Sashe 12
Meke Faruwa Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Mai martaba ya ce haka ne, kwarai na yi mamakin canzawar yaron lokaci guda, tsohon yace babu wanda zai gagara daga shaidan, don shi ba rago ba ne, yanzu kaje gida akwai istihara da zan yi game da al'amarin shi idan Ubangiji yaso sai musan ta in da za'a bullo, mai martaba ya shiga godiya tare da yin sallama da tsohon wanda ya yunkura ya tashi ya yo ma sirikin nashi rakiya zuwa gurin mota.
Yarima zaune kan wani dan dakali karkashin wata bishiya mai sanyi cikin makaranta, yana nazarin littafan biology, dago kan shin da zai ya sai ko ya sauke idanunshi kan wata yarinya 'yar mutanan China tana sanye da gajeran siket wanda iyakarshi tsakiyar cinyarta, rigar jikinta kuwa singileti ce mai dan siririn hannu,
Ta cikin gilashin idonshi yake kare mata kallo nan zuciyar shi ta kwadaitu da lafiyayyar fatar ta, da takusa in da yake sai ya yi tamkar bai ganta ba, a nata gefen yau ne gani na uku da ta mishi gayen ya tsaya mata a rai, tayi niyya yau zata kula shi ta tsaya gefenshi cikin harshen turanci take CE mishi sannu da hutawa kasaitar tashi ta motsa, yi yayi tamkar bai ji ta ba, sai da ta sake maimaitawa sannan ya amsa ba tare da ya dube ta ba, tace zata iya zama kusa dashi?
Yace in taso haka zata iya, ta zauna tana satar kallon shi, ta dan yi gyaran murya, sannan tace shin zata iya tambayarshi? Hannu ya daga mata kafin yace yanzu ba time din tambaya ba ne, shiru tayi na dan lokaci sannan ta ce to zai iya taimakon ta? Ko yanzun ba lokacin taimako ba ne? Ya bata amsa dace wa in taimakon ya shafi kar2 ne zai iya in ko wani Abu ne daban to ba a yin shi cikin makaranta ya tambaye ta shin ta fahimta? Tace eh ta gane, nan ta soma mishi tambayoyi akan abubuwan da suka yi mata duhu shi ko ya shiga bata amsa yanda zata fahimta har zuwa lokacin sallar la'asar ya mike ta ce ina zai je ne? Yace ya fita lokacin kar2 ya shiga na sallah don haka yanzu sallah zai je.
[8:46AM, 12/28/2016] â€?+234 814 912 1821â€?: ðŸµMEKE FARUWA 20ðŸµ
Mamanmu ta dubi Bilkisu ta ce maigado ki daure kiyi amfani da maganin nan ga na turaren nan wannan kuma wanka zaki yi da shi, Bilkisu ta dube ta Mamanmu kada ki shiga cikin mata masu shiga gurin malamai saboda gudun shirka, aure lokaci ne. Mama tace maigado ba zan kauce hanya ba, wannan da ki ka gani Ummana ta ai ko dashi wannan na iskokai ne, abin nan yana bani tsoro, na rasa gane me ke faruwa? Bilkisu cikin sanyin murya tace kada ki damu Mamanmu, In'sha Allah, Allah zai kawo min mafi alkairi, wata rana sai labari,
yanzun su Bilkisu sun shiga shekara ta uku a jami'a { A.B.U} mass comm. Take karanta wa, tana sha'awar zama yar jarida duk da kasancewarta ba mai yawan surutu ba amman tana so ta zama cikin yan media, karatunta ta saka a gaba in da Mamanmu ta hana kanta ci da sha ta dage dan ganin burin maigado ya cika, duk da Abban Mansura yana taimaka mata sosai to karatun jami'a ya wuce wasa wasa, dan gane da mahaifinta sai abin da ya karu na tsana, da kuma tsangwama.
