Sashe 13
Meke Faruwa Part 3 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Yace Modibbo kana bani mamaki in na ce ka canza kana min musu yanzu har da haihuwar ce ba ka so? Yace eh bana so ko ka taba ganina na dauki wani yaro iya tsawon rayuwarka? Shin ko wasa kaga ina ma yara? Magajin Malam yace to tunda ka ce baka son matan nigerian sai yan wace kasar, yan China? Cikin gatse ya tambaye shi. Yarima yaja tsaki ni yanzu kawai ka ce mishi cikin su babu wadda ta min, kallon hotunan magajin Malam ke yi cike da mamakin yarima, yanmata ne kyawawa, ya dube shi matan sauran kasashin farar fata ba su fi namu kyau da cikar halitta ba,farin ne kurum amma matan arewa sune matan da ya dace mu aura sabo..... Yarima ya katse shi, please wannan ra'ayinka ne ni basu min ba, magajin Malam yace ni ko kaga akwai yarinya da nake so amma ina shakkar tunkararta. Yarima ya dube shi, wannan wace yarinya ce har da zata daga maka hankali? Magajin Malam yace sumayya yar gidan Umman gombe, tsaki Yarima yaja, sannan yace kai dai soko ne, yanzu dama wannan yar yarinya ce har kake wani kana shakkar ta? Kada ka bani kunya mana, ni nan shi yasa na ke matukar burge kaina, duk yanda mace ta kai da tsaruwa tayi kadan in tsaya ina wani binta ko in lallabata ba ayi ta ba, kuma ba za'a yi ta ba, in da na gagara kenan, magajin Malam yace ai matan sun fi son irin Ku masu wulakantasu, ni dai zan kai kaina gurin sumayya da naso ne in jira yi zuwan ka sai ka ja min gora muje, da sauri Yarima ya kalle shi muje INA? Gidan su can gomben cewar magajin Malam, god forbid, ba zan iya zuwa gidan su da sunan na raka ka tadi ba, sai dai in gaida Umman gombe naje kai ni fa ko matan nan da suke da daraja a idona sai dai su biyo ni, ba dai ni na biyo su ba, ni suke ya yi ba su nake ya yi ba.magajin Malam yace ba zaka gane ba ne, matanmu na arewa suna da kamun kai natsuwa da kuma kunya ba za su taba binka ba,sai dai in an dace da masu ra'ayinka su daban ne, tsaki Yarima yaja sannan yace ba a wata mace da zan so ta ba, kaf Nigeria, na fada da babbar murya, magajin Malam ya yi dariya sannan yace daina zafafawa shi Allah ba yanda bai iya ba, in yaso sai ya dauko wuyan ka ya mika ma yar nigerian ta yi ta juyi da kai son ranta, Yarima ya mike tare da fadin wannan kam tatsuniya ce irin ta mutanen da, ko cikin mafarki bana zaton zai yiwu bare a gaske, kai dai kai mishi hotuna ka ce basu yi ba, shi kenan magajin Malam yace in kuma shi yaga wadda ta yi ya zaba maka da kan shi fa? Murmushin takaici Yarima ya yi sannan ya shiga bedroom din shi don yin wanka.
***************************
Cikin sa'a Bilkisu ta soma aikin bautawa kasa, an fi turata gidan radio station na Kaduna, fannoni daban daban duk tana tabawa, wani sa'in ma har gefen TV sukan turata, yau kan news zata yi a dauka duk ta kasa sukuni saboda zata yi wani Abu ne da bata taba zaton zai zo kanta ba, duk da tana sha'awar hakan. Mansu ita da farooq dinta suna ta karfafa mata gwiwa tun a gida, sai da aka dora mata kyamara ta yi addu'a samun nutsuwa nan take natsuwa tazo mata, ta shiga karanto cikakkun labarai cikin harshen turancinta din nan dan gaske, Masha Allah haka duk wadanda suka kalli labaran litinin din yau suke cewa, saboda ganin kyau tare da zazzakar muryarta tana dawowa, Mansu ta rungume ta tana cewa kin ganki kuwa? Tamkar dama kin dade kina yi kina karantowa kina dago kai tare da juya kyawawan idanuwanki, Bilkisu ta ce har ma da sharri wane juya ido kuma? Abokan aikinta ma sun sha mamaki tare da al'ajabin kwazonta cewa suke Allah kin yi kokari Bilkisu Muhammad Salis.
A Zaria kuwa babansu haushin mama yake ji nashi ganin ta tura ya karuwancine a Kaduna, in ma ta sake ta debo ciwon zamani ba dai gidan shi ba,su Ladiyo ma haka suke cewa, ta tafi yawon dandi suna zuga shi yana faman fada. Goggo Amarya kuwa cewa ta yi Allah ya isa tsakaninta da Fatima kuma tayi bakin cikin hada zuri'a da ita, auduga Mamanmu ta sa ta toshe kunnenta tana yiwa 'yarta fatan alkairi ne ta tsaya tsayin daka dan yiwa 'yar tata addu'a saboda Allah yana saurin karbar addu'ar iyaye ga ya'ayansu.
