← Book details Meke Faruwa Part 3 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 10 OF 60

Sashe 10

Meke Faruwa Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kuka da mama ke makewa shi ne ya kwace cikin kuka take cewa nima wannan karan na gaji ai ba akan shi kike ba. Hakkinki da Allah ya dora mishi matsayinshi na uba bai kula dasu ba, sai yanzun ne zai ce hakkin shi ne ya zaba miki miji?

Zamu ji mugani, yan kwanakin nan rigingimu sun kankama cikin dan lokaci. Mutane kalilan ne suke cewa bai dace a aura ma inusa Bilkisu ba, tunda shi ba nutsattse ba ne, sauran kam sun ce an cuci Inusa, mahaifiyar Inusa ma tsalle ta daka tace sai da yar tayi kwantai sannan za a lika ma danta?

Har sassan su ta shigo cike da masifa ta samu mama tana wanka sai Bilkisu zaune ta tasa abinci ta kasa ci, saratu uwar Inusa ta dubi Bilkisu ta ce, ke ina uwarki gunta nazo, in kuma bata nan bari na baki sako ki gaya mata, ki ce nace hadin bai hadu ba kin gantsare kin rasa mai so za a maka wa dana? Har fa masallatai an kai cigiyar mai sonki an rasa, anyi yawo da hotunanki an gaji, ga bin maza ki je ki saka mishi ciwon zamani.

Mama ta aje bokitin wanka ta dubi saratu tace ke saro ki dube ni da kyau, in kina zaton nima na amince a hada min 'ya Da mahaukaci ne ki ka zo nan ki yi rashin mutunci to ki sake sabon tunani Inusa mutun ne? ina tambayarki? Don kunga ina muku shiru ba yana nufin tsoro bane kuma ba kasawa bane, duka nawa megadon take shekara 20 da yan watanni ne kuke mata wannan surutun, Ku shiga cikin unguwar nan Ku duba in babu wadanda suka girmeta . don haka daina daga jijiyar wuyanki nima ba zan yarda a dauki zukekiyar yarinya kamar maigado a ba Inusan da ko gabas bai sani ba bare yanda ake sallah,. Saratu cikin sanyin jiki tace oho dai na dai gaya miki kar a makalawa yarona, kila da ciwo ehe, mama tace ba gara kowane ciwo ba da ciwon dake jikinshi na jahilci, baki in yasan abin da zai fada bai San Wanda za a maida mishi ba, haka ce ta samu saratu ta tafi cike da kunya yayin da su Ladiyo dake gefe suna kallon suka ji haushin saratu yanda ta tsaya matar nan tayi mata ta tas.

Bilkisu ta ji dadin yanda mama ta gaggaya wa saratu magana, domin sun raina musu hankali a gidan rigima ta kasa karewa babansu Bilkisu da baba tsalha sun matsa ma Inusa randa ya amsa musu da dare cewa ya yarda washe gari da asubahi ya tattara yanashi- yanashi ya gudu don ba zai iya Auren Bilkisu ba, kuma shi kanshi ya rasa dalilin gudun Inusa yasa rigima ta tsananta uwarshi tace ba zata yarda ba kila asiri ne mama suka ma danta ya bar gari, su Ladiyo ma haka suka ce ma maigidan kuma ya hau kai ya zuna ya samu Mamanmu yana ta masifa fadi yake gara ma taje ta karya asirin tun kafin abu yayi nisa banza tai musu suka yi ta surutun su suka gaji suka yi shiru dama ance watan kwaram daya ne da ya wuce shi kenan. Sai dai ita kuma bilkisu tana mamakin akan kinta ne Inusa ya bar gari?In ko haka ne,da mamaki meke faruwa kenan?Lallai bakin jininta ya bunkasa, cikin dan tsakanin sakina ta haihu 'yarta mace, anyi suna da sati uku maryam ma ta haihu danta faisal yayin da yar sakina taci sunnan maman Abdul,Amina. suna kiranta da mimi, mansu ma anyi ciki shagwaba ta karu ga laulayi dole Bilkisu ta koma gidan saboda farooq kaduna yake in yazo Friday sai ta dawo gida.Haka rayuwar ta ci gaba da juyawa,Bilkisu tana zuwa makaranta har mansu ta haihu, dan yaronta mai kyau yaci sunnan baban farooq, suna kiran shi dady. Bilkisu tayi juyi yau shekara duka nawa ta sani ba wai tayi girman da za'a ce gashi gashi ba ne amma surutun mutane ya isheta,ita kanta tana so tayi aure yanzun.. Sai kuma gobe.

Yarima kwance kan wata kujera jikinshi sanye cikin gajeran fari tas din wando da yan singilet din ta, gefenshi Vicky ce sanye da da brezzier da pant wasannin su na yau da kullum suke tana da kusan rabi na abin da yake so a gurin mace, sun yi nisa cikin shagala Sam bai ji sallamar ba bare ya amsa,sai da mai sallamar ya shigo kai tsaye kuma ya rufe kofar da karfi da sauri ya zare bakin shi daga na Vicky wace ta soma fita daga hayyacinta, magajin Malam ne ya ce maza ka tashi tare da mai martaba....... Sallamar mai martaba ce ta katse magajin Malam daga maganar da yake, tsoro da faragaba tare da kunya ne suka rufe Yarima, Vicky kuwa tsawa magajin Malam ya mata, ta mike ta fita, Yarima yana zaune akan kafet ya dukar da Kan shi bai ji dadin wannan ziyara ta ba zata da da mahaifinshi ya kawo mishi ba, wannan shi ne karo na biyu da ya kamasa da mace wancan zuwan ya samu ya kare kanshi da cewa abokiyar karatunshi ce, duk da mai Martaban ya gansu ne suna kissing din juna, kuma bai ce ma Yariman kala ba shi ne dai yake ta borin kunyan shi to yau fa?

