Sashe 16
Meke Faruwa Part 3 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Mansura duk murna ta cika ta son surukarta ya kara shigarta, haka nan Bilkisu ji take tamkar mahaifiyarta CE,ta zayyane mata yanda suka yi da tsohon, itama taji dadin jin hakan ta kuma yi fatan alkairi taso su biya gurin Umman Mamanmu amma suna sauri ne jiya da suka je Bauchi, zariya suka tsaya Mamanmu tasha murana jin batun da tazo dashi washe gari da sassafe suka nufi Kaduna ta koma bakin aikinta.
Yarima yana kwance a dakin shi can malesia, ya rasa dalilin da yasa zuciyar shi ta cika da son ya tuno inda ya san yarinyar wadda zuciyar tashi ta mata lakabi da beauty, amma ya kasa, ya sani bashi da saurin mantuwa da sun taba haduwa kyanta ba mai saurin gushewa a rai ba ne da zai tuna, wata zuciyar tace meyasa ka damu kanka da tunanin inda kasan wannan yar kauyen? Tsaki yaja sannan ya mike yana ayyanawa a zuciyar shi, cewa cikin lokutan da ya tsara bai cire na tunanin kowa ba,saboda bai ga macen da ta isa ya tsaya tunaninta ba, can haka ya tashi ya nufi kicin don kora wani abin mai dan sanyi.
Dattijon ya maida hankali ne kan rokon Ubangiji ya karkato hankalin jikanshi ga aure, duk addu'o'in da ya yi mishi cikin ruwa da wadanda zai dinga karanta wa duk saboda hakan ne.
kwana uku tsakani zuciyar Yarima ta tsumu da sha'awar yarinyar da zuciyar shi tasa mata suna beauty, in suna kwance da chelen sai ya dinga rayo beauty, in su Vicky ma yanzu ana dai harka ne kawai, a tsarin shi baya son ya nemi yar arewa don baya son raini, su din basu waye ba, bayan haka ma baya son ya samu zubar da darajar gidansu, to meyasa ya samu kanshi da jin sha'awar yarinyar, ya tuno cikar kirjinta da yanda mazaunanta suke juyawa, lokacin da zata fita daga cikin masaukinsu na gidan kakanshi, tunanin yanda yarinyar take yaji irinta ta yaya, zai kai ga samun haka? Duk da ya kula sai saka yake yana warwarewa, kafin daga karshe ya yanke shawarar neman farooq, bayan sun gaisa ne farooq yace, lallai yau za'ayi ruwa da kankara Yarima yayi murmushi yace dan dai da ba ka da number ta ne shi yasa bana gaisuwa.
yace, haka ne kam dama ina son in tambaye wannan yarinyar ne wani Abu shin kana da number din ta? Farooq yace wace kenan? Yarima yace, wadda Ku ka zo tare din nan,. Ya ce OK kana nufin Bilkisu ba? Yarima yace, kila ita din ce, kawar dai matarka. Farooq yace kana sonta ne?
Ko kusa, zan dai tambaye ta ne wani Abu.farooq dai ya tura mishi number. Yarima ya soma tunanin yanda za ta dauki abin da zai gaya mata, amma sai yace bari ma dai ya fara sanin ina ta san shi? Kuma yaya suke? Ma'ana shi da ita
[8:47AM, 12/28/2016] â€?+234 814 912 1821â€?: ðŸµMEKE FARUWA 27ðŸµ
Ta dan watsa ruwa don taji iska kamar yanda ta saba yi kullum in zata kwanta, ta shafa humra mai hade da wani turare mai dan karan kanshi, ta saka rigar baccinta haye gado. Mansu ta shigo tana cewa. Bily ga dan gidan ki wai yau ma nan zai kwana.
Ta jawo shi ta kwantar a bayan ta tace. Ai dama dadyna dan rigima nasan nan zaka kwana ko?