***************************
Lokacin rakiyar magajin Malam filin jirgi ne suke tattaunawa a mota, Yarima yana me kara jaddada ma magajin Malam sakonshi gurin mai martaba, fadi yake yi don Allah kace mishi duk cikin su babu wadda ta yi min, yar dariya magajin Malam ya yi kafin yace wlh ba zan iya cewa mai martaba haka ba, jin ka kawai nake yi, dama shiru na maka in na shiga jirgi in duba hotunan wadda ta kwanta min a rai sai na ce mishi ga zabinka, Yarima yace tab ka ce kaso dai ka kulla min tsiya? Magajin Malam yace tabbas domin kuwa ina fada sai a shiga biki, sai dai kaji an gama.Yarima ya yi parking gefen titi yace da ka cuce ni yanzu to yaya zan yi ne ma? Magajin Malam yace oho, ni dai ba zan iya yiwa mai martaba rashin kunya ba, domin wannan rashin kunya ne, kai ka kira wayarshi ka sanar dashi cewa babu wace tayi maka. Yarima yace kasan ko da wasa ba zan iya ba, to shi ne ni ka ke son in je gaban shi in gaya mishi haka, kimarshi ta wuce nan a gurina, ni kawai ka kai ni kada lokaci ya kure, jirgi ya barni a tasha, wayarshi, ya shiga Neman layin mai martaba, a zuciyar shi kuma yana kisima me zai CE mishi? Yarima yayi sallama lokacin da ya ji an dauka, mai martaba ba ya amsa sannan ya soma gaishe da mahaifin nashi cikin girmamawa, mai martaba yace ina fata kuna lafiya? Lfy lau in ji Yarima sannan yace am dama shi kenan dai dama zan gaishe ka ne, mai martaba yace kayi magana Modibbo nasan akwai abin da ka ke son cewa Aa ba komai ranka ya dade, yace shikenan kaga sakon gurin magaji ko? Yace na gani ka zabe ne? Mai martaba ya jeho mishi tambaya, eh am...Aa ban amma dai kawai Ku zabar min don ni banga wadda ta kwanta min ba.
Yarima ka duba sosai kuwa? Cewar mai martaba, na duba amma Ku duba min duk wadda kuka ga ta yi shi kenan, ni nawa bi ne In'sha Allah, to ko dai auran ne ba ka so? Ina nufin ya yi wuri? Aa in ji Yarima, ni duk yanda kuka yi shikenan zan bi, shirun dan lokaci sannan mai martaba yace shi kenan tunda ba su yi ba za a duba maka wasu sai dai ina maka nasiha da cewa kazama na kirki a duk in da ka ke ka guji zina saboda ita babban zunubi ce ka sani in ka yi da yar wani sai anyi da taka in ko da matar wani kayi haka nan za'a yi da taka, ka zama na gari wannan shi ne yace to na gode Allah ya kara maka nasara, magajin Malam yana nan zuwa yanzu zai taso yace Allah ya kawo shi lfy.
Ya dubi magaji cike da fara'a na ci nasara, kai mugu har kana min dariya, suka tafa ya kai shi filin jirgi suka tashi ya juyo gida cike da nishadi prince kenan.
Watanni shida kenan da fara service din Bilkisu, sallah ce ta zo babba, sun samu dan Hutu na kwana uku su Mansura gombe zasu je sallah sun matsa mata da cewa lallai da ita za suje tace bari in munje zariya kila in je, haka ne kuwa, Allah yasa tana da rabon zuwa, Mamanmu ta ce kuje mana ba zai yiwa ba ma in hana ki zuwa, suna zaune a falon Mansura na gidansu a can gomben tsarar rangida ne da a ka ganshi cikin family house din su farooq an sauke su da kalolin abinci masu dadi dangin farooq suna matukar son Mansura,
[8:46AM, 12/28/2016] â€?+234 814 912 1821â€?: ðŸµMEKE FARUWA 23 ðŸµ
***************************
Cikin sa'a Bilkisu ta soma aikin bautawa kasa, an fi turata gidan radio station na Kaduna, fannoni daban daban duk tana tabawa, wani sa'in ma har gefen TV sukan turata, yau kan news zata yi a dauka duk ta kasa sukuni saboda zata yi wani Abu ne da bata taba zaton zai zo kanta ba, duk da tana sha'awar hakan. Mansu ita da farooq dinta suna ta karfafa mata gwiwa tun a gida, sai da aka dora mata kyamara ta yi addu'a samun nutsuwa nan take natsuwa tazo mata, ta shiga karanto cikakkun labarai cikin harshen turancinta din nan dan gaske, Masha Allah haka duk wadanda suka kalli labaran litinin din yau suke cewa, saboda ganin kyau tare da zazzakar muryarta tana dawowa, Mansu ta rungume ta tana cewa kin ganki kuwa? Tamkar dama kin dade kina yi kina karantowa kina dago kai tare da juya kyawawan idanuwanki, Bilkisu ta ce har ma da sharri wane juya ido kuma? Abokan aikinta ma sun sha mamaki tare da al'ajabin kwazonta cewa suke Allah kin yi kokari Bilkisu Muhammad Salis.
