Sashe 40
Mabaraciya Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yace" ke me kike yi a nan? Hararan sa tayi ,tana koma kan gado taci gaba da kukan ta " ke banason rashin kunyar nan naki ina kika kai matata ke kuma me ya kawo ki nan? " Kai zan tambaya ina ka kaimin Mijina kuma me ya kawo ka gidana? Wayar da ke aljihun sa ne yayi ringing dubuwa yayi yaga Ammi ce da sauri ya ɗaga wayar " kufito kai da Meerah ina falon ku"tana gama faɗar haka ta kashe wayar ,bin wayar yayi da ido me hakan ke nufi Ammi ta san da zuwan yarinyar kenan cikin gidan nan " kifito Ammi tana jiranmu a falo yana gama faɗa mata bejirata ba ya fice ,haɗiye kukan ta tayi tafa ra tambayar kanta " shin me hakan ke nufi wace Ammin ke ne man mu? Tashi tayi ta bi bayan sa don son cirewa zuciyarta ko konto ,tana fitowa Ammi ta taso da sauri ta rungumota jikin ta kusa da inda Mu'aiseen ya zauna ta zaunar da ita ,da sauri ta ɗaga kai ta kalleta.
Komawa Ammi tayi ta zauna ,kafin ta fara magana " A rayuwar nan duk abinda bawa zeyi ana so ya barwa Allah zaɓin sa da yawa zamu so abu wanda ba Alkhairi bane a garemu idan muka barwa Allah zaɓi de ya zaɓa mana mafi Alkhairi ,tun kafin a haife mutum ƙaddararsa take rubuce a littafin sa ,shiyasa ake son mu yawaita addu'a ,don neman yardar Allah a cikin lamurran mu Ameerah da ke zan fara ,dan idan har akwai cutarwa a cikin abun da na aikata to ke na cutar ,nayi karambani a cikin rayuwar ki ,duk da Ni nayi hakan ne a matsayin uwa a gareki ,don tunda na fara ganin ki sonki da tausayin ki ya lulluɓe zuciyata , kyawawan dabi'un ku yasaka ni jin bazan iya barinki ki fita daga cikin a halina ba
Na nemawa ɗana auren ki tare da roƙon iyayenki kar su sanar dake dan inajin tsoron irin boren da zakiyi, ban san hakan xe iya zama matsala ba ,ina roƙon ki da Allah ki amshi auren nan da hannu bibbiyu na tabba ta ze zamo Alkhairi a gareki , Meerah saboda kwaɗayin samun ki ga ɗana na fansar da Rumaisa ga Muhsin yanzu haka tana gidan sa " da sauri suka kalli Ammi
" Ƙwarai kuwa ,zan faɗa muku yadda akayi auren nan naku ya yiyu bayan ko wanne daga cikin ku yana da wanda ze aura"
"Maida hankalinsu sukayi gare ta ,seda ta sanar dasu komai sadai bata bayyanar da irin son da Mu'aiseen yakeyiwa Meerah ba ,kuma kai tsaye bata faɗa musu dalilin rashin ɗaura auren sa da Rufaida ba ,se cewa tayi dai auren sa da Rufaida ba yanzu ba saboda wani dalili da ya taso , sosai kuwa wannan dalilin yayiwa Mu'aiseen daɗi a ransa yake addu'ar Allah yasa dalilin ya zama silar rashin auren su da ita har abada.
" Yanzu Ammi kina nufin Rumaisa tayi aure kuma zasu bar ƙasar nan to karatun ta fa? Mu'aiseen kaidai ga amanar ƴaƴa nan na baka ,idan kacutar da ita Allah ya na kallon ka ,kayi hakuri da duk wani saɓani da zaku fuskanta ita yarinya ce bata san menene aure ba zata tarbiyyantu ne da tarbiyyar da kayi mata ,Ameerah " ɗago kai tayi ta kalli Ammi sedai kwarjinin da tayi mata yasakata saurin duƙar da kanta " kiyi biyayya ga mijin ki idan yayi Miki ba daidai ba kizo ki sanar dani ki ɗauke ni tamkar mahaifiyarki bazan taɓa barin Mu'aiseen ya cutar da ke ba ,inayi muku fatan Alkhairi ,Allah ya albarkaci rayuwar aure ku" tana gama faɗar hakan ta mike " ni zan tafi in kwanta bacci nikeji"
" Mungode sosai Ammi Allah ya saka da alkhari muje na raka ki "Mu'aiseen ya faɗa yana yunƙurawa dan rakata.