Da me zai kare kanshi? Dubi kayan jikinshi dubi nata, gara ma wancan karon duk da kaya a jinkinsu.

Magajin Malam ne ya soma magana afuwa Yarima yake nema Allah ya taya maka a yafe mishi. Mai martaba ya daga ma magajin Malam hannu alamar yayi shiru, sannan cikin magana irin ta manya yace, Modibbo dama saudiya zan shige na ratso domin in ganka, kuma na same ka lafiya duk muna waya kullum, yaya karatun naka? Cikin in-ina yace Alhamdulillah ranka ya dade, yaya su Umma? Ummar ka lafiya shin ko kana da matsalar kudi? Ya dan shafa kai I to ba dai sosai ba, mai martaba yace in da matsala ka fada, yace eh akwai bayan wannan fa? ya ce babu ranka shi dade, ita kenan, ya mike ya nufi kitchen yazo da ruwa da lemunkan sha, ya dire ma magajin Malam don yasan mai martaba ba zai sha ba, ya shiga daki ya saka kaya har lokacin jikinshi a sanyaye yake , yasan halin mahaifinshi sarai shirun da ya mishi ba yana nufin ya bar shi bane ya sani zai hukunta shi ta in da baya zato, don shi baya fada bare zagi, yanzun shi dai zai saurari hukuncin daza a yi masa Allah yasa kada ya maida shi gida nigeria da karatun shi dan ba ya son karatu can kuma matan can basa burge shi duk kyan ya mace .
[8:46AM, 12/28/2016] �+234 814 912 1821�: 🏵MEKE FARUWA 18🏵

kwanan mai martaba biyu a malaysia kafin ya wuce Saudi yayi kwanakin ne a wani shahararren masaukin baki dake cikin birnin na malaysia. Yarima sam bai yi mamakin shirun da mahaifin nashi yayi mishi ba. Domin yasan zai yi maganin abin, wani Abu da yaba magajin Malam mamaki, gidan Yarima yake kwana kuma ganin da mai martaba ya mishi bai sa Yarima ya daina kwana da mata guda biyu a shimfidarshi ba, don haka magajin Malam yake kwanciya a falo ko dayan dakin Yarima, magajin malam dai shine babban abokin Yarima kuma shi da ne ga waziri, mai martaba yana son shi tamkar Yarima. Shi yana karatun injiniya, yayin da Yarima ke karatun likita mai martaba yazo da shi don yaga abokinshi ya juya gida shi kuma ya wuce Saudi, bayan sun ga tashin mai martaba suka dawo gida, kai tsaye fridge magajin Malam ya nufa a kitchen ya dauko robar ruwa, kusa da Yarima ya zauna da yake kokarin kiran Ummarshi,

Layin ya ki shiga, ya dubi Yarima yana son yin magana amma yasan halin yan kayan shi, don haka sai yayi nufin share zancan amma kasancewar Yarima mai matukar saurin fahimta sai yace um'hum ina jin ka, magajin Malam yace ban yi magana ba.

Yarima ya dube shi cike da kasaita irin ta yayan sarakuna, sannan yace kana so yin maganar ne ai, magajin Malam yace nasan halinka ne zaka iya cewa yanzun ba time din amsa ba ne, Yarima yace tambaya zaka yi kenan?
Magajin Malam yace tun shekaran jiya nake son yin tambayar, Yarima yace bata dame ka ba ne da kayi ta koda ba zaka samu amsa ba.

Magajin Malam yace zan iya tambayar yanzun ko? Yarima ya tabe baki tare da fadin in kaso ba, magajin Malam ya gyara zama, dama ina son jin me yasa kaci ka son mata? Kuma me yasa ka canza daga silent din ka zuwa mara jin magana? Yarima ya ajiye wayar a gefenshi sannan ya ce na kasa samun Umma din ma ya kalli magajin Malam wacce zan amsa maka? Duka in har zan samu, ya ce to mata abin so ne don su ne nishadi na karshe, duk cikakken namiji mai lafiya yana son mata, sai dai kowa da nashi salon son, sannan ban canza ba har yau ina nan a silent dina, magajin Malam yace ka canza domin a da in har mai martaba ya hane ka da yin wani Abu ka bar shi har abada, amma yanzu ba ka damuwa da hakan. Yarima yace me ka gani? Ya ce in daina ban daina ba? watannin baya mun zonan dashi mun sameka da mace. Sai kuma gashi wannan zuwan ma gara wancan cikin sutura kuke wannan karon ba Ku da maraba da tsurara, sannan kuna cikin halin sumbatar Juna, kilama damun jima ba mu shigo ba mu same Ku cikin wani halin. Yarima ya zuba mishi ido babu wani hali da zaku same mu da ya wuce wannan domin ni kamar yanda ka sani komai da lokacin shi, wannan lokacin ne na wasanni kuma duk nacin mace ba zan wuce mata haka ba ka fahimta?
Chapter 10 · 0% Book details