← Book details Mabaraciya Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 38 OF 43

Sashe 38

Mabaraciya Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read

"Ammi ,Ammi " Amrah keta faman kira tana ratsa mutanen da ke cike da gidan kamar wata gigitacciya ,Ammi da ke faman waya ta jiyo wannan kiran da sauri ta fito dan a tunanin ta wani abunne ya faru da Rumaisa ,karo sukayi da juna ,a rikice Amrah tace " Ammi wai an ɗaura auren Rumaisa? to waye mijin ko shine dalilin wannan ciwon nata nan take? Kama hannun ta Ammi tayi suka shiga daga ciki ,zaunar da ita tayi tace " ki natsu ki kuma fahimta Amrah kisani Allah ya kadddara auren ta a yau ɗin nan kuma babu wanda ya isa ya canja ,ina so ki bata karfin gwiwa ,kece kawa mafi kusanci ga Rumaisa " amma Ammi Rumaisa bata taɓa faɗamin cewar tana da wani saurayi da har sukayi maganar aure da shi ba " Rumaisa ta fansarwa Yayanku mata ne ,kinsan dai Ameerah ko yarinyar da ke aiki ɓangaren Hajia Sauda idan baki manta ba munje gidanku da ita ,ita ce yarinyar da Yayanku ya daɗe yana so kuma babu wanda yasan hakan se ni tun tana ƙaramar ta yake fadin bayada wata mata se ita,na ɗauki abun wasa bansan yana son ta ba se a lokacin da ya nemeta ya rasa ,ya shiga damuwa sosai ,haka nasamu da addu'a da komai Allah ya cire ta a ransa , bayan tsawon lokaci se gashi yazo min da labarin wai yaga Meeran sa ,na ɗauka kawai shirmen sa ne ,da ga nan yaci gaba da bibiyarta har zuwanta gidan nan aiki sedai ni din bansan cewar ita bace se daga baya ,a wannan gaɓar kuma kawunki ya kawo zancen haɗasa da Rumaisa ,yaso yayi bore amma na dakatar dashi tare da nuna masa cewar Meerah har yanzu yarinya ce ya auri Rufaida a yanzu zuwa gaba ni xan goya masa baya akan auren Meerah , kwatsam ya samu labarin zatayi aure shine ya ɗaga hankalin sa har yana kwanciya dan haka banyi sanya ba na tafi can gidan su Meerah na samu Auntyn ta nayi mata bayani a bunda na fahimta ita kanta Auntyn kamar taso ace Mu'aiseen ne ya samu auren Meerah sadai babu yadda za'ayi suce bazasu baiwa shi Muhsin ba ,dukda wai ta fahimci dangin sa kamar basuyi murna da zaɓinsa ba kasancewar su talakawa , na nemi haɗuwa da Yayan Meerah wanda shine ya bada auren ta ,sedai ta nunamin shi mutum ne tsayayye baze taɓa canja magana ba dan haka na nemi sanin waye wanda aka baiwa auren ,har gidansu ta faɗa min da wurin aikin sa , da farko gidansu naso na tafi ,amma se nayi tunanin ba lalae bane iyayen sa su amince ,dan haka kai tsaye na wuce bank nasu ,bansamu matsala wurin ganin sa da seda ma amso numbern sa kafin na tafi ,na same shi na kuma roƙesa akan ya temakeni zan rasa yarona ,amma se ya nunamin cewar shi ma yana son ta hasalima tafiya ce a gabansa nan da wani lokaci ,kuma bazeyi yu yayi tafiyar babu iyali ba dan matar sa tace bazata bisa ba ,ganin na zube a gabansa ina kuka ,se jikinsa yayi sanyi ,yafara bani hakuri tare da amincewa buƙata na ,shi ya ɗauke ni har wurin Babansa ,nayi masa bayani shima ya amince sadai yace yarigada yagama gayyatar jama'a zuwa ɗaurin auren gaskiya baze iya cewa anfasa ba kuma rashin auren Meerah ze iya dakatar da shi Muhsin daga tafiya aikin da zeyi a waje dan shi be yarda magidanci kamar Muhsin yafati cikin turawa babu iyali ba ,bawai saboda be yarda dashi bane sedai yana gudun sheɗanun matan turawa ,ganin wannan dalilin ze kawo min cikas se na nace idan har ya amince zan bashi auren ƴata ,shi dai yace a'a ya haƙura dama beda burin ƙarin aure se akan Meerah tunda ya rasa ya haƙura ,amma se baban sa yace to lallai idan haka ne sadai na basu ƴar tawa don sun san Alh mutumin kirki ne kuma suna jin yadda mutanen gari ke yabon sa da haka dai suka amshi auren Rumaisa kinyi yadda akayi yanzu haka ita da shi basu taɓa ganin junan su ba