Hararan wasa tayi masa " bana son gulma tun yanzu zaka fara nuna rashin kulawa ga ƴar tawa ,idan katafi rakani ita ta zauna da wa? Kaga zo ka rufe ƙofa kawai se Allah ya tashemu lfy "Meerah kam da tunanin ta yabar jikin ta bata masan wainar da suke toyawa ba se jin maganar sa tayi tsakiyar kanta " wane tunani zakiyi bayan nasan cike kike da farin cikin samun miji me kyau kamata ,nide an cuceni da aka haɗa ni da farar kura " ni bazan ce an cuce ni ba dan nasan iyaye bazasu taɓa cutar da ƴarsu ba ,Amma ka sani auren Alfarma nayi maka wlh badan Ammi ba da a yau dinnan bazan kwana gidan ka ba kuma koda kaga ina tunani ni tunanin masoyi na nakeyi ba kai ba, to karkayi tunanin kana da matsayin da har zanyi tunanin ka ,kajira har baƙar matar ka tazo wata ƙila ita da batasan ciwon kanta ba zata iya ɓata lokaci da tunanin ka " ba zato ba tsammani taji ya murɗe mata baki ,kuma yaƙi sakar mata " daga yanzu kika sake maganar wani banza a gidana wlh se nabaki mamaki ,ni faɗa miki akayi nayi murna da liƙamin ke da kayi ko miye? Kema kinsani ba dan Ammi ce tayi wannan ba da babu abinda ze hanaki kwana gidanku a yau dinnan sakarya kuma ki wuce mutafi muyi sallah"
Wani irin kallo tayi masa " kayi sallah kai da wa? Kajira har wacce ba liƙa maka akayi ba ta shigo , ni banda wannan lokacin naka " tana gama faɗa tayi hanyar ɗaki ,daskarewa yayi saboda mamakin yarinya to me hakan ke nufi bata son sa ko me?
Lallai zan jure duk wani iskan ta amma baxan lamunci ta rika yimin zancen wani banza a gida na ba " Binta dakin yayi kasancewar 1 bedroom ne a wannan part din dole se ya shiga ɗakin ,zaune ya sameta ta rafka ta gumi da alama tunani takeyi ,tausayi ta bashi ganin yadda auren ta ya kasance ba tare da ta sani ba sedai yasan halin tsiwarta idan ya nuna mata tausayin tuburewa zatayi dan haka ya ɗaure fuska yace" yin na fila bayan aure Sunnah ce me ƙarfi saboda haka bandamu da baki so na ba na son ki ba ya zama dole a ɗabbaƙa wannan Sunnah a gidana ,kishiga ji ɗauro alwala zamuyi Sallah idan kin gadama kiyi wanka dan naga kazama aka kawomin se tsamin zufa kikeyi da kyar na daure da Ammi ta ajiye ki kusa da ni " yi tayi kamar bada ita yake ba dan ta kula neman rigima kawai yakeyi da ita ,tashi tayi ta kwanta kan gadon alamun bazatayi abun da yake so ba " wlh idan kika fusata Ni da kaina zan kaiki toilet na kuma yi miki wankan da kaina"
Ganin yana gyara hannun rigar sa yana do so gadon ya sakata tashi da sauri ta faɗa toilet tare da danna key ,dariya yayi yace
" Ga tsoro ga tsoka na "fita yayi toilet ɗin da ke ta waje yayi wanka ya ɗauro alwala ya dawo dakin ,da kayan jikin ta ya sake ganin ta amma da alama tayi wankan " wai ke wace iriyar kazama ce yanzu kayan jikin ki kika sake maida wa ? Turo baki tayi tace " to ina da wanda zan sa ne bayan su ? Ke kuma baxaki iya tambaya na ba ko ,to Bara ma kiji abun da baki sani ba wannan kayan na jikin ki ba ko wanda za'a kawo Miki daga gidanku kar ki yarda ki saka min su a cikin gida ,dan baze yiyu kiyi anfani da gumin wai gardi ba ,zanyiwa Ammi magana a haɗa miki lefe " nidai banga gardi ba wlh ga kanan ƙaton gardi da kai ,kuma se nayi amfani da kayana dan ina son su "se kuma ta fashe da kuka " ni baxan iya wannan rayuwar taka ba da ina tare da masoyi na yana lallaɓani amma kai se tsawa kakeyi min nide banyafe kukan da nayi ba