***************************
Jumma'ar yau kam Modibbo tsohon nan daga masallacin jumma'a ya nufi fada dan ganawa da mai martaba, cikin wani daki na musamman suka kebe duk suna zaune ne kan dar duma bayan gaisawa da suka yi Dattijon ya soma magana. Abu na farko da na fara gani cikin al'amarin Yarima na ganshi mai yawan fitsari ne in na ce mai yawan fitsari ina nufin yana da matsananciyar sha'awa, game da batun aure kuma ba da gaggawa kamar yadda ka ke nufi ba, amma zai yi aure ba da jimawa sosai ba, saboda matar tashi ba yar yankin nan jihar ba ce, sannan tana da matsala, haduwarsu da Yarima zai kawo abubuwa da dama, a cikin binciken nawa na ga al'amura da yawa, amma Allah shi ne mafi sani haka nan yafi mu sanin komai game da abin da zai faru, anan gaba. Sai dai za a iya nema mishi Auren daga wasu jihohi yazo yaga wadda zasu sasanta ko Allah zai sa tana ciki, haka ne in ji mai martaba, za a nemo mishi hotuna nan su sai in sa a kai mishi ya zaba in yaso sai ayi bikin a tura mishi can, dattijon yace to madalla haka din ma ya yi zamu bisu da addu'a, bayan tattaunawa suka yi sallama.
Yarima yana cikin bahon wankan mai cike da kanshin sabulai kaloli masu sa santsin jiki da laushin fata, kwance yake ciki ya yi lamo zuciyarshi dam da sha'awar yarinyar yar mutanen China, yau sati daya da haduwarsu kullum sai ta neme shi da yawa tana son shiga harkarshi musamman da ta San in yana makaranta to karatu yazo abin da bata sani ba makaranta tana cike ne da yammatanshi sai dai sun san baza ya kula su a school ba in kin matsu isko shi gidan shi sau biyu suna rigima da Vicky.
[8:46AM, 12/28/2016] â€?+234 814 912 1821â€?: ðŸµMEKE FARUWA 21ðŸµ
Bilkisu sun shiga shekara ta karshe a makaranta , da kyar da sidin goshin da taimakon su Abban Mansura ta gama Degree na farko, ta samu damar zama yar jarida, suna gida sai jiran bautar kasa, cikin yardar Ubangiji da sa'a Kaduna aka tura ta, farooq kam yace ba wata bautar kasa da Mansu zata yi saboda tsohon cikin dake gare ta tuni ma ya tafi da ita Kaduna gidanshi na can, don haka gidan su Mansu take son zama kamar yanda suka yi da Mansu, ta waya,
Dama cikin shekara hudun nan Mansu a shiririta take karatun, course din da aka bata ba shi ta nema ba, gidan farooq ya kama a malali na sani same road, ya yi kusa da sakatariyarsu, Bilkisu duk da cewa sai ka hau mashin, ranar da ta soma saka kayan NYSC zaku ganin tamkar tafi kowace mace sa'a Mansura ta ce kin yi kyau wlh Bily, ta dubi Mansu, ina tunanin yaya zanyi na fita da wando? Zan dinga saka after dress idan zan fita in naje zan cire.
zaune kofar gidan Yarima, magajin Malam ne tunda ya sauka ya iso gidan a kulle,ya sani kamar wannan lokacin Yarima yana makaranta, zaman kusan awa uku sai ga Yarima shi da yar mutanan China, hannuwansu rike cikin na juna, magajin Malam yace toh! Abu ya kara gaba, tunda yanzu har cikin gari yana yawo rike da mace, abin damuwa ba ne, ya tsaya cike da matukar mamaki ganin magajin Malam ya iso yana cewa, abokina tun yaushe ka ke a nan? Magajin Malam ya mike Yana dan karkade rigarshi, nafi awa biyu ina jiranka fa, suka yi musabiha rike da hannun juna suka nufi cikin gida, tana biye da su Yarima, ya ce jiki na fa ya yi sanyi da ganinka, Allah yasa ba hukuncin mai martaba ba ne zan fuskanta, magajin Malam yace barin na huta nayi sallah, to yi bari na amso mana take away suka fita shi da chelen don yanzu ta zamar mishi jaka, ko ina tana manne dashi ga tsinannan kishi, dama tana yawan gaya mishi su a dokar kasarsu mutum ba zai yi mata biyu ba.
