*
```{United we stand and succeed;Our ambition is to entertain & motivate the mind of readers}```
https://www.Facebook.com/kainuwawritersassociation
*____________________________________*

*23↪️24*

Jikinta ne ya fara rawa jin irin tsawar da Mus'ab yayi mata kwabe baki tayi haɗe da bashewa da kuka ta ɓoye kanta cikin ƙirjin Hajia,cikin ɓacin rai da ƙonan zuciya Hajia ta kallesa tace.

"bana son irin wannan fa Mus'ab daga aikenta shine zakama Bebyn haka"ta faɗa tana nuna masa ɓacin ranta.

Ɗan rausayar da kai yayi haɗe da ɗora kansa a ƙirjin Hajiayar,yayinda face ɗinsu ya haɗe shida Anusha,shagala yayi da kallon cikin idonta yayin da ita kuma take zabga masa harara.

"am sorry Hajiata ban ƙarawa pls"

Shafa kansa tayi hakan yasa ya lumshe idonsa yana jin wani irin soyyayar mahaifiyar tasa har ƙasan zuciyarsa."shikenan kada ka sake dukan Our beby,waima me tayi maka?"kafin yayi magana Anusha tayi saurin ɗaga kanta haɗe da cewa."Hajia wai danna ganshi babu kaya ai naga nima Mamana tana ciremin kaya idan zatai mani wanka ance yara basu da hankali ai"sosai Hajia take dariya jin abinea beby take faɗi yayinda Mus'ab ransa yake masa suya sabida ɓacin rai da baƙin ciki haɗe da kunya domin yana da kunya sosai,saida tayi dariya mai isarta sannan tace.
"A'a beby you are right shima ni yake jira nayi masa"ta faɗa tana kunshe dariyarta,washe baki Anusha tayi take dimples ɗinta suka lotsa"Hajia shime kene kike mashi wanka?"kai kawai ta ɗaga mata sabida dariya,gyara zama tayi a cinyar Hajia sannan ta kalli wandon Mus'ab ta juya ta kalli Hajia tace."kenan shi ba'ayi mashi kaciya ba?Mamana tace idan akayiwa mutum kaciya toya girma,Mus'ab najin haka yayi saurin tashi haɗe da yin gudu ya shige ɗakinsa,haba me Hajia zatai idan ba dariya ba saida tayi dariya sosai sannan ta kalli Anusha tace."Beby babu kyau kallan babba babu kaya,dukkan mutumin da yake buɗe tsaraicinsa ga wani to Allah ya tsine masa,cikar mutuncin mutum da kuma kima shine wanda yake riƙe mutuncinsa kada ki sake ki ƙara kallan babba babu kaya,kasa ki sake koda wasa naji kin buɗewa wani jikinki fatan kin fahimta?"ɗaga kai tayi alamar "eh"kanta ta shiga shafa tana jin soyyayar yariyar cikin zuciyarta jin saukar numfashinta tayi alamar bacci ya ɗauketa,hakan tasa ta kwantar da ita a hankali ta tashi domin zuwa Hosbital duba marasa lafiyanta.

Yana shiga ɗakinsa ya murza key haɗe da sauke wata ƙatuwar ajjiyar zuciya,wannan wacce irin mara kunyar yarinya ce talkative gril,mtwss wallahi saina ci ubanta shegiya da ido kamar mage mitsitsiya da ita ta iya kunyata mutum,shi yanzu da wanne ido zaiga Hajia'nsa?da wannan tunanin yayi kwance akan bed yana sauke numfa tunuwa yayi da golden eyers ɗinta masu haske da sharning ɗan taɓe baki yayi haɗe da cewa."shegiya ƴar baƙa kawai"da wannan zancen bacci ya ɗaukesa ba tare daya shirya ba.
Chapter 3 · 0% Book details