" Ohhh kice lallaɓa ki kike so nayi ,shi masoyi naki ai ke kike haukar banza akan sa tunda har ya iya musayar ki da wata to so be kai so ba ,danni yanzu ko duniya za'a mallakamin wani yace na bar masa Rufee na baxan iya ba dan tsananin so nakeyi mata " mstttwww aikin banza ai shiyasa naga kazo nan neman sallah da wacce baka so ,me yasa ba kaje wurinta kuyi ba? Dariya yayi ,saboda ya fahimci taji haushi " kar ki damu ai kamar gobe ne zan zo miki sallama cewar zan tafi amaryata matar so tana jira na"
"mtsssssw" ta ja dogon tsaki " wlh bansan matar so bace se an ɗaura auren ku a safiyar gobe ,ka gani se na tabbatar da ita ɗin kake so malam kadena wai nuƙu² kana jin daɗi a free ka samu mace kama ta batare da wahala ba ,dan kasan idan zaɓi za'a bani mace me kyau Irina baza ta zaɓeka ba dan baka cancanta ba ,baka mallaki komai da mace ke sha'awa ga namiji ba kai ni fa se ma nake ganin anya ba kai ɗin ba mata Maza bane" wannan kalmar ta mata maza ta faɗane kawai ba wai dan ta sa ma'anar ta ba ,a nufin ta dai na so ta cusa masa haushi ,aiko tayi nasarar haka ,cikin fushi yace " ke ni kike kira da mata maza yaushe kika girma da har kika san namiji ,ko da yake a matakin balaga kike kanki na hayaƙi kina kallon kowa daidai da ke ,yau zan nuna Miki idan Ni namiji ne ko mata maza"ganin ya damƙota cikin fushi da karfi ta ƙwalla ƙara tana ƙankame shi " dan Allah Ya Mu'aiseen kar ka dake ni nifa wasa nakeyi Allah kai Namiji ne ,kabari muyi sallah dare yana yi " tsaye yayi yakasa motsa wa sakamakon amon da Muryar ta tayi a cikin kunnuwan sa karo na farko da ta ambata sunan shi a rayuwarta se yaji kamar babu macen da ta iya kiran sunan kamar ita ,cikin mutuwar jiki yace " ki buɗe sip akwai hijabi ki ɗauko muyi sallar" jikin ta na rawa ta ɗauko hijab din lokacin ya fuskanci alkibila saboda haka ta tsaya a bayan sa ,suka kabbarta .
_Manage pls_
Comments and share
Komawa Ammi tayi ta zauna ,kafin ta fara magana " A rayuwar nan duk abinda bawa zeyi ana so ya barwa Allah zaɓin sa da yawa zamu so abu wanda ba Alkhairi bane a garemu idan muka barwa Allah zaɓi de ya zaɓa mana mafi Alkhairi ,tun kafin a haife mutum ƙaddararsa take rubuce a littafin sa ,shiyasa ake son mu yawaita addu'a ,don neman yardar Allah a cikin lamurran mu Ameerah da ke zan fara ,dan idan har akwai cutarwa a cikin abun da na aikata to ke na cutar ,nayi karambani a cikin rayuwar ki ,duk da Ni nayi hakan ne a matsayin uwa a gareki ,don tunda na fara ganin ki sonki da tausayin ki ya lulluɓe zuciyata , kyawawan dabi'un ku yasaka ni jin bazan iya barinki ki fita daga cikin a halina ba
Na nemawa ɗana auren ki tare da roƙon iyayenki kar su sanar dake dan inajin tsoron irin boren da zakiyi, ban san hakan xe iya zama matsala ba ,ina roƙon ki da Allah ki amshi auren nan da hannu bibbiyu na tabba ta ze zamo Alkhairi a gareki , Meerah saboda kwaɗayin samun ki ga ɗana na fansar da Rumaisa ga Muhsin yanzu haka tana gidan sa " da sauri suka kalli Ammi
" Ƙwarai kuwa ,zan faɗa muku yadda akayi auren nan naku ya yiyu bayan ko wanne daga cikin ku yana da wanda ze aura"
"Maida hankalinsu sukayi gare ta ,seda ta sanar dasu komai sadai bata bayyanar da irin son da Mu'aiseen yakeyiwa Meerah ba ,kuma kai tsaye bata faɗa musu dalilin rashin ɗaura auren sa da Rufaida ba ,se cewa tayi dai auren sa da Rufaida ba yanzu ba saboda wani dalili da ya taso , sosai kuwa wannan dalilin yayiwa Mu'aiseen daɗi a ransa yake addu'ar Allah yasa dalilin ya zama silar rashin auren su da ita har abada.