Yarima kam ya ce mata shi sai dai tayi hakuri da shi, soyayyah zai yi da mata da yawa, amma macen aurenshi daya ce, ta kan ce ita ce? Sai yace mata ba zai iya sani ba, zaune suke tsakiyar falon Yarima da magajin Malam, yan ciye ciye suke yi tare da yan hirarraki ya matsu yasan Dalilin zuwan magajin Malam shi ko magajin Malam sai ja mishi rai yake yi, tare da tsokanarshi, Yarima don Allah magajin Malam yi min bayani mana, mikewa ya yi ya shiga bedroom din Yarima Ya dauko jakarshi irin wacce ake ratayawa , yazo ya zauna ya zage ta ya ciro envelop ya mika ma Yarima gashi in ji mai martaba sakon kenan yace lallai ka duba in je mishi da amsa, ya mike rike da jakarashi duba ina zuwa bari na maida jakar.
Daya bayan daya yake bin hotunan da kallo, ya'ya ne na sarakuna da na manyan attajirai, kuma yan juhohi daban- daban, domin ya gani a bayan hoton magajin Malam ya dawo ya zauna kusa dashi cike da tashin hankali mai tsanani Yarima ya dubi magajin Malam, wai martaba yana nufin in zabi mata? Ina zaton haka ne in ji magajin Malam, Yarima Ya ce gaskiya ba amin a dalci ba, 24 years shi ne zan yi aure? Gaskiya ba zan iya ba, kwana kadan mutum ya tsufa, ya tara yara magajin Malam yace to yanzu ya zaka yi?
Nasan dai ba zaka yi gangancin fada mishi wadannan magananun ba? Yarima zufa yake yi, ya dubi magajin Malam ni gaskiya ko da aure zan yi ban sha'awar matanmu na nigeria, musamman. 'Yan arewarmu kauyawa ne, ya watso ma magajin Malam hotuna duba fa ka gani, kalle su bana son irin mutanan gaskiya ni kuma bana da sha'awar Auren mata da yawa, mata daya jal zan yi dan bana son a cika min gida da yara yanda mazan hausawa suke yi, kallon shi kawai magajin Malam ke yi cike da mamaki.
[8:46AM, 12/28/2016] â€?+234 814 912 1821â€?: ðŸµMEKE FARUWA 22ðŸµ
Yarima zaune kan wani dan dakali karkashin wata bishiya mai sanyi cikin makaranta, yana nazarin littafan biology, dago kan shin da zai ya sai ko ya sauke idanunshi kan wata yarinya 'yar mutanan China tana sanye da gajeran siket wanda iyakarshi tsakiyar cinyarta, rigar jikinta kuwa singileti ce mai dan siririn hannu,
Ta cikin gilashin idonshi yake kare mata kallo nan zuciyar shi ta kwadaitu da lafiyayyar fatar ta, da takusa in da yake sai ya yi tamkar bai ganta ba, a nata gefen yau ne gani na uku da ta mishi gayen ya tsaya mata a rai, tayi niyya yau zata kula shi ta tsaya gefenshi cikin harshen turanci take CE mishi sannu da hutawa kasaitar tashi ta motsa, yi yayi tamkar bai ji ta ba, sai da ta sake maimaitawa sannan ya amsa ba tare da ya dube ta ba, tace zata iya zama kusa dashi?
Yace in taso haka zata iya, ta zauna tana satar kallon shi, ta dan yi gyaran murya, sannan tace shin zata iya tambayarshi? Hannu ya daga mata kafin yace yanzu ba time din tambaya ba ne, shiru tayi na dan lokaci sannan ta ce to zai iya taimakon ta? Ko yanzun ba lokacin taimako ba ne? Ya bata amsa dace wa in taimakon ya shafi kar2 ne zai iya in ko wani Abu ne daban to ba a yin shi cikin makaranta ya tambaye ta shin ta fahimta? Tace eh ta gane, nan ta soma mishi tambayoyi akan abubuwan da suka yi mata duhu shi ko ya shiga bata amsa yanda zata fahimta har zuwa lokacin sallar la'asar ya mike ta ce ina zai je ne? Yace ya fita lokacin kar2 ya shiga na sallah don haka yanzu sallah zai je.