Yace, eh momy. Haka yake kiran su su duka. Momy Bilkisun ma yace momy mansu tace bari in je in kwanta kamshinki yana rinjayata. Bily tace kija mana kofa sai da safe.
Cikin bacci taji wayarta, cike da mamaki ta dauko ta daga saman kanta ba ko shakka kuskuren numba ne tunda ita ban da mansu da mijinta sai kannanta su Sakina sai ko abokan aikinta bata da mai kiranta amma duk da haka sai ta dauka cikin yana yin bacci tayi sallama daga can gefen ya amsa a kasaice, sannan yace.
A ina ne ki ka san Yarima?
Nan ta wartsake, haushin shi ne ya cikata tace rai a bace.
Wanene kuma Yarima? Ni ban san wani Yarima ba, kai Malam. Yayi shiru maganar ta matukar ba shi takaici,amma ya dake.
Kada ki damu please sanar dani.
Tace kai ni fa ban san shi ba.
Dole ne kin san shima don in da ba ki san shi ba ai baza ki nuna mishi sani ba,amma tunda kin ce haka menene dangantarki da Modibbo family?
Wadannan tambayoyin fa sun ishe ni haka, ta ce da shi.
Dole ne kuma ki amsa su. Shima yace a fusace.
Tsaki tayi sannan ta kashe wayar, ta kwanta zuciyar ta tam takaici.
A nashi gefen kam yafi ta bakin ciki sosai, bai taba zaton wata mace zata yi mishi wulakanci haka ba, wai macen ma yar Nigeria kuma yar arewa bakauyiya. Ya girgiza kai.
Alkawari ne sai na rama ko ta halin yaya ne. Ya yi niyyar share ta amma sai ya fasa. Kuma kiranta yayi
ta dauka, wai lafiya?
Amsa min tambaya ta, yace da ita sai ka zo ka shake ni na amsa maka din.
In kin fi son haka za ki samu.
Tace toh bismilla, ina jiran ka. Ta kuma kashewa.
Ya mike tsaye, ba a taba cin mutuncinshi haka ba,mace ce ma tayi mishi haka kai shi ko namiji ma bai taba mishi wannan cin kashin ba, bare Mace wadda bai dauke ta komai ba sai abin nishadi ya na bata daraja ta wannan fanni amma baya daukar raini, kwana yayi yana da na sanin kiranta kuma yanzun in ya barta haka taci nasara akan shi kai sai ya yagata.
Washe gari da safe yana kwance cikin bahon wanka tunani ne ya ci kanshi Sam ya kasa yin komai saboda takaici yana son ya samu mafita amma ya rasa sai dai zuciyar shi tafi tafiya kan Abu daya, ya yi soyayyan karya da ita ma'ana ya daure yace yana sonta sai ta shiga tarkon shi sannan ya yagata, ya gama wanka ya fito bai tsaya gurin shafe shafe ba, kai tsaye ya wuce bedroom din shi waya ya dauka sannan ya zauna kan wata kujera dake gaban dogon madubin nashi, ya soma kiran layinta dai dai suna karyawa ita da dady tana sauri ta fita ta dauki wayar tana dubawa shi din ne,dama ta zargi haka,ta dauka a dake yace.
Ki sanar dani in da ki ka sanni.
In an kifa?
Tace a fusace.
Zaki yarda ma,ba kamar ma in kin shirya yin aure? Dan nasan shi ne kawai zai yi maganin rashin kunyar ki.
A tsaye zancan yazo mata a ranta tace wannan kanshi daya kuwa? Amma a fili sai ta ce
Ba ka isa ka aure ni ba ka min kankanta ka min yaro, nasan kuruciyarka nasan yarintarka don haka ka min kadan kai kanin bayana ne don haka.....
Ya katse ta.