" Yanzu Ammi kina nufin Rumaisa tayi aure kuma zasu bar ƙasar nan to karatun ta fa? Mu'aiseen kaidai ga amanar ƴaƴa nan na baka ,idan kacutar da ita Allah ya na kallon ka ,kayi hakuri da duk wani saɓani da zaku fuskanta ita yarinya ce bata san menene aure ba zata tarbiyyantu ne da tarbiyyar da kayi mata ,Ameerah " ɗago kai tayi ta kalli Ammi sedai kwarjinin da tayi mata yasakata saurin duƙar da kanta " kiyi biyayya ga mijin ki idan yayi Miki ba daidai ba kizo ki sanar dani ki ɗauke ni tamkar mahaifiyarki bazan taɓa barin Mu'aiseen ya cutar da ke ba ,inayi muku fatan Alkhairi ,Allah ya albarkaci rayuwar aure ku" tana gama faɗar hakan ta mike " ni zan tafi in kwanta bacci nikeji"
" Mungode sosai Ammi Allah ya saka da alkhari muje na raka ki "Mu'aiseen ya faɗa yana yunƙurawa dan rakata.
Hararan wasa tayi masa " bana son gulma tun yanzu zaka fara nuna rashin kulawa ga ƴar tawa ,idan katafi rakani ita ta zauna da wa? Kaga zo ka rufe ƙofa kawai se Allah ya tashemu lfy "Meerah kam da tunanin ta yabar jikin ta bata masan wainar da suke toyawa ba se jin maganar sa tayi tsakiyar kanta " wane tunani zakiyi bayan nasan cike kike da farin cikin samun miji me kyau kamata ,nide an cuceni da aka haɗa ni da farar kura " ni bazan ce an cuce ni ba dan nasan iyaye bazasu taɓa cutar da ƴarsu ba ,Amma ka sani auren Alfarma nayi maka wlh badan Ammi ba da a yau dinnan bazan kwana gidan ka ba kuma koda kaga ina tunani ni tunanin masoyi na nakeyi ba kai ba, to karkayi tunanin kana da matsayin da har zanyi tunanin ka ,kajira har baƙar matar ka tazo wata ƙila ita da batasan ciwon kanta ba zata iya ɓata lokaci da tunanin ka " ba zato ba tsammani taji ya murɗe mata baki ,kuma yaƙi sakar mata " daga yanzu kika sake maganar wani banza a gidana wlh se nabaki mamaki ,ni faɗa miki akayi nayi murna da liƙamin ke da kayi ko miye? Kema kinsani ba dan Ammi ce tayi wannan ba da babu abinda ze hanaki kwana gidanku a yau dinnan sakarya kuma ki wuce mutafi muyi sallah"
Wani irin kallo tayi masa " kayi sallah kai da wa? Kajira har wacce ba liƙa maka akayi ba ta shigo , ni banda wannan lokacin naka " tana gama faɗa tayi hanyar ɗaki ,daskarewa yayi saboda mamakin yarinya to me hakan ke nufi bata son sa ko me?