[8:46AM, 12/28/2016] â€?+234 814 912 1821â€?: ðŸµMEKE FARUWA 20ðŸµ
Mamanmu ta dubi Bilkisu ta ce maigado ki daure kiyi amfani da maganin nan ga na turaren nan wannan kuma wanka zaki yi da shi, Bilkisu ta dube ta Mamanmu kada ki shiga cikin mata masu shiga gurin malamai saboda gudun shirka, aure lokaci ne. Mama tace maigado ba zan kauce hanya ba, wannan da ki ka gani Ummana ta ai ko dashi wannan na iskokai ne, abin nan yana bani tsoro, na rasa gane me ke faruwa? Bilkisu cikin sanyin murya tace kada ki damu Mamanmu, In'sha Allah, Allah zai kawo min mafi alkairi, wata rana sai labari,
yanzun su Bilkisu sun shiga shekara ta uku a jami'a { A.B.U} mass comm. Take karanta wa, tana sha'awar zama yar jarida duk da kasancewarta ba mai yawan surutu ba amman tana so ta zama cikin yan media, karatunta ta saka a gaba in da Mamanmu ta hana kanta ci da sha ta dage dan ganin burin maigado ya cika, duk da Abban Mansura yana taimaka mata sosai to karatun jami'a ya wuce wasa wasa, dan gane da mahaifinta sai abin da ya karu na tsana, da kuma tsangwama.
***************************
Jumma'ar yau kam Modibbo tsohon nan daga masallacin jumma'a ya nufi fada dan ganawa da mai martaba, cikin wani daki na musamman suka kebe duk suna zaune ne kan dar duma bayan gaisawa da suka yi Dattijon ya soma magana. Abu na farko da na fara gani cikin al'amarin Yarima na ganshi mai yawan fitsari ne in na ce mai yawan fitsari ina nufin yana da matsananciyar sha'awa, game da batun aure kuma ba da gaggawa kamar yadda ka ke nufi ba, amma zai yi aure ba da jimawa sosai ba, saboda matar tashi ba yar yankin nan jihar ba ce, sannan tana da matsala, haduwarsu da Yarima zai kawo abubuwa da dama, a cikin binciken nawa na ga al'amura da yawa, amma Allah shi ne mafi sani haka nan yafi mu sanin komai game da abin da zai faru, anan gaba. Sai dai za a iya nema mishi Auren daga wasu jihohi yazo yaga wadda zasu sasanta ko Allah zai sa tana ciki, haka ne in ji mai martaba, za a nemo mishi hotuna nan su sai in sa a kai mishi ya zaba in yaso sai ayi bikin a tura mishi can, dattijon yace to madalla haka din ma ya yi zamu bisu da addu'a, bayan tattaunawa suka yi sallama.
Yarima yana cikin bahon wankan mai cike da kanshin sabulai kaloli masu sa santsin jiki da laushin fata, kwance yake ciki ya yi lamo zuciyarshi dam da sha'awar yarinyar yar mutanen China, yau sati daya da haduwarsu kullum sai ta neme shi da yawa tana son shiga harkarshi musamman da ta San in yana makaranta to karatu yazo abin da bata sani ba makaranta tana cike ne da yammatanshi sai dai sun san baza ya kula su a school ba in kin matsu isko shi gidan shi sau biyu suna rigima da Vicky.
[8:46AM, 12/28/2016] â€?+234 814 912 1821â€?: ðŸµMEKE FARUWA 21ðŸµ
Bilkisu sun shiga shekara ta karshe a makaranta , da kyar da sidin goshin da taimakon su Abban Mansura ta gama Degree na farko, ta samu damar zama yar jarida, suna gida sai jiran bautar kasa, cikin yardar Ubangiji da sa'a Kaduna aka tura ta, farooq kam yace ba wata bautar kasa da Mansu zata yi saboda tsohon cikin dake gare ta tuni ma ya tafi da ita Kaduna gidanshi na can, don haka gidan su Mansu take son zama kamar yanda suka yi da Mansu, ta waya,
Dama cikin shekara hudun nan Mansu a shiririta take karatun, course din da aka bata ba shi ta nema ba, gidan farooq ya kama a malali na sani same road, ya yi kusa da sakatariyarsu, Bilkisu duk da cewa sai ka hau mashin, ranar da ta soma saka kayan NYSC zaku ganin tamkar tafi kowace mace sa'a Mansura ta ce kin yi kyau wlh Bily, ta dubi Mansu, ina tunanin yaya zanyi na fita da wando? Zan dinga saka after dress idan zan fita in naje zan cire.