A Zaria kuwa babansu haushin mama yake ji nashi ganin ta tura ya karuwancine a Kaduna, in ma ta sake ta debo ciwon zamani ba dai gidan shi ba,su Ladiyo ma haka suke cewa, ta tafi yawon dandi suna zuga shi yana faman fada. Goggo Amarya kuwa cewa ta yi Allah ya isa tsakaninta da Fatima kuma tayi bakin cikin hada zuri'a da ita, auduga Mamanmu ta sa ta toshe kunnenta tana yiwa 'yarta fatan alkairi ne ta tsaya tsayin daka dan yiwa 'yar tata addu'a saboda Allah yana saurin karbar addu'ar iyaye ga ya'ayansu.
***************************
Lokacin rakiyar magajin Malam filin jirgi ne suke tattaunawa a mota, Yarima yana me kara jaddada ma magajin Malam sakonshi gurin mai martaba, fadi yake yi don Allah kace mishi duk cikin su babu wadda ta yi min, yar dariya magajin Malam ya yi kafin yace wlh ba zan iya cewa mai martaba haka ba, jin ka kawai nake yi, dama shiru na maka in na shiga jirgi in duba hotunan wadda ta kwanta min a rai sai na ce mishi ga zabinka, Yarima yace tab ka ce kaso dai ka kulla min tsiya? Magajin Malam yace tabbas domin kuwa ina fada sai a shiga biki, sai dai kaji an gama.Yarima ya yi parking gefen titi yace da ka cuce ni yanzu to yaya zan yi ne ma? Magajin Malam yace oho, ni dai ba zan iya yiwa mai martaba rashin kunya ba, domin wannan rashin kunya ne, kai ka kira wayarshi ka sanar dashi cewa babu wace tayi maka. Yarima yace kasan ko da wasa ba zan iya ba, to shi ne ni ka ke son in je gaban shi in gaya mishi haka, kimarshi ta wuce nan a gurina, ni kawai ka kai ni kada lokaci ya kure, jirgi ya barni a tasha, wayarshi, ya shiga Neman layin mai martaba, a zuciyar shi kuma yana kisima me zai CE mishi? Yarima yayi sallama lokacin da ya ji an dauka, mai martaba ba ya amsa sannan ya soma gaishe da mahaifin nashi cikin girmamawa, mai martaba yace ina fata kuna lafiya? Lfy lau in ji Yarima sannan yace am dama shi kenan dai dama zan gaishe ka ne, mai martaba yace kayi magana Modibbo nasan akwai abin da ka ke son cewa Aa ba komai ranka ya dade, yace shikenan kaga sakon gurin magaji ko? Yace na gani ka zabe ne? Mai martaba ya jeho mishi tambaya, eh am...Aa ban amma dai kawai Ku zabar min don ni banga wadda ta kwanta min ba.
Yarima ka duba sosai kuwa? Cewar mai martaba, na duba amma Ku duba min duk wadda kuka ga ta yi shi kenan, ni nawa bi ne In'sha Allah, to ko dai auran ne ba ka so? Ina nufin ya yi wuri? Aa in ji Yarima, ni duk yanda kuka yi shikenan zan bi, shirun dan lokaci sannan mai martaba yace shi kenan tunda ba su yi ba za a duba maka wasu sai dai ina maka nasiha da cewa kazama na kirki a duk in da ka ke ka guji zina saboda ita babban zunubi ce ka sani in ka yi da yar wani sai anyi da taka in ko da matar wani kayi haka nan za'a yi da taka, ka zama na gari wannan shi ne yace to na gode Allah ya kara maka nasara, magajin Malam yana nan zuwa yanzu zai taso yace Allah ya kawo shi lfy.
Ya dubi magaji cike da fara'a na ci nasara, kai mugu har kana min dariya, suka tafa ya kai shi filin jirgi suka tashi ya juyo gida cike da nishadi prince kenan.
Watanni shida kenan da fara service din Bilkisu, sallah ce ta zo babba, sun samu dan Hutu na kwana uku su Mansura gombe zasu je sallah sun matsa mata da cewa lallai da ita za suje tace bari in munje zariya kila in je, haka ne kuwa, Allah yasa tana da rabon zuwa, Mamanmu ta ce kuje mana ba zai yiwa ba ma in hana ki zuwa, suna zaune a falon Mansura na gidansu a can gomben tsarar rangida ne da a ka ganshi cikin family house din su farooq an sauke su da kalolin abinci masu dadi dangin farooq suna matukar son Mansura,
[8:46AM, 12/28/2016] â€?+234 814 912 1821â€?: ðŸµMEKE FARUWA 23 ðŸµ