← Book details Meke Faruwa Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 9 OF 60

Sashe 9

Meke Faruwa Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Tsaida bikin watan may,wata biyu kenan, shirin bikin suka kama saboda babu lokaci ishasshe,Mansu dai rigima suke tasha da farooq,duk da irin lallashin da yake mata. Ana sauran sati biyu bikin yace za'a kawo akwatuna,nan tasa mishi rigimar in dai bai yi ma Bilkisu komai da yayi mata na akwatin ba,wallahi ba zata taba saka kayan ba,kallonta ya tsaya yi yana tunanin kanta daya kuwa?Yace kin san nawa na kashe mansura?Tace ni ina ruwana ko gida bana saka kaya in har bata da irinshi in ma kasan baka da halin yi mata tun kan a kawo kaje ka raba mana wanda ba iri daya ba ne ka canzo ta fitittike taki sauraronshi kan dole yaje ya sayo zannuwan da ta kalman zuwa gyalulluka,kayan shafa da akwatuna ne bai sa yaba da 'yan kunne,yaje ya aje,randa aka kawo akwatuna suna makaranta amma sun san da zuwan 'yan kawo kayan,tunda yan gombe ne zasu amsa daganan sai suka hadu da danginAbba da na farooq su kawo zaria, kawayen,umma ne suka tari yan kawo kayan kaya ne na ban mamaki, da suka dawo daga mkrnta gidansu Bilkisu suka zame
Mamanmu tana basu labarin kaya,Bilki duk ta matsu suje su gani, masha Allah in ji bilkis time da ta gama duba kayan,umma farooq yayi kokari,mansu kam kosawa tayi yazo ran sati don ta ji ina na sahibarta? Ya kam iso da kayan cikin katuwar akwati guda daya ko rufuwa bata yi, amma sai mansu tace ita kam sai ya sayi set din akwatin,yace haba mansu wlh account dina yanzun ba ko naira,yakike son in yi? Tace to gaskiya zan je in ciro 2 ka hada mata da wannan ni sai na dauki biyu da ket,yana mamakin wane irin so ne wannan mansu take ma Bily?Suna cikin haka sai ga bilkisun, da fara'arta ta kwankwasa glass din motar a tare suka fito tace brother kasha kamshi fa,yace kanwata ya gari da shirye-shirye? Tace mungode Allah,ya naku? Bata jira amsar shi ba, ta dubi mansura dake cika tana batsewa,tace yaya ne mansu any problem?Mansura ta dan daga kafadunta alamar babu dan bata son tasan maganar. Farooq yace akwai ya koro mata komai, kasa magana bily tayi kallon mansu kurum take yi...
Kafin daga baya tace laifin kane farooq daka ki sanar dani harka biye mata kasiyo kayan yanzun kuma zaka juya da sune ka mai da bana so kuma na lura mansu bata son mu rabu lfyne, ni da ita,shawarar da zan baka kai namiji ne,kuma sai yanda tace zaka sha wahala don bata da hankali kasa ni kai ne mai bada umarni da hani suna gurinka,so be carefull,kaya kuma nagode bana so ko ka kara mata ko kuma ka maida ka amshi kudinka.ta juya ta koma gida tana mamakin son da mansura take mata, nan ta kara shiga damuwa dama tana tare da tunanin yanda zata kasance in mansu tayi aure tunda yanzun ma gidan take kwana,amma taji mamanmu tana cewa zata sa atoshe uwar dakinta abude ma Bilkisun kofa ita da Asma'u,mkrnt tare ko ina tare,Umma suka kaima kayan itama sai da tayima farooq fadan biyewa mansuran sannan tayi godiya ta kira mamanmu ta bata, mama ma kin karba tayi sai da Abba yasa baki yace kayan mansura na Bilkisu ne,haka nan kayan Bilkisu na mansura ne shi ko daya baiga laifin mansura don tace mijinta yayi ma Bilki kayaba Bilkisu taki ayi wasu bidi'o'i a bikin tace walima kurum zasu yi in da zasu gayyato mlmai dan su yi wa'azi haka ko akayi,dama daurin auren can gomben aka yi sun soma walimar bayan sallar la'asar,inda malama sa'adiya tayi wa'azi akan hakkin aure wato miji akan matarsa Bilkisu wace suke zaune kusa da juna ita da mansu tace kin dai ji ko?Mansu kam jikinta ne yayi sanyi,dayake gombe za akaita can ma akayi jeren in hutun shi ya kare sai ya samar mata gida nanzaria saboda karatu shi kuma zai na zuwa mata hutun karshen mako.washe gari suka dauki hanyar gombe kuka mansu keyi tun daga zariya har gombe haka nan bilkisu sai ma washe gari randa zasu dawo a wannan rana mansu da bily sun sha kuka,da kyar suka rabu har ma wasu sun taya su kukan, aure kenan, tun a mota bilkisu ta soma kewar mansu, dashi ke su mamanmu ne suka je jere gomben basu je kai amarya ba,mama ma a talauce dubu biyar taba umma da kyar ma ta amsa.