Amrah bawai na yi fafutukar nan kawai saboda Yayanku ya samu wacce yake so bane wlh kinji na rantse miki kaso 70 saboda rayuwar yarinyar ne ina tausayin ta ina kuma ƙaunar ta har cikin raina ,ina da tabbacin zata samu farin ciki a wurin mu ne musamman da Aunty ta sanar dani cin fuskan da dangin Muhsin sukayi musu ,ga yanada mata ,tayi karama da zaman kishi ,burin Rumaisa rayuwar yarinyar ta inganta ta samu ilmi kamar kowa ,nima shine nawa ,saboda haka ina so ki rarrashi Rumaisa ta kwantar da hankalin ta da Allah ,kar ki ƙara mata damuwa "

"Haba Ammi gaskiya bakiyiwa Rumaisa a dalci ba yanzu fa kika gama lissafa irin ƙalubalen da ke tattare da auren shi Muhsin ɗin ,ita Rumaisa zata iya zaman kishi ne ? Kuma bakiyi tunanin ya zasu amshe ta ba hala ma zasufi amsar ita Meerah ɗin akan ta saboda ko babu komai ita ɗan uwansu ya gani ya kuma ce yana so ,kuma shima yana sonta baze bari su wulaƙanta ta ba " Amrah , Rumaisa tafi Meerah shekaru ilmi da wayewar kai ,saboda ita tayi karatu kuma ta tashi a gidan nan taga irin zaman kishin da akeyi ,duk da bana fatan kishiyarta ta kasance irin Sauda amma dai ina faɗa miki duk mugun halinta to fa Rumaisa zata iya zama da ita ,kuna dangin sa matsalar su kuɗine ina da tabbacin sunan Alh kawai da sukaji ya siyawa mata daraja dan kuwa yafi su arziki nesa ba kusa ba shi kuma yaron na san ko be sota ba to baze wulaƙanta ta ba kuma zuwa gaba ze sota matuƙar ta zame masa mace ta gari ,da bayada kirki da a lokacin da yaga hawaye a ido na baze ɗaga hankalin sa har ya sadaukar min da abinda yake so ba , Rumaisa ma tana da kyan da kowa ze iya son ta ,kuma nasan bazata taɓa tabewa ba ko da biyayyar da tayi mana ,ki tayata da addu'a kawai insha'Allah duk zakuyi farinciki da wannan auren."

Ni dama tun ranar da nafara ganin Meerah da yaya nace kamar wasu masoya ,amma yarinyar nan ta Musa yanzu to Ammi ya Meerah zatayi da Sis Rufaida kinsan dai akwai matsala ko me ze hana a raba musu gida idan ba haka ba wlh zata iya cutar da ƴar mutane " karki damu a yanzu dai ba'a ɗaura auren Rufaida da Mu'aiseen ba ,bansan ko nan gaba ba shi yasa ma nayi shawara da Alh be kamata Meerah akaita gidan Mu'aiseen ba ,an gyara ɗayan part din nan da ke ta can baya ,komai akwai a ciki so ana zasu zauna gaskiya kafin nan gaba idan yarinyar ta kara gogewa dan nasan boren da Rufaida tayi ba'a hayyacin ta bane idan ta farfaɗo zata iya zuwa kaiwa ƴar mutane hari to Gara ta zauna nan kusa dani ,kinga nima zata rage min kewar Rumaisa ko,tunda rabuwar mu yazo babu shiri .

Meerah

Daƙyar Aunty ta samu tayi wanka ta saka ɗaya daga cikin kayan lefen da aka kawo mata ,ita madai gidansu babu lefi ya cika da mutanen unguwa da suke abun arxiƙi se dangin Aunty da Yaya suma duk sun zo tum a jiya ma ,ita dai danginta mutum 2 ne suka zo ɗayar yayar Mamanta ne wacce suke uba ɗaya ,se ɗayar kuma matar yayan Mamanta ,babu lefi kuwa sun kawo abun arziƙi duk da babu wani shaƙuwa tsakanin su da Meerah dan tunda tazo ta gaishe su basu sake ganin ta ba ,tana shirya wa ta kwanta bacci me nauyi yayi nasarar sace ta.

Hajia Sauda

Tun da Rufaiy ta fadawa Dady cewar bata son Mu'aiseen shikenan hankalin ta ya yakwnata dan tasan yanzu dole ze janye daga ƙudirin da yayi ,duda haka zuciyarta a ɗardar take ,na hukuncin da ze yanke ,ita dai fatan ta kawai auren ya fasu shine
Chapter 38 · 0% Book details