Ke!!! Kina hauka ne? Ni ki ke gaya ma haka ? Ki sani ban taba samun macen da taci min mutun ci irin haka ba,zan nuna miki ni yaro ne sai na aure ki kuma sai na ganar dake kurenki I promise za ki San wanene YARIMA
[8:47AM, 12/28/2016] â€?+234 814 912 1821â€?: ðŸµMEKE FARUWA 28ðŸµ
Yarima yana kwance a dakin shi can malesia, ya rasa dalilin da yasa zuciyar shi ta cika da son ya tuno inda ya san yarinyar wadda zuciyar tashi ta mata lakabi da beauty, amma ya kasa, ya sani bashi da saurin mantuwa da sun taba haduwa kyanta ba mai saurin gushewa a rai ba ne da zai tuna, wata zuciyar tace meyasa ka damu kanka da tunanin inda kasan wannan yar kauyen? Tsaki yaja sannan ya mike yana ayyanawa a zuciyar shi, cewa cikin lokutan da ya tsara bai cire na tunanin kowa ba,saboda bai ga macen da ta isa ya tsaya tunaninta ba, can haka ya tashi ya nufi kicin don kora wani abin mai dan sanyi.
Dattijon ya maida hankali ne kan rokon Ubangiji ya karkato hankalin jikanshi ga aure, duk addu'o'in da ya yi mishi cikin ruwa da wadanda zai dinga karanta wa duk saboda hakan ne.
kwana uku tsakani zuciyar Yarima ta tsumu da sha'awar yarinyar da zuciyar shi tasa mata suna beauty, in suna kwance da chelen sai ya dinga rayo beauty, in su Vicky ma yanzu ana dai harka ne kawai, a tsarin shi baya son ya nemi yar arewa don baya son raini, su din basu waye ba, bayan haka ma baya son ya samu zubar da darajar gidansu, to meyasa ya samu kanshi da jin sha'awar yarinyar, ya tuno cikar kirjinta da yanda mazaunanta suke juyawa, lokacin da zata fita daga cikin masaukinsu na gidan kakanshi, tunanin yanda yarinyar take yaji irinta ta yaya, zai kai ga samun haka? Duk da ya kula sai saka yake yana warwarewa, kafin daga karshe ya yanke shawarar neman farooq, bayan sun gaisa ne farooq yace, lallai yau za'ayi ruwa da kankara Yarima yayi murmushi yace dan dai da ba ka da number ta ne shi yasa bana gaisuwa.
yace, haka ne kam dama ina son in tambaye wannan yarinyar ne wani Abu shin kana da number din ta? Farooq yace wace kenan? Yarima yace, wadda Ku ka zo tare din nan,. Ya ce OK kana nufin Bilkisu ba? Yarima yace, kila ita din ce, kawar dai matarka. Farooq yace kana sonta ne?
Ko kusa, zan dai tambaye ta ne wani Abu.farooq dai ya tura mishi number. Yarima ya soma tunanin yanda za ta dauki abin da zai gaya mata, amma sai yace bari ma dai ya fara sanin ina ta san shi? Kuma yaya suke? Ma'ana shi da ita
[8:47AM, 12/28/2016] â€?+234 814 912 1821â€?: ðŸµMEKE FARUWA 27ðŸµ
Ta dan watsa ruwa don taji iska kamar yanda ta saba yi kullum in zata kwanta, ta shafa humra mai hade da wani turare mai dan karan kanshi, ta saka rigar baccinta haye gado. Mansu ta shigo tana cewa. Bily ga dan gidan ki wai yau ma nan zai kwana.
Ta jawo shi ta kwantar a bayan ta tace. Ai dama dadyna dan rigima nasan nan zaka kwana ko?
Yace, eh momy. Haka yake kiran su su duka. Momy Bilkisun ma yace momy mansu tace bari in je in kwanta kamshinki yana rinjayata. Bily tace kija mana kofa sai da safe.