Bilkisu kam itama mamanmuce ta bata dubu bakwai tayi ma mansu yar sayayya ba dan sun ishe ta ba,sai don bata dashi amma tasha alwashin in ta gama karatu tana kama aiki zata kula da mansu fiye da kanta,ba don mansu bata da shi ba,sai donta kwanta,hakanan Bilkisu taci gaba da zuwa makaranta ita daya, amma kullum sai tasha kukan rashin mansu. Can ma gombe ango yakasa gano kan amaryarshi,duk da lallashi gami da ban bakin da yake mata,har dan hutun nashi na sati hudu ya kare,kafin nan yasamu dan madaidaicin gida,suka dawo sunyi murna da ganin juna ita da mansura suka ci gaba da zuwa mkarnta. Wannan satin ko nace Friday farooq yazo dawuri lokacin suna makaranta shi ne yaje yazo da su bayan ya kira mansura cikin new phone din ta nokia.cewa gashi nan zuwa nan take ta canza fuska har Bily ta gane, tace bakiso zuwanshi ba ne?Tace a'a nadai gaji ne.Bily taso su sauke ta gida amma sai farooq yace yana son magana da ita,agidansu ne yake cewa na sani be dace in miki zancan nan ba sbda ke ba matar aure bace kuma irin zancan nan..
[8:46AM, 12/28/2016] �+234 814 912 1821�: 🏵MEKE FARUWA 17🏵

bai dace ya hada mu ba sai dai dole ne in mikishi dan nasan kece zaki iya min mganin abin da yardar Allah mansura dai tun da muka yi aure sam taki yarda dani yau sati biyar kenan sai kace wata yar karamar yariya.na mata wa'azin nayi fadan nagaji tana cutar dani,batun yayi ma Bily nauyi har ma ta kasa kallon farooq,amma duk da haka tace kayi hakuri ka yafe mata tayi kuskure bazata kara ba,taja hannun mansu cikin dakinta,suka zauna gefen gado ta dube ta cikin yanayin damuwa, kin san masifar dakike ciki kuwa?Kin san zunubin da kike diba? Koda yake nasan kin sani tunda tare muka yi karatu nace malami daya ya koyar damu,..nan dai Bily Tai tayi mata fada da nasiha..!Cikin hawaye take ma bilkisu wlh bily,tsoro nake ji,dariya ma ta ba bilkisu, jibe ki wai tsoro ta mike ina son gobe labari ya canza in ba haka ba wlh- wlh kinemi wata bilyn bani ba,ta fita mansu ta biyo ta tana kira,kin tsayawa tayi farooq ya biyota shine ya sauke ta gida lokacin Babansu yana nan zaune awaje tare da wasu yan uwansu,kallo yabita dashi.Baba tsalha wan shine yadube shi.