zaune kofar gidan Yarima, magajin Malam ne tunda ya sauka ya iso gidan a kulle,ya sani kamar wannan lokacin Yarima yana makaranta, zaman kusan awa uku sai ga Yarima shi da yar mutanan China, hannuwansu rike cikin na juna, magajin Malam yace toh! Abu ya kara gaba, tunda yanzu har cikin gari yana yawo rike da mace, abin damuwa ba ne, ya tsaya cike da matukar mamaki ganin magajin Malam ya iso yana cewa, abokina tun yaushe ka ke a nan? Magajin Malam ya mike Yana dan karkade rigarshi, nafi awa biyu ina jiranka fa, suka yi musabiha rike da hannun juna suka nufi cikin gida, tana biye da su Yarima, ya ce jiki na fa ya yi sanyi da ganinka, Allah yasa ba hukuncin mai martaba ba ne zan fuskanta, magajin Malam yace barin na huta nayi sallah, to yi bari na amso mana take away suka fita shi da chelen don yanzu ta zamar mishi jaka, ko ina tana manne dashi ga tsinannan kishi, dama tana yawan gaya mishi su a dokar kasarsu mutum ba zai yi mata biyu ba.
Yarima kam ya ce mata shi sai dai tayi hakuri da shi, soyayyah zai yi da mata da yawa, amma macen aurenshi daya ce, ta kan ce ita ce? Sai yace mata ba zai iya sani ba, zaune suke tsakiyar falon Yarima da magajin Malam, yan ciye ciye suke yi tare da yan hirarraki ya matsu yasan Dalilin zuwan magajin Malam shi ko magajin Malam sai ja mishi rai yake yi, tare da tsokanarshi, Yarima don Allah magajin Malam yi min bayani mana, mikewa ya yi ya shiga bedroom din Yarima Ya dauko jakarshi irin wacce ake ratayawa , yazo ya zauna ya zage ta ya ciro envelop ya mika ma Yarima gashi in ji mai martaba sakon kenan yace lallai ka duba in je mishi da amsa, ya mike rike da jakarashi duba ina zuwa bari na maida jakar.
Daya bayan daya yake bin hotunan da kallo, ya'ya ne na sarakuna da na manyan attajirai, kuma yan juhohi daban- daban, domin ya gani a bayan hoton magajin Malam ya dawo ya zauna kusa dashi cike da tashin hankali mai tsanani Yarima ya dubi magajin Malam, wai martaba yana nufin in zabi mata? Ina zaton haka ne in ji magajin Malam, Yarima Ya ce gaskiya ba amin a dalci ba, 24 years shi ne zan yi aure? Gaskiya ba zan iya ba, kwana kadan mutum ya tsufa, ya tara yara magajin Malam yace to yanzu ya zaka yi?
Nasan dai ba zaka yi gangancin fada mishi wadannan magananun ba? Yarima zufa yake yi, ya dubi magajin Malam ni gaskiya ko da aure zan yi ban sha'awar matanmu na nigeria, musamman. 'Yan arewarmu kauyawa ne, ya watso ma magajin Malam hotuna duba fa ka gani, kalle su bana son irin mutanan gaskiya ni kuma bana da sha'awar Auren mata da yawa, mata daya jal zan yi dan bana son a cika min gida da yara yanda mazan hausawa suke yi, kallon shi kawai magajin Malam ke yi cike da mamaki.
[8:46AM, 12/28/2016] â€?+234 814 912 1821â€?: ðŸµMEKE FARUWA 22ðŸµ