Cikin bacci taji wayarta, cike da mamaki ta dauko ta daga saman kanta ba ko shakka kuskuren numba ne tunda ita ban da mansu da mijinta sai kannanta su Sakina sai ko abokan aikinta bata da mai kiranta amma duk da haka sai ta dauka cikin yana yin bacci tayi sallama daga can gefen ya amsa a kasaice, sannan yace.
A ina ne ki ka san Yarima?
Nan ta wartsake, haushin shi ne ya cikata tace rai a bace.
Wanene kuma Yarima? Ni ban san wani Yarima ba, kai Malam. Yayi shiru maganar ta matukar ba shi takaici,amma ya dake.
Kada ki damu please sanar dani.
Tace kai ni fa ban san shi ba.
Dole ne kin san shima don in da ba ki san shi ba ai baza ki nuna mishi sani ba,amma tunda kin ce haka menene dangantarki da Modibbo family?
Wadannan tambayoyin fa sun ishe ni haka, ta ce da shi.
Dole ne kuma ki amsa su. Shima yace a fusace.
Tsaki tayi sannan ta kashe wayar, ta kwanta zuciyar ta tam takaici.
A nashi gefen kam yafi ta bakin ciki sosai, bai taba zaton wata mace zata yi mishi wulakanci haka ba, wai macen ma yar Nigeria kuma yar arewa bakauyiya. Ya girgiza kai.
Alkawari ne sai na rama ko ta halin yaya ne. Ya yi niyyar share ta amma sai ya fasa. Kuma kiranta yayi
ta dauka, wai lafiya?
Amsa min tambaya ta, yace da ita sai ka zo ka shake ni na amsa maka din.
In kin fi son haka za ki samu.
Tace toh bismilla, ina jiran ka. Ta kuma kashewa.
Ya mike tsaye, ba a taba cin mutuncinshi haka ba,mace ce ma tayi mishi haka kai shi ko namiji ma bai taba mishi wannan cin kashin ba, bare Mace wadda bai dauke ta komai ba sai abin nishadi ya na bata daraja ta wannan fanni amma baya daukar raini, kwana yayi yana da na sanin kiranta kuma yanzun in ya barta haka taci nasara akan shi kai sai ya yagata.
Washe gari da safe yana kwance cikin bahon wanka tunani ne ya ci kanshi Sam ya kasa yin komai saboda takaici yana son ya samu mafita amma ya rasa sai dai zuciyar shi tafi tafiya kan Abu daya, ya yi soyayyan karya da ita ma'ana ya daure yace yana sonta sai ta shiga tarkon shi sannan ya yagata, ya gama wanka ya fito bai tsaya gurin shafe shafe ba, kai tsaye ya wuce bedroom din shi waya ya dauka sannan ya zauna kan wata kujera dake gaban dogon madubin nashi, ya soma kiran layinta dai dai suna karyawa ita da dady tana sauri ta fita ta dauki wayar tana dubawa shi din ne,dama ta zargi haka,ta dauka a dake yace.
Ki sanar dani in da ki ka sanni.
In an kifa?
Tace a fusace.
Zaki yarda ma,ba kamar ma in kin shirya yin aure? Dan nasan shi ne kawai zai yi maganin rashin kunyar ki.
A tsaye zancan yazo mata a ranta tace wannan kanshi daya kuwa? Amma a fili sai ta ce
Ba ka isa ka aure ni ba ka min kankanta ka min yaro, nasan kuruciyarka nasan yarintarka don haka ka min kadan kai kanin bayana ne don haka.....
Ya katse ta.
Ke!!! Kina hauka ne? Ni ki ke gaya ma haka ? Ki sani ban taba samun macen da taci min mutun ci irin haka ba,zan nuna miki ni yaro ne sai na aure ki kuma sai na ganar dake kurenki I promise za ki San wanene YARIMA
[8:47AM, 12/28/2016] â€?+234 814 912 1821â€?: ðŸµMEKE FARUWA 28ðŸµ