Yace toga shaida kana gani? Amma zan dauki mataki,gara dai cewar baba tsalha. washi gari tun misalin bakwai saura sai ga farooq yayi sallama da Bilkisu, suka gaisa yace ta taimaka suje gida ta lallasar mashi mansura tana can tana ta kuka ko kula shi taki tayi Bily tayi maza ta shirya ta bishi suna shiga gidan mansu tayi saurin fadawa jikin mansu ta kara fashewa da kuka tana Allah farooq baya sona baya tausayi na mansu tayi saurin rufe mata baki tana lallashin ta nan ta wuni tana kula da ita sai dare ta tafi.

Baba tsalha yakalli mamman sannan yace,ina jinka mamman, kace Inusa ya shirya aure?Mamman yace, haka nace.Baba tsalha yace,ban da kai mamman wanne mahaukacin uba ne zai ba Inusa auren 'yarsa? Yaron da bai san ciwon kansa ba,sai shaye-shaye da bin kwararo yana damke kajin mutane da agwaginsu ba sana'a. Malam mamman yace to nina bashi Bilkisu tunda ita shegen bakin jini yayi mata yawa,Baba tsalha yace to ni fa ba ruwana kuma bani da kudin masa aure, mamman yace dama ai sadaka zan bashi,kuma da zaka ce babu ruwanka ka sani ko sanadin auren ya shiryu?Baba tsalha yace shi kenan zan mishi bayani.Abin ban mamaki,Inusa ma da tsohonshi baba tsalha yakira shi yayi mishi zancan Bilkisu cewa yayi a'a tafi karfinsa.Babansu bilki tare da baba tsalhan ne suka tasa shi suna rokonshi ya yarda,yace zai dai yi tunani. Yayi sallama kofar mamanmu tana ninke kayanta yayin da Bilkisu ke cin tuwo,fuskarshi sam babu annuri gaban bilkisu ya fadi dama duk sanda ta ganshi sai gabanta yayi muguwar faduwa,balle yanzun da ya shigo afusace,ya dube ta ke Bilkisu daga yau naba inusa ke tunda abin naki ya zama iyashege,haba dole mana maza suyi ta gudunki,kowa yana tsoron ciwon kanjamau, ashe maza kike bi, su ladiyo sun sha gaya min amma na kasa yarda sai yanzun da na gane ma idona,dan tsabar iskanci kam har kofar gida ake zuwa daukarki to na kawo kasrhen abin inusa shi ne na bawa ke,ido ta zuba mishi cike da mamaki tana kallonshi, yanzu ne ta kara yarda mahaifinta baya kaunarta,domin duk uban da yake son yarshi bazai taba yarda ya kwatanta ta da auren yaro irin inusa ba yaron da babu arabi balle boko, sai shaye-shaye,kullum cikin datti tamkar mahaukaci,ga satar tsiya ba sana'a tana cikin tunani ya katse ta,kin tsare ni da ido ba neman shawara nake yiba,umarni na bada dama ai nine musulunci ya bawa damar in zaba miki miji,bata san sanda tace amma baba Inusa baya daya daga cikin mazajan da musulunci ya yarda a basu aure, saukar mari taji sannan yace sai ki gaya min Wanda musuluncin ya yarda a bashi ke da kike rainawa yanzun haka ya ki sai lallashin shi ake yi ya rufa miki asiri har kina da ta cewa? Ya dube mama wadda ta tsananin bakin ciki da mamaki ya hanata magana yace kece ke zugata na jima da sanin haka to ki sani kan wannan Auren kema naki Auren yana siradin karshe, in kin tafi gidanku kuma in daura Auren ya fice fuu...... Kuka mai karfi Bilkisu ta saki sannan ta juya tana kallon Mamanmu cikin kuka take fadin Allah Mamanmu wannan karon bazan yarda ba ni ba zan aure inusa ba, shi baba baya kaunata Sam ta matsa ta kama kafafun mamanmu tana cewa me yasa baya sona? Me na mishi? Ko dai ni din ba yarsa bace?
Chapter 9 · 0% Book details