Lallai zan jure duk wani iskan ta amma baxan lamunci ta rika yimin zancen wani banza a gida na ba " Binta dakin yayi kasancewar 1 bedroom ne a wannan part din dole se ya shiga ɗakin ,zaune ya sameta ta rafka ta gumi da alama tunani takeyi ,tausayi ta bashi ganin yadda auren ta ya kasance ba tare da ta sani ba sedai yasan halin tsiwarta idan ya nuna mata tausayin tuburewa zatayi dan haka ya ɗaure fuska yace" yin na fila bayan aure Sunnah ce me ƙarfi saboda haka bandamu da baki so na ba na son ki ba ya zama dole a ɗabbaƙa wannan Sunnah a gidana ,kishiga ji ɗauro alwala zamuyi Sallah idan kin gadama kiyi wanka dan naga kazama aka kawomin se tsamin zufa kikeyi da kyar na daure da Ammi ta ajiye ki kusa da ni " yi tayi kamar bada ita yake ba dan ta kula neman rigima kawai yakeyi da ita ,tashi tayi ta kwanta kan gadon alamun bazatayi abun da yake so ba " wlh idan kika fusata Ni da kaina zan kaiki toilet na kuma yi miki wankan da kaina"
Ganin yana gyara hannun rigar sa yana do so gadon ya sakata tashi da sauri ta faɗa toilet tare da danna key ,dariya yayi yace
" Ga tsoro ga tsoka na "fita yayi toilet ɗin da ke ta waje yayi wanka ya ɗauro alwala ya dawo dakin ,da kayan jikin ta ya sake ganin ta amma da alama tayi wankan " wai ke wace iriyar kazama ce yanzu kayan jikin ki kika sake maida wa ? Turo baki tayi tace " to ina da wanda zan sa ne bayan su ? Ke kuma baxaki iya tambaya na ba ko ,to Bara ma kiji abun da baki sani ba wannan kayan na jikin ki ba ko wanda za'a kawo Miki daga gidanku kar ki yarda ki saka min su a cikin gida ,dan baze yiyu kiyi anfani da gumin wai gardi ba ,zanyiwa Ammi magana a haɗa miki lefe " nidai banga gardi ba wlh ga kanan ƙaton gardi da kai ,kuma se nayi amfani da kayana dan ina son su "se kuma ta fashe da kuka " ni baxan iya wannan rayuwar taka ba da ina tare da masoyi na yana lallaɓani amma kai se tsawa kakeyi min nide banyafe kukan da nayi ba
" Ohhh kice lallaɓa ki kike so nayi ,shi masoyi naki ai ke kike haukar banza akan sa tunda har ya iya musayar ki da wata to so be kai so ba ,danni yanzu ko duniya za'a mallakamin wani yace na bar masa Rufee na baxan iya ba dan tsananin so nakeyi mata " mstttwww aikin banza ai shiyasa naga kazo nan neman sallah da wacce baka so ,me yasa ba kaje wurinta kuyi ba? Dariya yayi ,saboda ya fahimci taji haushi " kar ki damu ai kamar gobe ne zan zo miki sallama cewar zan tafi amaryata matar so tana jira na"
"mtsssssw" ta ja dogon tsaki " wlh bansan matar so bace se an ɗaura auren ku a safiyar gobe ,ka gani se na tabbatar da ita ɗin kake so malam kadena wai nuƙu² kana jin daɗi a free ka samu mace kama ta batare da wahala ba ,dan kasan idan zaɓi za'a bani mace me kyau Irina baza ta zaɓeka ba dan baka cancanta ba ,baka mallaki komai da mace ke sha'awa ga namiji ba kai ni fa se ma nake ganin anya ba kai ɗin ba mata Maza bane" wannan kalmar ta mata maza ta faɗane kawai ba wai dan ta sa ma'anar ta ba ,a nufin ta dai na so ta cusa masa haushi ,aiko tayi nasarar haka ,cikin fushi yace " ke ni kike kira da mata maza yaushe kika girma da har kika san namiji ,ko da yake a matakin balaga kike kanki na hayaƙi kina kallon kowa daidai da ke ,yau zan nuna Miki idan Ni namiji ne ko mata maza"ganin ya damƙota cikin fushi da karfi ta ƙwalla ƙara tana ƙankame shi " dan Allah Ya Mu'aiseen kar ka dake ni nifa wasa nakeyi Allah kai Namiji ne ,kabari muyi sallah dare yana yi " tsaye yayi yakasa motsa wa sakamakon amon da Muryar ta tayi a cikin kunnuwan sa karo na farko da ta ambata sunan shi a rayuwarta se yaji kamar babu macen da ta iya kiran sunan kamar ita ,cikin mutuwar jiki yace " ki buɗe sip akwai hijabi ki ɗauko muyi sallar" jikin ta na rawa ta ɗauko hijab din lokacin ya fuskanci alkibila saboda haka ta tsaya a bayan sa ,suka kabbarta .
_Manage pls_
Comments and share